Saturday, December 6
Shadow
Da Duminsa: An bayyana sunayen sojoji 16 da suka yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin Mulki, Duk ‘yan Arewa ne

Da Duminsa: An bayyana sunayen sojoji 16 da suka yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin Mulki, Duk ‘yan Arewa ne

Duk Labarai
Rahotanni daga Sahara Reporters sun bayyana sunayen sojojin da ake zargi da yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Juyin Mulki. Sojojin dai guda 16 ne duk da yake sabon rahoto daga Daily Trust yace an samu karin sojoji 26 da aka kama. Ga jadawalin sunayen sojojin da jihohin da suka fito: Akwai Lieutenant Commander B Abdullahi. Sai Brigadier General Musa Abubakar Sadiq (N/10321) wanda shine ake zargin shugaban tawagar Yunkurin Juyin Mulkin. Sai Colonel M.A. Ma’aji (N/10668). Banufe ne daga jihar Naija. Lieutenant Colonel S. Bappah (N/13036). Dan asalin Jihar Bauchi ne. Lieutenant Colonel A.A. Hayatu (N/13038). Dan jihar Kadunane. Sai Lieutenant Colonel P. Dangnap (N/13025) dan jihar Filato ne. Lieutenant Colonel M. Almakura (N/12983). Dan jihar Nasarawa ne...
Kalli Bidiyon Likafa ta yi gaba: Idris Maiwushirya da ‘YarGuda sun koma Legas inda suka ci gaba da yin Bidiyo su acan

Kalli Bidiyon Likafa ta yi gaba: Idris Maiwushirya da ‘YarGuda sun koma Legas inda suka ci gaba da yin Bidiyo su acan

Duk Labarai
Bayan kamasu a Kano aka musu hukunci, Tauraron Tiktok, Idris Maiwushirya da abokiyar da suke waka tare, Abasiya 'YarGuda sun tafi Legas. A Bidiyon daya wallafa a Tiktok, An ga Maiwushirya da 'YarGuda sun ci gaba da salok Wakokin da suke yi a Kano wanda dalilin haka aka kamasu. https://www.tiktok.com/@maiwushiryabackup/video/7566925862801657106?_t=ZS-90z7t4mUWa8&_r=1
Kalli Bidiyo: A karshe dai Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta fito daga hannun ‘yansanda inda tace fhadanta da Marwat ya kare

Kalli Bidiyo: A karshe dai Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta fito daga hannun ‘yansanda inda tace fhadanta da Marwat ya kare

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta sanar da fitowarta daga hannun 'yansanda bayan da aka kamata. Tace Kabiru Legas ne ya je wajan 'yansanda yace an yiwa rayuwarsa barazana inda aka tambayeshi wa yake zargi yace ita yake zargi. Tace dan haka dole ne yasa aka kirata amma Allah ya wanke ta. A karshe ta yi godiya ga masoyanta da abokan sana'arta da 'yan uwa bisa irin soyayyar da aka nuna mata.
Da Duminsa: An kama karin sojoji 26 bisa zarginsu da hannu a yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Da Duminsa: An kama karin sojoji 26 bisa zarginsu da hannu a yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa yawan sojojin da ake tsare dasu ana bincikensu kan zargin hannu a yunkurin yiwa shugaba Tinubu juyin mulki sun kai 42. A baya dai rahotanni sun ce sojoji 16 ne aka kama ake bincike. Saidai a yanzu yawan sojojin sun kai 42 wanda ake bincike kamar yanda jaridar Daily Trust ta ruwaito. Jaridar tace wasu majiyoyi a gidan sojin sun sanar da ita cewa, ana gayyatar manyan sojoji inda ake musu tambayoyi game da zargin hannu a yunkirin juyin mulkin.
Sabbin Bayanai sun sake fitowa game da sojojin da ake zargin sun yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Sabbin Bayanai sun sake fitowa game da sojojin da ake zargin sun yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Duk Labarai
Sabbin Bayanai sun sake fitowa game da sojojin da ake zargin sun yi yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Juyin mulki. Kafar Premium times ta bayyana cewa, a cikin sojojin guda 16 da ake tsare dasu akwai Brigadier General daya da Conel daya da Lieutenant Colonel guda 4, sai masu mukamin Major 5 sai masu mukamin Captain 2, sai mai mukamin Lieutenant daya. Guda 14 daga cikinsu sojojin kasa ne sai sauran akwai sojan ruwa dana sama. Saidai har yanzu jaridar bata bayyana sunayensu ba. Wata majiya dai tace an kama karin sojoji da ake zargi da hannu a lamarin bayan su.
Da Duminsa:Duka ‘yan majalisar wakilai daga jihar Enugu sun koma jam’iyyar APC daga PDP

Da Duminsa:Duka ‘yan majalisar wakilai daga jihar Enugu sun koma jam’iyyar APC daga PDP

Duk Labarai
Duka 'yan majalisar wakilai da suka fito daga jihar Enugu sun bar jam'iyyar PDP zuwa APC. Kakakin Majalisar, Tajudeen Abbas ne ya sanar da haka a zaman majalisar na ranar Alhamis. Gwamnan jihar Enugu, Peter Mba ya shaida wannan lamari a majalisar. 'Yan majalisar sun ce sun koma APC ne saboda jam'iyyar su ta PDP rikicin cikin gida na neman gamawa da jam'iyyar.
Dan Majalisa, Honarabul Musa Lawal Maja Kura daga jihar Yobe na daukar Hankula bayan ganin tsaffon hotunansa shekaru 2 da suka gabata

Dan Majalisa, Honarabul Musa Lawal Maja Kura daga jihar Yobe na daukar Hankula bayan ganin tsaffon hotunansa shekaru 2 da suka gabata

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} IKON ALLAH: Cikin Shekara Biyu Wannan Dan Majalisar Ya Murmure Ya Koma Haka Dan majalisar jiha ne da yake wakiltar karamar hukumar Nguru a jihar Yobe, wato Honarabul Musa Lawal Maja Kura, a cikin shekaru biyu kacal da hawan sa kujerar amma kun ga yadda rayuwarsa ta sauya. Nan hotunansa a lokacin da yake koyarwa a makaranta da sana'ar POS, da kuma bayan ya zama dan majalisa.
An baiwa Babban Bankin Najeriya, CBN shawarar fito da takardun kudi na Naira 20,000 da 10,000

An baiwa Babban Bankin Najeriya, CBN shawarar fito da takardun kudi na Naira 20,000 da 10,000

Duk Labarai
Wata kungiya me suna Quartus Economics ta bada shawara ga babban bankin Najeriya da ya fito da takardar kudin Naira 20,000 da 10,000. Kungiyar tace dalili kuwa shine a yanzu takarar Naira 1000 bata iya sayen wani abin a zo a gani. Tace fito da manyan kudaden zai ragewa mutane wahalar daukar kudade da yawa wajan gudanar da kasuwanci. Ungiyar tace ba gaskiya bane abinda ake fada cewa idan aka fito da sabbin kudin zasu iya saka farashin kayan masarufi su tashi. Kungiyar tace darajar Naira ta lalace sosai.
Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saka harajin kaso 15 kan Man fetur da Gas

Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saka harajin kaso 15 kan Man fetur da Gas

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban kasa na cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince ko ya saka hannu kan kudirin dokar saka Harajin kaso 15 cikin 100 akan man fetur da gas da ake shigowa dasu Najeriya. Sakataren shugaban kasar, Damilotun Aderemi ne ya dauki takardar kudirin dokar inda ya kaiwa hukumomin da lamarin ya shafa dan a fara zartas da wannan doka. Ana tsammanin wannan sabuwar dokar haraji zata kara farashin man fetur da akalla N0.99, kamar yanda The Cable ta ruwaito.