Saturday, January 17
Shadow
Tsohon Ministan Kwadago, Chris Ngige ya nemi Beli inda yace yana fama da rashin lafiya bayan da kotu tace a tsareshi a gidan yarin Kuje, amma EFCC tace kada a bada belinsa dan zai iya tserewa

Tsohon Ministan Kwadago, Chris Ngige ya nemi Beli inda yace yana fama da rashin lafiya bayan da kotu tace a tsareshi a gidan yarin Kuje, amma EFCC tace kada a bada belinsa dan zai iya tserewa

Duk Labarai
Tsohon Ministan Kwadago Chris Ngige ya nemi Beli bayan da Kotu tasa a daureshi a gidan yarin Kuje. Yace yana fama da rashin lafiya, kamar yanda Lauyansa, Patrick Ikwueto ya bayyanawa me shari'a ta babbar kotun tarayya dake Gwarimpa a Abuja Justice Maryam Aliyu Hassan Saidai Lauyan EFCC, Sylvanus Tahir, SAN yace kotun kada ta bayar da belinsa dan a baya ita EFCC ta sakeshi inda aka saka mai ranar da zai sake komawa dan ci gaba da bincike amma yaki komawa. Yace tsohon Ministan ka iya tserewa idan aka bayar da belinsa. Saidai Mai shari'a Maryam Aliyu Hassan tace a ci gaba da tsare Ngige a gidan yarin kuje har ranar 18 ga watan Disamba kamin ta yanke hukunci kan maganar Belin.
Kalli Bidiyon: Tinubu ba zai ci zabe a 2027 ba>>Inji Sanata Enyinnaya Abaribe

Kalli Bidiyon: Tinubu ba zai ci zabe a 2027 ba>>Inji Sanata Enyinnaya Abaribe

Duk Labarai
Sanata Enyinnaya Abaribe ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba zai ci zabe ba a shekarar 2027. Ya bayyana hakane a hirar da Jaridar Channels TV ta yi dashi. Yace ko da a zaben 2023 Tinubu ba zabe yaci ba. Yace yana da yakinin Tinubu ba zai ci zabe bane saboda yanda mutane ke cikin wahala a gwamnatinsa. https://twitter.com/channelstv/status/2000637809325908386?t=zYn2EMO6acuG-s3FgP_n2A&s=19
Allan Sarki Kalli Bidiyon: Matar Tsohon Shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari ta bayyana yanda rayuwa ta kasance musu bayan rashin Buharin

Allan Sarki Kalli Bidiyon: Matar Tsohon Shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari ta bayyana yanda rayuwa ta kasance musu bayan rashin Buharin

Duk Labarai
Matar tsohon Shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari ta bayyana cewa rayuwa ta canja musu ba yanda suka sababa ba bayan rasuwar mijinta. Game da mutanen da yake hulda dasu, tace ita dama ba wai ta cika shiga mutane bane, tunda suka je suka musu gaisuwa yawanci shikenan. Tace yanzu tana rayuwane ita da 'ya'ya da jikokinta. https://www.tiktok.com/@arewa.update8/video/7584144959083711765?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7584144959083711765&source=h5_m&timestamp=1765825145&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medi...
Kalli Bidiyon: Kakakin ‘Yansandan jihar Kano ya bayar da cikakken bayanin abinda ya faru a masallacin Hotoro

Kalli Bidiyon: Kakakin ‘Yansandan jihar Kano ya bayar da cikakken bayanin abinda ya faru a masallacin Hotoro

Duk Labarai
Kakakin 'yansandan Jihar Kebbi, Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayar da cikakken bayanin abinda ya faru a masallacin Hotoro. Yace wanine ya je ya Kashe Ladani Yace wanda ake zargin an samu makogoron Ladanin a aljihunsa. Kuma da suka je sun tarar da gawarwakin mutanen biyu bayan da jama'a suka farwa wanda ake zargin shima suka aikashi Lahira. Yace an kai gawarwakin nasu zuwa Asibiti, inda Likitoci suka tabbatar sun mutu Yace suna kan Bincike kuma suna fatan mutane zasu basu hadin kai. https://www.tiktok.com/@bashir_officer0005/video/7584079066769280267?_t=ZS-92FV8vgSZxB&_r=1
Mu Inyamurai mun fi kowa Baqin Hali a Najeriya, idon mu a kudi yake, Yarbawa na girmama manyansu, haka Hausawa ma na girmama manyansu amma bandamu><Inji Fasto Chris

Mu Inyamurai mun fi kowa Baqin Hali a Najeriya, idon mu a kudi yake, Yarbawa na girmama manyansu, haka Hausawa ma na girmama manyansu amma bandamu><Inji Fasto Chris

Duk Labarai
Fasto Chris Okafor wanda Inyamuri ne ya bayyana cewa su Inyamurai halayensu basu da kyau. Yace Hausawa na girmama na gaba dasu, Yarbawa ma na girmama na gaba dasu amma banda Inyamurai. Yace Inyamuri shi kudinshi ne a gabanshi. https://twitter.com/kepukepunews/status/2000484512946597894?t=gfLTdrf1FY0DreRkXVQ3sQ&s=19
Kalli Bidiyon: Ni da ku Shyègyè ka fasa, zan zake siyo Motocin dakon ma fetur dan karya farashin man>>Dangote ya gayawa ‘yan kasuwa masu shigo da man fetur daga kasar waje

Kalli Bidiyon: Ni da ku Shyègyè ka fasa, zan zake siyo Motocin dakon ma fetur dan karya farashin man>>Dangote ya gayawa ‘yan kasuwa masu shigo da man fetur daga kasar waje

Duk Labarai
Attajirin dan kasuwa, Aliko Dangote ya bayyana cewa, masu shigo da man fetur daga kasashen waje duk da matatarsa dake aiki ba zai hanasu ba. Yace su ci gaba. Yace amma suna da motocin Dakon mai gida 4000 da ya siyo kwanakin baya, kuma yace idan ma basu isa ba, zai sake siyo wasu. https://twitter.com/NigeriaStories/status/2000500235114631639?t=JwrC2h48JYnkvlH9aX6Aeg&s=19
Kalli Bidiyo da Hotuna yanda Abdulsamad Rabiu BUA ya bayyana cewa Minista Hannatu Musa Musawa tsohuwar matarsa ce

Kalli Bidiyo da Hotuna yanda Abdulsamad Rabiu BUA ya bayyana cewa Minista Hannatu Musa Musawa tsohuwar matarsa ce

Duk Labarai
Me kamfanin BUA, Abdulsamad Rabiu BUA ya bayyana cewa, IMinista Hannatu Musa Musawa tsohuwar matarsa ce. Ya bayyana hakane a wajan taron nasarorin daya samu a kamfaninsa sannan kuma bayan hakan sun rungumi juna inda suka dauki hotuna tare. https://twitter.com/gamawa_amina/status/2000511064929153206?t=_9aQptNsQ_zjFdwCXwUhNg&s=19