Tuesday, February 17
Shadow
Wannan Bidiyon na Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma Wakili tana Rawa tare da Rùngùmàr wani ya dauki hankula

Wannan Bidiyon na Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma Wakili tana Rawa tare da Rùngùmàr wani ya dauki hankula

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma Wakili ta dauki hankula bayan da aka ganta tana rawa tare da rungumar wani a Bidiyo. Wasu dai sun rika cewa danta ne inda wasu ke cewa kaninta ne saboda yanda suka yi kama dashi. Bidiyon ya jawo muhawara sosai. https://www.tiktok.com/@asmee.wakili286/video/7588808148765658389?_t=ZS-92cX8MbQt85&_r=1
Sowore Wanda Kirista ne yace bai yadda da ikirarin shugaban kasar Amurka, Donald Trump ba na cewa yana son ceton Kiristocin Najeriya ba

Sowore Wanda Kirista ne yace bai yadda da ikirarin shugaban kasar Amurka, Donald Trump ba na cewa yana son ceton Kiristocin Najeriya ba

Duk Labarai
Mawallafin Jaridar Sahara reporters kuma dan fafutuka, Omoyele Sowore ya bayyana cewa, bai yadda da ikirarin shugaban kasar Amurka, Donald Trump ba na cewa, wai yana son ceton Kiristocin Najeriya ba. Yace ta yaya Trump zai ce yana son ceton Kiristocin Najeriya amma ya hanasu shiga kasar Amurka? Shugaba Donald Trump dai ya saka tsatstsauran mataki kan 'yan Najeriya dake son shiga kasar Amurka ba tare da banbance musulmi ko Kirista ba. https://twitter.com/sowore/status/2005397646861607248?t=QYuZlJd_H9UzyTcFGdQJ8g&s=19
Kalli Bidiyon yanda Cristiano Ronaldo ya ce Insha Allah zai cimma burinsa

Kalli Bidiyon yanda Cristiano Ronaldo ya ce Insha Allah zai cimma burinsa

Duk Labarai
Cristiano Ronaldo ya lashe gasar gwarzon dan kwallo na gabas ta tsakiya sau 3 a jere. A wajan taron bada kyautar da aka bashi, a cikin jawabinsa, yace insha Allahu zai cimma burinsa. Fadar wannan kalma tasa mutane da yawa, musamman Musulmai jin dadin hakan da fatan cewa Allah yasa wataran ya karbi kalmar Shahada. https://twitter.com/utdnarmi/status/2005358913739485656?t=fgdm3zKLWW8YzOOAStk1yQ&s=19
Da Duminsa: Rashin Lafiyace tasa Shugaba Tinubu ya tafi Turai>>Inji Sowore

Da Duminsa: Rashin Lafiyace tasa Shugaba Tinubu ya tafi Turai>>Inji Sowore

Duk Labarai
Mawallafin jaridar Sahara reporters, Omoyele Sowore yayi zargin cewa, Rashin Lafiya ce tasa aka fitar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zuwa Turai. Hakanan yayi zargin cewa, kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio shima bashi da lafiya. Yace bai kamata ace su rika tatsar kudin Najeriya ba suna kula da lafiyarsu. https://twitter.com/sowore/status/2005368009347461144?t=yby3RtkrB5QOTgwPfMZCiA&s=19
Gwamna Abba Kabir Yusuf zai koma jam’iyyar APC ba tare da Kwankwaso ba

Gwamna Abba Kabir Yusuf zai koma jam’iyyar APC ba tare da Kwankwaso ba

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf na shirin komawa jam'iyyar APC. Hakan ya fito ne daga jaridar Daily Nigerian. Jaridar tace ana tsammanin Abba zai koma APC ne a makon farko na shekarar 2026. Hakanan jaridar tace an yiwa Kwankwaso tayin komawa APC din amma yace ba zai koma ba. Jaridar tace akwai shirin tsige mataimakin gwamnan jihar ta Kano inda za'a baiwa Sulen Garo mataimakin Gwamnan. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2005346746399130068?t=r3jZ53BXohJbwR7aq94qxA&s=19 A wani ci gaba da aka samu game da lamarin, Du 'yan jam'iyyar NNPP musamman masu aiki a gidan Gwamnatin jihar ta Kano sun sanar da cewa sun amince Kwankwaso da Abba su jasu zuwa APC.
Kalli Bidiyon: ‘YarGuda tace wannan gadon ya mata kadan

Kalli Bidiyon: ‘YarGuda tace wannan gadon ya mata kadan

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, 'YarGuda ta bayyana cewa wani gado da Maiwushirya ya nuna mata yace an sai mata saboda aurenta ya kusa ya mata kadan. Ta bayyana cewa babban gado take so irin wanda akewa kowa itama a mata. Shima dai Maiwushiryan abin ya bashi mamaki. https://www.tiktok.com/@maiwushiryabackup/video/7588949937325444372?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7588949937325444372&source=h5_m&timestamp=1766949104&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7568740291232040721&share_link_id...
Kalli Bidiyon: Wani jirgin sama da ya rika shawagi kasa-kasa ya saka Zullumi a zukatan mutane a jihar Bauchi

Kalli Bidiyon: Wani jirgin sama da ya rika shawagi kasa-kasa ya saka Zullumi a zukatan mutane a jihar Bauchi

Duk Labarai
Wani jirgin sama da ya rika shawagi kasa-kasa a jihar Bauchi ya dagawa mutane Hankali. An wani Bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta an ga jirgin mutane na daukarsa Bidiyon da wayarsu. An ji suna cewa basu san me yake nufi dasu ba. https://twitter.com/Engr_imran_mk/status/2004873555297604025?t=5ExJbs9DRHO1PaLCMTsOFw&s=19 Saidai Wasu bayanan sirri sun ce, Jirgin na sojojin Najeriya ne kuma yana aikin tattara bayanan sirri ne.
Da Duminsa: Bayan Khàryn data kai Sokoto, Hankalin kasar Amurka ya koma Jihar Borno, har ta aika jirgin sama

Da Duminsa: Bayan Khàryn data kai Sokoto, Hankalin kasar Amurka ya koma Jihar Borno, har ta aika jirgin sama

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka bayan Khàryn data kai jihar Sokoto, ta kuma aika jirgin leken Asiri zuwa jihar Borno. Me saka ido akan harkar tsaro da tafiye-tafiyen Jiragen sama na tsaro, Brant Philip ne ya bayyana hakan inda yace an samu rahotannin cewa kasar, Amurkar ta aika jirgin leken asiri zuwa Dajin Sambisa dake jihar Borno. Yace sunan jirgin da Amurkar ta aika jihar Borno, Gulfstream V,. Ga abinda ya wallafa da turanci kamar haka: “The United States resumed ISR operations today on *** in the Sambisa forest, Borno State in northeast Nigeria, after a pause of one day following the strikes in Sokoto State,” Philip wrote on X (formerly Twitter).