Tauraruwar Fina-finan Hausa,Rahama Sadau ta yiwa masoyanta gaisuwar barka da shiga sabon wata.
Rahama ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta inda kuma ta saki kayatattun hotunan ta.
Kamfanin mai na kasa,NNPCL ya koka da cewa bashin masu kawo man fetur ya mai yawa.
Kamfanin ya tabbatar da hakan ne ta bakin me magana da yawunsa, Olufemi Soneye inda yace kamfanin na fama da matsalar bashin masu kawo mai.
Yace hakan na barazana ga wadata kasarnan da man fetur.
Saidai ya bayyana cewa, NNPC ba zata yi kasa a gwiwa ba wajan ganin ta ci gaba da gudanar da aiki a matsayin babbar me wadata kasarnan da Man fetur.
Rikicin dan wasan Najeriya, Victor Osimhen da kungiyarsa ta Napoli ya kara kamari inda a yanzu babu tabbacin zai bugawa kubgiyar wasa a wannan kakar duk da yake cewa har yanzu yana kungiyar bai samu tafiya Chelsea kamar yanda ya so ba.
Osimhen dai yaki yin atisaye da kungiyar da tunanin cewa zai barta amma sai ciniki bai kaya ba na komawa Chelsea.
Hakanan kungiyar Napoli ta buga wasanta na farko da Parma kuma ba'a ga Osimhen a ciki ba wanda dama bai buga wasannin Preseason ba.
Kungiyar ta Napoli dai tuni ta baiwa Remolu Lukaku lamba 9 da Victor Osimhen ke goyawa.
A yanzu dai an dakatar da Osimhen daga duka wasanni da atisayen kungiyar ta Napoli kuma bai san makomarsa ba.
Daga: Abbas Yakubu Yaura
Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya ce tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari bai taba son shugaba Bola Tinubu ya gaje shi ba a matsayin shugaban kasa.
Lamido ya kuma ce Buhari bai taba amincewa da tsohon mataimakinsa Yemi Osinbajo ya gaje shi ba, ya kara da cewa tsohon shugaban kasar yana son tsohon shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan ne ya gaje shi.
Lamido ya ci gaba da cewa, babu wanda ya isa ya zama shugaban kasa saboda Tinubu mutum ne jajirtacce kuma mai son kansa.
Da yake magana da jaridar Tribune, Lamido ya ce: “Kafin taron, shi (Tinubu) yana Abeokuta, jihar Ogun, inda ya yi takama da cewa lokaci ya yi da zai mulki Najeriya. Shi kuwa Buhari saboda butulci yana kallo. Bai taba son Tinubu ba. Akwai wanda yake so.
“Bai ma aminta da nas...
Gwamatin Tarayya Ta Sanar Da Shirinta Na Zuba Jarin Dalar Amurka Biliyan 4.8 a Fannin Kiwon LafiyaNajeriya
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ne ya bayyana hakan a yayinda yake karin haske kan sauye-sauyen da gwamnatin ta yi a fannin kiwon lafiya wanda a cewarsa, zai lashe sama da dala biliyan 4.8 wajen zuba jari duk a yunkurin gwamnati na ganin an farfado da ingancin kiwon lafiya a Najeriya tare da magance Kalubalen da ya jima yana addabar bangaren kiwon lafiyar
Shettima, ya bayyana hakan ne a wajen bikin kaddamar da rukunin asibitocin Sahad a birnin Abuja,
"Gwamnatin mu ta kuma Kaddamar da gyare-gyare a kan bangarori huɗu masu mahimmanci wanda suka haɗa: sauya tsarin kula da kiwon lafiya, samar da ingatattun bangarorin binciken lafiya, buɗe Sabbin Cibiyoyin , da ƙa...
Ma'aikacin dake aiki a filin jirgin sama na malam Aminu Kano dake jihar Kano, Auwal Dankode wanda ya tsinci dala $10,000 kwatancin sama da Naira Miliyan 15 ya mayar da ita ga maisu ya samu karin girma.
Auwal ya samu karin girma da kyautar kudi sannan an bashi aikin jakadar hukumar NAHCO da yakewa aiki.
Shugaban hukumar, Mr. Indranil Gupta ne ya bayyana haka inda yace auwal ya nuna kwarewa da jajircewa da gaskiya wajan aikinsa inda ya karfafeshi cewa ya ci gaba da wannan aiki.
Auwal dai ya tsinci kudinne yayin da yake aikin share jirgin saman Egypt Air, kuma nan take ya mika kudin ga shugabansa.
Akwai yiyuwar Shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu zai canja wasu ministoci a majalisarsa ta zartaswa.
Hakan wani mataki ne na cire ministocin da basa tabuka wani abin azo a gani.
Shugaban dai ya jima yana fuskantar matsi akan ya canja ministocin da basa yin aikinsu yanda ya kamata.
A shekarar da ta gabata ne dai shugaban kasar ya kafa wani tsari na auna kokarin ministocin inda yayi gargadin duk wanda ba ya kokari za'a koreshi daga aiki.
BABBAR MAGANA: Bello Ťùŕjì Da Tawagarsa Šùñ Ķwaçe Mòťàŕ Ýàķìn Śòjòji Da Sauran Màķamaì Bayan Wani Artabu Da Suka Ýi.
A wani bidiyon dake dauke da lamarin, an nuno 'ýañ ta'àďďañ sun kewaye motar suna ta murna da shewa.
Jarumin Finafinan Hausa, Yakubu Muhammad Ya Dauki Nauyin Karatun Wasu Yara Guda Biyu Har Zuwa Jami'a.
Jarumin ya dauki nauyin karatun yaran ne bayan ya ga wani bidiyon su a kafar sadarwa inda suke kalaman aluta da 'yan jami'a suke yi. Wanda hakan ya sa ya yi tattaki har zuwa garin Wudil domin ganawa da yaran da kuma iyayensu.