
Hukumar kula da harkar Sadarwa ta kasa, NCC ta bayyana fara duba farashin kiran waya dana aikawa da sako a Najeriya.
Hakan zai sa a kara kudin kiran dana sako kamar yanda Rahotanni suka nunar.
Wani me ruwa da tsaki a harkar sadarwar, Wole Adenekan ya tabbatar da hakan inda yace karin ya zama dole saboda an samu sauye-sauyen tattalin arziki da na kimiyya da fasaha.
Yace maimakon a rika biyan kudi kadan amma ba’a samun sabis me kyau, gara a rika biyan ainahin kudin kiran dana aika sako sabis din ya inganta.
Hakan na zuwane a yayin da ‘yan Najeriya da dama ke kokawa da matsalar tsaro.