Monday, May 12
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Kalli Bidiyo: Dan gidan Ministan Abuja, Wike ya wallafa irin rayuwa kece rainin da yake yi

Kalli Bidiyo: Dan gidan Ministan Abuja, Wike ya wallafa irin rayuwa kece rainin da yake yi

Duk Labarai
Daya daga cikin 'ya'yan Ministan Abuja, Nyesom Wike ya wallafa Bidiyon rayuwar kece Raini da yake. Bidiyon ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda aka ganshi a cikin jirgin sama da kasashen waje da sauran gurare na alfarma. https://twitter.com/GossipMillNaija/status/1921517476505878616?t=XiTAWxRUilQ20N2Hp3eV6Q&s=19 Wasu dai sun bayyana cewa, wannan kudin al'ummar Najeriya ne.
Taron Coci ya watse a Karu Abuja bayan da aka zargi Faston cocin da dirkawa daya daga cikin mabiyansa ciki

Taron Coci ya watse a Karu Abuja bayan da aka zargi Faston cocin da dirkawa daya daga cikin mabiyansa ciki

Duk Labarai
Wata hatsaniya ta faru a Cocin Redeem church dake Karu a babban birnin tarayya, Abuja bayan da aka zargi faston cocin da dirkawa daya daga cikin membobinsa ciki. Rahoton yace faston ya zubar da cikin bayan da ya ga Asirinsa zai tonu. Sannan ya bayar da Naira miliyan 3 toshiyar baki dan kada a tona masa asiri amma duk da haka ana tsaka da taron Lahadi a cocin wani ya masa tonon silili.
Jarabawar JAMB: Jihohin Anambra da Legas ne suka fi yawan masu satar Jarabawar ta 2025

Jarabawar JAMB: Jihohin Anambra da Legas ne suka fi yawan masu satar Jarabawar ta 2025

Duk Labarai
Rahoton da Hukumar JAMB data fitar ya bayyana cewa, jihohin Anambra da Legas ne suka fi yawan dalibai da ake zargi da aikata satar jarrabawar UTME na shekarar 2025, inda aka kama mutane 80 ta hannun 'yan sanda. Shugaban JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Abuja, ranar Juma’a. Ya ce an gano sababbin hanyoyin satar amsa, ciki har da canjin fasalin fuska da yatsun hannu tsakanin ɗalibai da masu yi musu jarrabawa a madadinsu, tare da hadin gwiwar wasu cibiyoyin CBT. Anambra ce ke kan gaba da mutum 14 da ake zargi, inda 13 daga ciki ke fuskantar tuhuma kan amfani da wasu wajen rubuta musu jarrabawa, sannan guda ɗaya na da matsalar daidaito hoton wani da bayanan yatsa. A jihar Legas, an kama mutum tara bi...
Jihar Legas ta hana Masu gidajen haya karbar kudin haya na shekaru 2

Jihar Legas ta hana Masu gidajen haya karbar kudin haya na shekaru 2

Duk Labarai
Jihar Legas ta nemi masu haya da su kai karar duk wani me gida da ya nemi su biya kudin haya na shekara 2. Jami'ar Hukumar kula da gidaje ta jihar, Barakat Bakare ce ta bayyana hakan a wata hira da aka yi da ita a gidan Talabijin TVC. Tace gwamnan jihar na kokarin ganin mutane sun samu gidajen haya da sauki sannan kuma za'a saka ido da tabbatar da an bi doka wajan bayar da hayar.
Mijina ba zai sake neman takarar shugaban kasa ba, Tinubu zamuwa Yakin neman zabe saboda aikinsa na kyau>>Inji Matar tsohon shugaban kasa, Patient Jonathan

Mijina ba zai sake neman takarar shugaban kasa ba, Tinubu zamuwa Yakin neman zabe saboda aikinsa na kyau>>Inji Matar tsohon shugaban kasa, Patient Jonathan

Duk Labarai
Matar tsohon shugaban kasa, Dame Patient Jonathan ta bayyana cewa, Mijinta ba zai nemi takarar shugaban kasa ba. Ta bayyana cewa, Maimakon haka, zata hada kai da matar shugaban kasa, Remi Tinubu dan su yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yakin neman zabe. Ta bayyana hakane a yayin wata kyautar karramawa da aka bata a Abuja. Tace a baya lokacin da mijinta ya fito takarar shugaban kasa a 2011 Itama Remi Tinubu da mijinta shugaban kasa sun taimaka musu.
“Ba na yin TikTok” — Natasha ta karyata bidiyon da aka nuna ta na rawar waƙar Rarara ta ‘Omo Ologo’

“Ba na yin TikTok” — Natasha ta karyata bidiyon da aka nuna ta na rawar waƙar Rarara ta ‘Omo Ologo’

Duk Labarai
"Ba na yin TikTok" — Natasha ta karyata bidiyon da aka nuna ta na rawar waƙar Rarara ta ‘Omo Ologo’ Natasha Akpoti-Uduaghan, sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya, ta nesanta kanta da wani faifen bidiyo da ya karade shafin TikTok wanda ke nuna ta a cikin wani yanayi na raha ta na rawar wata waka da Rarara ya yi wa Shugaba Bola Tinubu mai taken Komo Ologo. A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X , sanatar ta bayyana cewa ba ta da wani shafi a TikTok. “Ba ni da shafin TikTok,” in ji sanatar. “Akwai wasu shafukan bogi da dama da ke amfani da sunana a X (Twitter), Instagram, Facebook da TikTok. Wasu daga cikinsu sun tara mabiya masu yawa.” Ta ce bidiyon da ya karade kafafen sada zumunta an yi shi ne ta amfani da wani tsohon bidiyo daga shekarar 2023 tare da nufin ya...
NDLEA ta kama wata mata da ta ɓoye ƙwayoyi a cikin al’aurar ta

NDLEA ta kama wata mata da ta ɓoye ƙwayoyi a cikin al’aurar ta

Duk Labarai
NDLEA ta kama wata mata da ta ɓoye ƙwayoyi a cikin al'aurar ta. An kama wata mata mai suna Ihensekhien Miracle Obehi da ta rufe kanta da hijabi don fitar da kwayoyi iri daban-daban zuwa kasar Iran ta hanyar boye su a cikin al'aurarta, cikinta da kuma jakarta. Jami'an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) su ka damke ta a filin jirgin sama na Port Harcourt, Jihar Rivers. Obehi, wadda ta sanya hijabi don guje wa binciken tsaro, an cafke ta a zauren tashi na filin jirgin a ranar Lahadi, 3 ga Mayu, 2025, yayinda take ƙoƙarin hawa jirgin Qatar Airline zuwa Iran ta hanyar Doha, bayan samun bayanan sirri. Bayan an bincike ta, an gano tanada kwayoyi guda uku da ta saka a al'aurarta, da wasu manyan kunsoshin kwayoyi guda biyu da aka ɓoye a cikin jakarta, sanna...
Sai kun yi nadamar komawa APC, Kwankwaso ga su Kawu Sumaila

Sai kun yi nadamar komawa APC, Kwankwaso ga su Kawu Sumaila

Duk Labarai
Sai kun yi nadamar komawa APC, Kwankwaso ga su Kawu Sumaila. Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa ‘yan majalisar tarayya da aka zabe su a karkashin jam’iyyar NNPP da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, za su yi nadamar wannan matakin da suka dauka. DAILY NIGERIA ta rawaito cewa wasu daga cikin ‘yan majalisar da suka fito daga NNPP sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a kwanan nan. Cikin wadanda suka koma APC akwai Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kawu Sumaila, da Alhassan Rurm, da sauransu. Sai dai lokacin da ya ke jawabi ga daruruwan magoya bayan NNPP daga karamar hukumar Takai, wadanda su ka ƙi bin Kawu Sumaila zuwa APC, amda suka kai masa ziyara a gidansa a ranar Juma’a, Kwankwaso ya bayyana sauy...
Kalli Bidiyon: Masu zagin mu akan wai yanzu bama wa’azi me zafi irin wanda muke yi Lokacin mulkin Goodluck Jonathan basu da wuta basu da Aljannah kuma basu da Siradi>>Sheikh Kabir Gombe

Kalli Bidiyon: Masu zagin mu akan wai yanzu bama wa’azi me zafi irin wanda muke yi Lokacin mulkin Goodluck Jonathan basu da wuta basu da Aljannah kuma basu da Siradi>>Sheikh Kabir Gombe

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Kabir Gombe ya bayyana cewa masu zaginsu akan cewa basa wa'azi me zafi irin wanda suka yi zamanin Mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan basu da wuta basu da Aljannah. Yace Shi Allahn da suke yi danshi ya sani. Yace kuma ko a lokacin Goodluck Jonathan ba a farkon Mulkin sa suka fara mai wa'azi me zafi ba sai da aka yi wasu abubuwan da basu dace ba. https://twitter.com/el_uthmaan/status/1921317149236183139?t=9JEnJuCvNwroA2j76440sA&s=19 Ana dai ta zargin Malaman Cewa suna samu a jikin Gwamnati ne shiyasa basa iya fada mata gaskiya.
Za A Shafe Makonni Biyu Ana Buɗe Ayyuka Albarkacin Cikar Shugaban Ƙasa Tinubu Shekaru Biyu A Kan Mulki

Za A Shafe Makonni Biyu Ana Buɗe Ayyuka Albarkacin Cikar Shugaban Ƙasa Tinubu Shekaru Biyu A Kan Mulki

Duk Labarai
Za A Shafe Makonni Biyu Ana Buɗe Ayyuka Albarkacin Cikar Shugaban Ƙasa Tinubu Shekaru Biyu A Kan Mulki. Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa shugaban ƙasa Tinubu ya kafa gagarumin tarihin samar da manyan ayyuka masu tasiri a fagen shugabancin Najeriya. Dan haka, za a shafe tsawon makonni biyu ana buɗe ayyukan da ya yi a Abuja ta fannin tituna, ruwa, da sauran ɗumbin ayyukan raya ƙasa, albarkacin cikarsa shekaru biyu a matsayin shugaban ƙasar Najeriya.