Saturday, December 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ni Mutuniyar Kirki ce, bana Shan Ghìyà>>Inji Fitsararriyar mawakiyar Amurka yayin da take shirin zuwa kasar Saudiyya yin waka

Ni Mutuniyar Kirki ce, bana Shan Ghìyà>>Inji Fitsararriyar mawakiyar Amurka yayin da take shirin zuwa kasar Saudiyya yin waka

Duk Labarai
Fitsararriyar mawakiyar Amurka, Cardi B ta bayyana cewa ita mutuniyar kirki ce. Tace bata shan giya kuma tana bin doka. Ta bayyana hakane yayin da take shirin zuwa kasar Saudiyya yin waka. Lamarin ya jawo cece-kuce da yi mata dariya da shagube. https://twitter.com/mymixtapez/status/1999160605308035422?t=iAXjrIfLj-sn5EHvrKy1_w&s=19
Kalli Bidiyon: Dangote ya kaddamar da Naira Biliyan 100 duk shekara dan tallafawa matasa dalibai inganta karatunsu

Kalli Bidiyon: Dangote ya kaddamar da Naira Biliyan 100 duk shekara dan tallafawa matasa dalibai inganta karatunsu

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya kaddamar da tallafin Naira Biliyan 100 duk shekara dan ya rika tallafawa matasa dalibai inganta karatunsu. Shirin zai tallafawa dalibai akalla 155,000 duk shekara. Shirin zai kashe Naira Tiriliyan 1 a cikin shekaru 10 mazu zuwa. https://twitter.com/BashirAhmaad/status/1999044396893749275?t=KdUKmDYL4stFbpLHImsntw&s=19
EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige

EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige

Duk Labarai
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC, ta tsare tsohon ministan ƙwadago kuma tsohon gwamnan jihar Anambra, Chris Ngige. Mai magana da yawun Ngige, Fred Chukwuelobe, ya tabbatar da tsare shi da safiyar ranar Alhamis, bayan wasu rahotanni da aka yaɗa cewa an sace shi. Chukwuelobe ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa, “Ngige yana tare da EFCC. Ba a sace shi ba.” Har zuwa yanzu, EFCC ba ta bayyana dalilin tsare Ngige ba amma kuma ana sa ran hukumar za ta fitar da cikakken sanarwa kan tsare shi da binciken da take yi a kansa. Ngige ya zama mutum na biyu daga cikin tsoffin ministocin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da aka tsare a kwanan nan. Kafin shi, an fara tsare tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami, wanda shima yake hannun EFCC.
Ba zamu yafe abinda aka mana a Zaria ba>>Inji Sheikh Ibrahim Zakzaky

Ba zamu yafe abinda aka mana a Zaria ba>>Inji Sheikh Ibrahim Zakzaky

Duk Labarai
Shekara goma kenan tun bayan kisan da jami’an sojin Najeriya suka yi wa mabiya mazhabar Shi’a a garin Zaria na jihar Kaduna. A wancan lokaci an yi amanna ɗaruruwan mutane ne suka mutu, da dama kuma suka jikkata, bayan zargin rundunar soji cewa mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky sun tare musu hanya. Lamarin ya haddasa suka daga kungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam na duniya, waɗanda suka zargi sojoji da amfani da ƙarfi fiye da kima. Shugaban dandalin tattauna al’amura naƙkungiyar mabiya Shi’a ta IMN a Najeriya, Farfesa Abdullahi Danladi, ya ce duk da wucewar shekaru goma tun bayan faruwar wannan mummunan lamari, har yanzu ba za su taɓa yafe wa waɗanda suka aikata wannan mummunan aikin ba. A tattaunawarsa da BBC, Farfesan ya ce raɗadin abin da ya faru na ci gaba da sosa zuƙatan al’ummar Sh...
Venezuela ta zargi Amurka da sata da kuma fashin teku

Venezuela ta zargi Amurka da sata da kuma fashin teku

Duk Labarai
Venezuela ta zargi Amurka da sata karara da kuma fashin teku bayan da dakarun Amurkan suka kwace wani jirgin ruwa na dakon mai a gabar tekun Venezuela din. Ma'aikatar harkokin wajen ƙasar ta ce matakin wani shiri ne na lalata arzikin makamashi na Venezuela da gangan. Sai dai jami'an Amurka sun ce jirgin ruwan yana safarar man da aka sanya takunkumin sayar da shi ne zuwa Iran kuma kudin da ake samu daga cinkin ana taimaka wa kungiyoyin ta'addanci ne. https://twitter.com/AGPamBondi/status/1998875795151024337?t=ucDi6xifDOsVYsbJydJHJQ&s=19 Lamarin ya kasance ƙarin wata sabuwar dambarwa ta matsin lambar da Amurka ke yi wa shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro - mai ra'ayin gurguzu. Mai dai shi ne babbar hanyar samun kudade na kasar ta Venezuela