Friday, January 2
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Da Duminsa: Sanata Godswill Akpabio yace ya yafewa Sanata Natasha Akpoti yace lauyoyi su janye karan da ya shigar akanta

Da Duminsa: Sanata Godswill Akpabio yace ya yafewa Sanata Natasha Akpoti yace lauyoyi su janye karan da ya shigar akanta

Duk Labarai
Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya ce ya yafewa Sanata Natasha Akpoti abinda ta masa. Sannan yace ya baiwa lauyoyin sa umarnin su janye karar da ya shigar akanta dama duka wasu da ya ke kararsu akan sun bata masa suna. Yace dalilinsa na yin haka shine Faston sa ya masa wa'azi kuma wa'azin ya shigeshi. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2006714564621037783?t=d8iGOafoZPdJz0fJ7bzYbw&s=19
Allah Sarki:An samu wani ya saiwa matashiyar nan da wani yawa wayau ya tafi mata da waya sabuwar waya

Allah Sarki:An samu wani ya saiwa matashiyar nan da wani yawa wayau ya tafi mata da waya sabuwar waya

Duk Labarai
Matashiyarnan da ta ce sun hadu da wani a Shoprite Kano ya mata wayau da sunan yana sonta ya tafi mata da waya, Rahotanni sun ce an samu wani ya sai mata waya. A baya dai, Hutudole ya kawo muku yanda aka ga matashiyar na ta rusa kuka inda tace an tafi mata da waya. Da aka tambayi kudin wayar an ce Naira 95k ne. Saidai a yanzu an samu wani ya sai mata sabuwar waya.
Kalli Bidiyon: A karshe Dai Sheikh Salihu Zaria yayi bayani filla-filla kan Rahotannin dake cewa An afka masa saboda magana kan Haraji

Kalli Bidiyon: A karshe Dai Sheikh Salihu Zaria yayi bayani filla-filla kan Rahotannin dake cewa An afka masa saboda magana kan Haraji

Duk Labarai
Malamin addinin Islama, Sheikh Salihu Zaria ya yi karin haske kan Harin da ake cewa an kai masa saboda yayi magana akan Haraji. Malamin yace ba gaskiya bane, ba'a kai masa hari ba. Yace har ma Karatu yayi, dan haka masu cewa, an kai masa Hari karya suke. Yace kuma sune suka tallata gwamnatin Musulim Muslim kuma a yanzu bata abinda ya kamata dan haka dole su fito su fada. https://www.tiktok.com/@dclhausa/video/7590339768127409430?_t=ZS-92i0aHm9ROy&_r=1
Kalli Bidiyon: A akidar Ahlussunah da kuma koyarwar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) babubinda akace talakawa su dumama Shuwagabannin, kamar yanda Sheikh Salihu Zaria ke cewa>>Inji Dr. Jamilu Aliyu

Kalli Bidiyon: A akidar Ahlussunah da kuma koyarwar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) babubinda akace talakawa su dumama Shuwagabannin, kamar yanda Sheikh Salihu Zaria ke cewa>>Inji Dr. Jamilu Aliyu

Duk Labarai
Malam Dr. Jamilu Aliyu ya bayyana cewa yana tare da Sheikh Salihu zaria game da kin biyan Haraji da gwamnati ke kokarin sakawa Talakawa Saidai yace baya tare da Malam Salihu Zaria akan cewa wai a Dumama 'yan Majalisa, yace ba koyarwa lr Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) bace dumama shuwagabanni. Yace Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi umarni da a yi hakuri idan aka samu shuwagabanni marasa adalci. Malam kuma yace wasa yayi yawa a wa'azin Sheikh Salihu Zaria inda yace ya kamata ya gyara. https://www.tiktok.com/@isah_bello_assalafy_garo/video/7590329793590152468?_t=ZS-92huS6g5bNp&_r=1
Kalli Bidiyon: Bayan da Rahama Saidu ta wallafa wannan Bidiyon da ya jawo cece-kuce sosai, wata tace mata, wata Tace mata “Nòwnùwà sun yi kyau, Allah kawo Kasuwa”

Kalli Bidiyon: Bayan da Rahama Saidu ta wallafa wannan Bidiyon da ya jawo cece-kuce sosai, wata tace mata, wata Tace mata “Nòwnùwà sun yi kyau, Allah kawo Kasuwa”

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Rahama Saidu ta wallafa Bidiyo wanda ya dauki hankula sosai a shafinta na Tiktok. Wata ta mata comment cewa, Nonuwa sun yi kyau, Allah kawo Kasuwa. Saidai abin baiwa Rahama Saidu dadi ba inda ta mayar mata da martani me zafi. https://www.tiktok.com/@rahamasaidu2/video/7590092459124772114?_t=ZS-92hrmmNoPHk&_r=1
Da Duminsa: Rahotanni sun ce wasu da ba’a san ko su wanene ba sun Afkawa Sheikh Salihu Zaria biyo bayan maganar da yayi kan cewa ba za’a biya kudin Haraji ba

Da Duminsa: Rahotanni sun ce wasu da ba’a san ko su wanene ba sun Afkawa Sheikh Salihu Zaria biyo bayan maganar da yayi kan cewa ba za’a biya kudin Haraji ba

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wasu da ba'a san ko su wanene ba sun Afkawa Malam Sheikh Salihu Zaria biyo bayan cewa da yayi ba za'a biya kudin Haraji ba. Sheikh Salihu Zaria dai yace duk wanda ya zo karbar Haraji a wajan Talakawa zai dandana kudarsa. A cewa wanda ya kawo Rahotanni yace an kaiwa malam farmakinne dalilin wannan wa'azi da yayi. https://www.tiktok.com/@ib_danfilm01/video/7590153453876301086?_t=ZS-92honfTPePw&_r=1
Allah Sarki Duniya, Abokan Anthony Joshua sun zo Najeriya da kafafunsu, gashi yanzu za’a mayar dasu kasashensu a akwatunan Gawa

Allah Sarki Duniya, Abokan Anthony Joshua sun zo Najeriya da kafafunsu, gashi yanzu za’a mayar dasu kasashensu a akwatunan Gawa

Duk Labarai
An tafi da gawar Abokan dan damben Najeriya, Anthony Joshua zuwa kasashensu. Abokan Anthony Joshua su biyu ne suka rasa rayukansu a Hadarin motar da ya rutsa das a kan hanyar Legas zuwa Ibadan. Shi kuma Anthony Joshua ya ji raunuka aka kwantar dashi a Asibiti amma ya ji sauki an sallameshi. https://twitter.com/Cleverlydey4u/status/2006622653919146317?t=9mfXxwQKg-_NWaE2-bQcXA&s=19
Ana Rade-radin cewa, Akwai yiyuwar shugaba Tinubu ya dauki Shugaban jam’iyyar APC amatsayin mataimaki a 2027

Ana Rade-radin cewa, Akwai yiyuwar shugaba Tinubu ya dauki Shugaban jam’iyyar APC amatsayin mataimaki a 2027

Duk Labarai
Rade-radi na yawo a kafafen sada zumunta cewa, akwai yiyuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai dauki Shugaban jam'iyyar APC a matsayin mataimakinsa a 2027. A baya dai an ta yada cewa, Tinubu zai dauki wani wanda ba Kashim Shettima ba a matsayin mataimakinsa a zaben 2027. https://twitter.com/Pharmacio001/status/2006390423208480984?t=KPEcFr0W1vB0CfLcxTxopA&s=19