Tuesday, January 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Allah Sarki: Wannan Fasto ne da ya karbi Shahada ranar Kirsimeti

Allah Sarki: Wannan Fasto ne da ya karbi Shahada ranar Kirsimeti

Duk Labarai
Wannan wani fasto ne Bayerabe da ya karbi Shahada Ranar Kirsimeti. Yace yana cikin karanta Baibul ne sai ya je inda yaga cewa Jesus yayi Sallah irin ta musulmai. Yace kuma yaga inda Jesus ya la'anci masu bauta ta hanyar rawa da waka, yace shine ya je ya nunawa faston dake gaba dashi. Amma sai yace masa wai kuskurene aka yi. Yace to shine yace waye yayi kuskuren, Jesus ne yayi kuskuren ko wanene? Shine fa ya fara neman yanda zai musulunta inda yace bari yaje wajan malaman Hausawa yasan sune ba zasu karbi kudi da yawa ba. Shine ya tambaya cewa nawa malaman Hausawa ke karba idan za'a shiga Musulunci? Aka ce masa kyautane shine ya musulunta. https://www.tiktok.com/@yusuf__t1/video/7588036613431741717?_t=ZS-92e4Qk61UlU&_r=1
Wata Sabuwa: Daya daga cikin manyan malaman Arewa ya nemi auren matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari

Wata Sabuwa: Daya daga cikin manyan malaman Arewa ya nemi auren matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa daya daga cikin manyan malaman Arewa ya nemi auren matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari. Saidai tace masa bata so kuma ya kiyaye ta idan ba haka ba zata tona masa Asiri. Daya daga cikin malam ne ya tona wannan asiri. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7589412053593459980?_t=ZS-92e3HqKAYxE&_r=1 A baya dai, Hajiya A'isha Buhari tace bata da niyyar yin aure bayan rasuwar Mijinta, tace zata ci gaba da rayuwa tsakanin 'ya'ya Da jikoki ne.
Na yi magana da Anthony Joshua da mahaifiyarsa, bayan Khàdàrìn da ya rutsa dashi>>Inji Shugaba Tinubu

Na yi magana da Anthony Joshua da mahaifiyarsa, bayan Khàdàrìn da ya rutsa dashi>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, Yayi magana da dan Damben Najeriya, Anthony Joshua da mahaifiyarsa. Yace ya yiwa AJ gaisuwar abokansa 2 da suka rasu a hadarin sannan ya masa fatan samun sauki. Shugaba Tinubu yace AJ yace masa yana samun kulawa me kyau. Yace kuma yawa mahaifiyar AJ jaje inda tace tana godiya da kulawar da shugaban kasar ya nuna musu.
Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je kallon AFCON a kasar Morocco yace Najeriya giwar banza ce a Afrika Amma kasar Morocco tafi ta ci gaba

Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je kallon AFCON a kasar Morocco yace Najeriya giwar banza ce a Afrika Amma kasar Morocco tafi ta ci gaba

Duk Labarai
Dan Najeriya, Isaac Fayose da ya je kallon gasar cin kofin Afrika da ake bugawa a kasar Morocco, watau AFCON ya bayyana cewa Kasar ta Morocco tafi Najeriya ci gaba. Yace Girman Najeriya a baki ne kawai. Yace Morocco ga tsafta ga ci gaba. https://twitter.com/dammiedammie35/status/2005677250134610233?t=7x4hyX18ESbzeGGiSaENkw&s=19
Mutane 2 da suka Rako Dan Danben Najeriya, Anthony  Joshua daga kasar waje sun rasu a Khàdàrìn da ya rutsa dashi

Mutane 2 da suka Rako Dan Danben Najeriya, Anthony Joshua daga kasar waje sun rasu a Khàdàrìn da ya rutsa dashi

Duk Labarai
Mutane biyu wanda abokanshine da suka rako Shahararren dan ben Najeriya, Anthony Joshua gida sun rasu a hadarin daya rutsa dashi. Kuma daya daga cikin mutanen Musulmi ne. Wani abin tausai shine Bidiyon su da aka gani yana ta yawo a kafafen sada zumunta inda suke cewa gasu a hanya zasu raka Anthony Joshua Najeriya. https://twitter.com/instablog9ja/status/2005657900635873434?t=W8raaus8ctGOZbYKNXvDmw&s=19
Kalli Bidiyon: Zee Diamond, watau Talatuwa ta cikin shirin Labarina na fama da rashin Lafiya ana neman Naira Miliyan 25 a kaita kasar Egypt

Kalli Bidiyon: Zee Diamond, watau Talatuwa ta cikin shirin Labarina na fama da rashin Lafiya ana neman Naira Miliyan 25 a kaita kasar Egypt

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Tauraruwar fina-finan Hausa ta cikin shirin Labarina, Zee Diamond wanda aka fi dani da Talatuwa tana kwance ba lafiya. Tana neman Naira Miliyan 25 dan a kaita kasar Egypt a mata aiki. Rahoton yace ta sayar da Gidan abincinta, ta sayar da motarta da duk wani abu data mallaka sannan ta samu taimako daga. Malam Aminu Saira. Rarara A'ishatulhumaira Dan Small da sauransu. Yanzu dai an hada Naira Miliyan 18, Naira Miliyan 7 ake nema dan kaita kasar Egypt. https://www.tiktok.com/@buroshi_mawaka_sokoto/video/7589251434281962772?_t=ZS-92d794AxhLt&_r=1