Sunday, March 8
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ji Bukatun da Kwankwaso ya gabatarwa da APC kamin ya yadda ya koma jam’iyyar inda APC din tace ba ta yadda ba zarinsa yayi yawa

Ji Bukatun da Kwankwaso ya gabatarwa da APC kamin ya yadda ya koma jam’iyyar inda APC din tace ba ta yadda ba zarinsa yayi yawa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana game da bukatun da Kwankwaso ya mikawa jam'iyyar APC kamin ya yadda ya koma jam'iyyar. Saidai APC din ta ki amincewa da wadannan bukatu. Rahotanni sun bayyana cewa Kwankwaso ya nemi a bashi iko da kaso 20 cikin 100 na jam'iyyar sannan a bashi kujerar mataimakin shugaban kasa. Saidai APC din ta ki amincewa da hakanninda tace kujerar mataimakin shugaban kasa ba zaa baiwa kowa ba. Rahoton yace dalili kenan da Kwankwaso yaki komawa APC din.
Yayin da ake ta cece-kuce akan murtuke fuska da Madina Maishanu ta yi yayin hira da Kwankwaso, ‘yan Kwankwasiyya sun nemo wata tsohuwar hira da ta yi da Sheikh Daurawa inda aka ga tana ta dariya

Yayin da ake ta cece-kuce akan murtuke fuska da Madina Maishanu ta yi yayin hira da Kwankwaso, ‘yan Kwankwasiyya sun nemo wata tsohuwar hira da ta yi da Sheikh Daurawa inda aka ga tana ta dariya

Duk Labarai
Murtuke fuskar da ma'aikaciyar BBChausa, Madina Maishanu ta yi yayin hira da Kwankwaso ya dauki hankula sosai. Wasu musamman 'yan Kwankwasiyya sun rika sukarta inda wasu kuma suka rika cewa hakan ya kamata ta yi lura da cewa matar aurece kuma uwa. Saidai 'yan Kwankwasiyyar sun nemo wani tsohon Bidiyon ta inda aka ga tana hira da malamin addinin Islama, Sheikh Aminu Daurawa tana dariya. https://twitter.com/i/status/2016930803976954281
Da Duminsa:An kama wani dan Fim cikin wadanda akw zargi da yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Da Duminsa:An kama wani dan Fim cikin wadanda akw zargi da yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Duk Labarai
Rahotanni daga kafar Premium times sun bayyana cewa, an kama dan fim din kudu me suna Stanley Amandi saboda hannu a yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki. Rahoton yace sojojij sun dauki Stanley Amandi aiki ne dan ya musu aikin yada farfaganda akan Jhuyin mulkin. Saidai da yawa sun bayyana mamakin kamashi inda wasu ke cewa ba'a wani sanshi sosai ba, irin wannan aikin sananne ake baiwa yawanci.
Kalli Bidiyon: A karshe dai an yi magana da matarnan data kori mahaifiyarta daga gidanta saboda bata biya kudin haya ba

Kalli Bidiyon: A karshe dai an yi magana da matarnan data kori mahaifiyarta daga gidanta saboda bata biya kudin haya ba

Duk Labarai
Matarnan da ta baiwa mutane mamaki saboda korar mahaifiyarta da 'yan uwanta daga gidanta saboda basu biya kudin haya ba an samu zantawa da ita Rahotanni dai sun bayyana cewa, sun biyata Naira dubu 70 amma babu cikon dubu 30 a kudin shine tace su tashi daga gidan. Saidai da aka kirata ta yi ta kame-kame. https://www.tiktok.com/@socialcare74/video/7600703268276145428?_r=1&_t=ZS-93UHf0hYbTM
Gwamnatin tarayya zata gina Titin jirgin kasa na cikin gari a Kano irin wanda ake gani a kasashen Turawa

Gwamnatin tarayya zata gina Titin jirgin kasa na cikin gari a Kano irin wanda ake gani a kasashen Turawa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya zata gina titin jirgin kasa na cikin gari da zai rika jigilar mutane a jihar Kano. Hakan ya fitone daga bakin gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf. Yace Gwamnatin zata kashe Naira Tiriliyan 1 wajan gina wannan titin jirgin. Ya bayyana cewa wannan na daga dalilan da suka sa ya koma jam'iyyar APC dan hada kai da Gwamnatin tarayya wajan kawowa jihar Kano ci gaba.
Da Ganduje ya cireshi wani gari ya kaishi, amma mu ba zami yi haka ba, ina rokon A kaishi Koda Wudil ne>>Inji Sarkin Dawaki

Da Ganduje ya cireshi wani gari ya kaishi, amma mu ba zami yi haka ba, ina rokon A kaishi Koda Wudil ne>>Inji Sarkin Dawaki

Duk Labarai
A yayin da ake rade-radin cewa, Gwamnatin Kano zata sauke Sarki Muhammad Sanusi II, Wani Bidiyon Sarkin Dawaki ya bayyana. Inda aka ji yana cewa, Ganduje da ya saukeshi, wani gari ya kaishi, amma su ba zasu yi haka ba, yace suna rokon ko Wudil ne a kaishi. Ya bayyana cewa kaninsa ne. https://twitter.com/i/status/2016814073669640324
Shin da gaske Gwamnatin Kano tace zata sauke Sarki Sanusi?

Shin da gaske Gwamnatin Kano tace zata sauke Sarki Sanusi?

Duk Labarai
Rahotanni sun karade kafafen sada zumunta cewa wai Gwamnatin Kano tace zata sauke me martaba sarkin Kano, Muhammad Sanusi II. Wasu kuma na cewa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya fara shirin sauke sarkin bayan komawarsa jam'iyyar APC. Saidai duka wannan babu sahihancin labarin ko daya. Abinda muka sani shine, Kwaishinan yada labarai, Ibrahim Waiya ya bayyana cewa, Gwamnatin na shirin kawo karshen rikicin masarautar ta Kano. ya bayyana cewa, za'a dauki matakin sulhu da kuma tattaunawa da masu ruwa da tsaki a lamarin dan ganin an kawo karshen rikita-rikitar masarautar ta Kano.
An baiwa mataimakin Gwamnan Kano umarnin sauka daga mukaminsa

An baiwa mataimakin Gwamnan Kano umarnin sauka daga mukaminsa

Duk Labarai
Kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya ya baiwa mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam Gwarzo Umarnin sauka daga mukaminsa. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi inda yace Gwamna da mataimakinsa na tafiya a tikiti daya ne dan haka mataimakin Gwamnan idan ba zai iya bin Abba ba, abu mafi kyawu da zaiyi shine ya sauka daga mukaminsa. Ya kara da cewa tunda dai yaga ba zai iyawa jagoransa biyayya ba kawai ya sauka daga mukamin.