Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Yahya Kenan a wannan Bidiyon nata da aka ganta a wajan wani biki.
Bidiyon dai ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa shigar tata bata dace ba
https://www.tiktok.com/@mistinbestiebackup/video/7544876237164924168?_t=ZS-8zLd5QUaC6j&_r=1
Tsohon gwamnan jihar Kaduna malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa yayi iya lissafinsa bai ga ta yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sake con zabe ba a 2027.
Ya bayyana hakane hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace Tinubu na 3 zaizo a zaben.
Yace amma akwai yiyuwar za'a yi saben zagaye na biyu dan da wuya a samu wanda yayi nasara a zagayen farko.
Yaron dan Damisa, dan daba na Kaduna daya addabi mutane ya sake fitar da Bidiyo a karo na biyu inda yake cewa ya ga ana ta buga labarinsa.
Ya nanata gargadinsa inda yace zasu yi maganin masu murna da mutuwar me gidansu.
https://www.tiktok.com/@abdulrahamanaliyukafita/video/7544690317098847493?_t=ZS-8zLaaQjtnl3&_r=1
Jam'iyyar APC ta lashe ƙananan hukumomi 20 cikin 23 a zaɓen ƙananan hukumomi jihar Rivers da aka gudanar a jiya Asabar.
A ɗaya ɓangaren kuma, jam'iyyar PDP mai mulki a jihar, ta samu nasarar lashe ƙananan hukumomi uku, kamar yadda hukumar zaɓen jihar ta sanar.
Dakataccen gwamnan jihar, Siminalayi Fubara ya sha kaye a ƙaramar hukumarsa ta Opobo-Nkoro, inda ɗan takarar jam'iyyar APC ya lashe zaɓen.
Shugaban hukumar zaɓen, Dr Michael Odey ne ya sanar da sakamakon zaɓen a hedkwatar hukumar da ke titin Aba a Fatakwal kamar yadda jaridar Punch mai zaman kanta ta ruwaito.
A bara dai an yi wani zaɓen, inda Fubara ya tsayar da na hannun damarsa a jam'iyyar APP, inda suka doke ƴan takarar Wike a zaɓen, amma mutanen tsohon gwamnan suka je kotu, inda aka yi ta tafka shari'a har k...
Malami me wa'azi a Tiktok, Dr. Hussain ya bayyana cewa, abinda wasu 'yan darija suke yi na "Shirka" yafi abinda dan daba, Habu Dan Damisa da aka kashe a Kaduna na kisan mutane ba gaira babu dalili.
Malamin ace karkari dai ace habu yayi shaye-shaye ko kisa da sauransu, yace to hakan bai kai shirka ba a wajan Allah.
Sannan malamin yace Dabbaci da jahilci ne murna da mutuwar Dan Damisa, Addu'a ya kamata a yi masa.
https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7544116373421690168?_t=ZS-8zKrppT3L0a&_r=1
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ya shirya zuwa Kasa me tsarki dan tsinewa Azzalumai.
Ya bayyana hakane a Bidiyon jawabinsa biyo bayan harin da 'yan daba suka kai suka tarwatsa taronsu na jam'iyyar ADC ranar Asabar.
El-Rufai ya bayyana cewa, ya tsinewa wadanda suka aikata wannan abu.
https://www.tiktok.com/@mohammed.adamu69/video/7544467195057786130?_t=ZS-8zKqoveRqTZ&_r=1
Gwamnan jihar Katsina, Umar Dikko Radda ya bayyana cewa, Hotunan da aka rika yadawa inda aka ganshi yana daukar hoto a kasashen Turawa tsaffin hotunane.
Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi.
!A lokacin da aka kai hari wani kauyen Mantau dake Malunfashi jihar Katsina inda aka kashe masallata da yawa, an rika yada hotunan inda aka rika cewa, Gwamna na can kasashen Turai yana hutawa yayin da aka kashe mutane a jihar Katsina.
Gwamna Dikko Radda yace neman lafiya yaje, kuma yace a wancan lokacin shi ba gwamnan jihar Katsina bane, sabida ya mika ragamar mulki a hannun mataimakinsa.
A jiya ne dai rahotanni suka bayyana cewa, An kaiwa taron jam'iyyar ADC hari a Kaduna inda aka lalata dukiyoyi.
Taron wanda tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya jagoranta ya dauki hankula sosai.
Daga baya, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya fito inda yake bayyana zargin Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani da daukar nauyin wadanan 'yan daban.
https://www.tiktok.com/@saiduturakikd/video/7544443730007297301?_t=ZS-8zKfdtPSAaW&_r=1
https://www.tiktok.com/@saiduturakikd/video/7544443928754294037?_t=ZS-8zKfgQsbAG1&_r=1