Monday, February 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Rikicin jam’iyyar APC ya kara kazancewa, Sakataren jam’iyyar ya mayarwa Wike da martani

Rikicin jam’iyyar APC ya kara kazancewa, Sakataren jam’iyyar ya mayarwa Wike da martani

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Rikicin Jam'iyyar APC ya kara ci gaba da kazancewa inda ake cacar baki tsakanin Ministan Abuja Nyesom Wike da sakataren jam'iyyar APC din, Ajibola Basiru. Ajibola Basiru ya bayyana cewa, kamata yayi Wike ya sauka daga mukamin nasa saboda munanan kalaman da yayi akan jam'iyyar APC. Wike a wajan taron da yayi a jihar Rivers yace duk wanda ke son yi musu katsalandan a siyasar jiharsu ta Rivers, zai kwashi kashinsa a hannu. iHakan na zuwane dai yayin da rikici tsakanin Gwamnan Rivers, Simi Fubara da Wike din ke kara kazanta. Wike ya dage cewa, Fubara ba zai tsaya takara ba a karo na biyu.
Mahaifiyarmu ce tasa muka fito muka yi Bidiyon akan babanmu

Mahaifiyarmu ce tasa muka fito muka yi Bidiyon akan babanmu

Duk Labarai
'Yan matannan da suka fito suka bayyana cewa ba zasuwa mahaifinsu addu'a ba bayan rasuwarsa sun ce mahaifiyarsu ce ta sakasu. Sun bayyana cewa, kuma duk masu zaginsu, suna fatan Allah ya baiwa 'ya'yansu mazaje irin mahaifinsu. https://www.tiktok.com/@fatima.yakubu54/video/7591800870786829589?_t=ZS-92pBiVULCjZ&_r=1 Yan matan dai sun dauki hankula bayan da suka bayyana suna murna da rasuwar mahaifinsu inda suka ce ya yaddasu bai musu komai ba, mahaifiyarsu ce ke wahala dasu har suka girma. Marikiyarsu wadda 'yar uwa ce a wajan Mahaifiyarsu ta bayyana cewa, sun yi hakanne dan ya zama wa'azi ga sauran maza masu irin wannan hali.
Wata Sabuwa: Ana rade-radin akwai yiyuwar tsohon Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar zai koma jam’iyyar ADC

Wata Sabuwa: Ana rade-radin akwai yiyuwar tsohon Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar zai koma jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Jigawa na cewa, akwai yiyuwar Tsohon gwamnan jihar kuma tsohon Ministan tsaro, Abubakar Badaru ,ai bar jam'iyyar APC zuwa ADC. Rahoton yace hakan na zuwane yayin da baraka ke ci gaba da bayyana a tsakanin tsohon Ministan da magajinsa gwamna me ci na yanzu, watau Namadi. https://twitter.com/i/status/2008108500493197502
Da Duminsa: An samu Baraka a jam’iyyar APC, ji maganganu marasa dadi da Wike yake gayawa shugaban kasa

Da Duminsa: An samu Baraka a jam’iyyar APC, ji maganganu marasa dadi da Wike yake gayawa shugaban kasa

Duk Labarai
Wani Bidiyon Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya bayyana inda aka jishi yana wata barazana. An ji Wike na barazanar ne a wajan wani taron siyasa a jiharsa. Ya bayyana cewa mutum kada ya zo ya kawo musu abinda ba shi kenan ba a jihar Rivers. Wike bai fadi da wanda yake ba inda yace mutum ya tambayi abinda ya faru da wadanda suka yi yunkurin yiwa jihar Rivers kutse a baya. saidai wasu sun ce da sakataren Jam'iyyar APC yake inda wasu kuma ke cewa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yake. https://twitter.com/i/status/2008170575286419869