Friday, December 5
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Abu na kara Zafafa: Kalli sabon Bidiyon da Hadiza Gabon ta saki dan baiwa Magoya bayan Adam A. Zango dake sukarta Haushi

Abu na kara Zafafa: Kalli sabon Bidiyon da Hadiza Gabon ta saki dan baiwa Magoya bayan Adam A. Zango dake sukarta Haushi

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta saki sabon Bidiyon dan baiwa Magoya bayan Adam A. Zango dake sukarta Haushi. Ta saki Bidiyo ne a Tiktok inda ta dora wakar Gambara da Dapboy ne suna Lokaci. https://www.tiktok.com/@hadizaaliyugabon/video/7579685550538362134?_t=ZS-91v8pGVhlC5&_r=1 Fada tsakanin Magoya bayan Adam A. Zango da Hadiza Gabon ya samo Asali ne bayan da ta saka hotunan wasu jarumai a dakin da take hira da mutane amma ba'a ga hoton Adam A. Zango ba. Magoya bayan Adam A. Zango sun rika kiranta da butulu. Saidai a dazu ta musu martani a Instagram inda tace mutum da gidansa ya kamata ace zai iya yin fendin da ya ga dama.
Kalli Bidiyon: Tauraruwar fina-finan Hausa, Samha M. Inuwa ta yi raddi kan zargin da ake cewa ta yi Bìdìyò tsyràrà, babu kaya a jikinta

Kalli Bidiyon: Tauraruwar fina-finan Hausa, Samha M. Inuwa ta yi raddi kan zargin da ake cewa ta yi Bìdìyò tsyràrà, babu kaya a jikinta

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Samha M. Inuwa ta yi karin haske kan zargin da ake wai ta saka Bidiyon a shafinta na Tiktok babu kaya a jikinta. Samha tace ba gaskiya bane akwai kaya a jikinta kawaidau mutane sun ga abinda suke son ganine. Tace 'yan uwa da abokan arziki sun yi ta kiranta dan jawo hankalinta kan Bidiyon kuma aka sata ta gogeshi. Tace amma ba tsirara take ba akwai kaya a jikinta. https://www.tiktok.com/@samha_m_inuwa/video/7579631993542036754?_t=ZS-91v6nnCl9hB&_r=1
Da Duminsa:A karshe dai majalisa ta amince da Janar Christopher Musa a matsayin sabon Ministan tsaro

Da Duminsa:A karshe dai majalisa ta amince da Janar Christopher Musa a matsayin sabon Ministan tsaro

Duk Labarai
Bayan Tambayoyi da dambarwa, Majalisar Dattijai ta amince da Janar Christopher Musa a matsayin Ministan tsaro. Hakan na zuwane bayan da aka kammala tantanceshi kuma sanatocin suka gamsu da irin amsoshin da ya basu. Janar Christopher Musa zai fuskanci kalubale sosai a matsayin ministan tsaro duba da irin matsalolin tsaron da ake fama dasu a sassa daban-daban na kasarnan.
Gwamna Dauda Lawal Dare ya baiwa Shugaba Tinubu sharadin sauke Matawalle daga karamin Ministan tsaro kamin ya koma APC

Gwamna Dauda Lawal Dare ya baiwa Shugaba Tinubu sharadin sauke Matawalle daga karamin Ministan tsaro kamin ya koma APC

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa, Gwamnan jihar, Dauda Lawal Dare ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sharadin sauke Matawalle daga Ministan tsaro kamin ya yadda ya koma jam'iyyar APC. Jaridar Sunnews ta bayyana cewa, a baya gwamnan ya zauna da shugaban kasa Tinubu a Paris tare da gwamnonin Taraba da Enugu inda ya bayyana aniyarsa ta komawa APC. A yanzu da Muhammad Badaru Abubakar ya sauka daga ministan tsaro, Gwamna Dauda ya sake dawowa da bukatarsa inda yace a sauke Matawalle daga karamin Ministan tsaro shi kuma zai koma APC. Yayi Alwashin jawo mutane da yawa mabiyansa zuwa jam'iyyar ta APC a jihar Zamfara.
Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Dambarwa ta barke a majalisa inda wasu sanatoci suka ce a bar Janar Christopher Musa ya wuce amma wasu sukace basu yadda ba sai an masa tambayoyin da suka kamata

Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Dambarwa ta barke a majalisa inda wasu sanatoci suka ce a bar Janar Christopher Musa ya wuce amma wasu sukace basu yadda ba sai an masa tambayoyin da suka kamata

Duk Labarai
An samu dambarwa a majalisar Dattijai yayin tantance janar Christopher Musa a matsayin Ministan tsaro. Sanata Sani Musa daga jihar Naija ya nemi a bar Janar Christopher Musa ya wuce kamar yanda aka sabawa ministocin da aka aika majalisar dan a tantancesu. Yace Janar Musa tsohon sojane sannan kuma duk tambayoyin da suke masa yanzu sun taba masa irinsu a baya dan haka shi a shawarce yana ganin a kyaleshi ya wuce kawai. Saidai bai samu goyon bayan sauran 'yan majalisar ba inda suka ce ya kamata a tsaya a masa tambayoyin da suka kamata. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1996240738586153221?t=RWLtj3y8T64C4iwGVKBp6g&s=19
Mun Baka Wata 6 idan baka tabuka abin azo a gani ba, zamu sa a tsigeka>>Majalisar Tarayya ta gayawa Janar Christopher Musa

Mun Baka Wata 6 idan baka tabuka abin azo a gani ba, zamu sa a tsigeka>>Majalisar Tarayya ta gayawa Janar Christopher Musa

Duk Labarai
Sanatoci a majalisar Dattijai sun bayyanawa janar Christopher Musa cewa, sun bashi watanni 6 su ga kokarinshi a wajan magamce matsalar tsaro. Sun ce idan bai tabuka komai ba har watanni 6 suka wuce to lallai zasu bada shawarar a tsigeshi a matsayin Ministan tsaro. Sun bayyana hakane yayin tantance shi a zauren majalisar. https://twitter.com/thecableng/status/1996234023127965814?t=i8Ff53GnNIU2bHJ1A3gfVw&s=19
Burin kowane Tshàgyèràn Dhàjì dake kasashen Afrika shine ya zo Najeriya saboda a tunaninsu Najeriya akwai kudi>>Inji Janar Christopher Musa

Burin kowane Tshàgyèràn Dhàjì dake kasashen Afrika shine ya zo Najeriya saboda a tunaninsu Najeriya akwai kudi>>Inji Janar Christopher Musa

Duk Labarai
Janar Christopher Musa ya bayyana cewa, Burin kowane dan Bindiga a kasashen Afrika shine ya zo Najeriya saboda tunaninsu a Najeriya akwai kudi. Ya bayyana hakane a lokacin tantancesa a majalisar Dattijai. Ya kara da cewa zai hada kai da sauran ma'aikatun tarayya da kuma jami'an tsaro da kasashe makwabtan Najeriya da dauransu dan samar da tsaro. https://twitter.com/dammiedammie35/status/1996228876444340649?t=mUwYTwatPHCs2AXDYSIgcg&s=19