Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da shugaban kamfanin Google, Sundar Pichai a kasar Faransa.
Wannan hoton ganawar nasu ne.
Da yake magana akan ganawar tasu, Sundar yace sun tattauna kan yanda za'a samu ci gaban fasahar zamani ta AI a Najeriya.
Dan siyasa a jiar Kano, Dan Balki Kwamanda ya bayyana nadama kan jawo hankalin mutane da yayi suka zabi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaban kasa.
Yace yayi nadamar yakin neman zaben da yawa Tinubu.
Yace tunda yake a rayuwarsa bai taba yin abinda yayi nadamarsa sosai ba kamar yiwa Tinubu yakin neman zabe.
Yace dalili kuwa shine alkawuran da Bola Ahmad Tinubu ya dauka be cika ba kuma mutane na cikin matsananciyar wahala.
Ya bayyana hakane a watan hira da gidan Jaridar Daily Trust suka yi dashi inda yace yana neman yafiyar wadanda ya yaudara.
Rahotanni daga hukumar kula da wutar Lantarkin Najeriya me suna National Grid sun bayyana cewa, wutar ta samu matsala gaf da karfe 12 na rana yau.
Hukumar tace wani sashe na kasarnan ya fada Duhu.
Suce nan gaba kadan za'a samu cikakken bayani kan lamarin.
Majalisar tarayya ta tuhumi shugaban 'yansandan Najeriya, (IGP), Kayode Egbetokun bisa bacewar Bindigu 3,907 a hannun 'yansandan.
Hakanan an masa tambayoyi game da aikata ba daidai ba da kudi a shekarar 2019.
Shugaban 'yansandan da farko ya baiwa majalisar hakuri kan rashin amsa gayyatar da suka masa.
Sannan ya wakilta mataimakinsa, AIG Suleiman Abdul ya wa 'yan majalisar jawabi kan tambayoyin batan kudaden da suke masa.
Saida ya kasa bayar da gamsashshiyar amsa game da bacewar Bindigun inda suka nemi a shiga tattaunawar sirri a kori 'yan jarida daga dakin taron.
Saidai 'yan majalisar sun ki amincewa da wannan kira inda suka ce shugaban 'yansandan ya kkma ya nemo amsar tambayoyin da suka masa.
Juna-biyun da na ke ɗauke da shi ba shi da alaƙa da wani gwamna - Jaruma Nengi
Nengi Hampson, tsohuwar jaruma a shirin fim na gasar Big Brother Naija (BBNaija), ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sadarwa cewa tana dauke da juna biyu da wani gwamna a Najeriya ya yi mata.
Jaridar TheCable ta rawaito cewa rahotannin farko sun yi ikirarin cewa jarumar mai shekara 27 ta haifi jariri ga wani gwamna mai shekara 65 kuma har ta zama matarsa ta biyar.
A wani rubutu da ta wallafa kwanan nan a shafin X, Nengi ta bayyana takaicinta game da wannan jita-jita, tana mai cewa da ta sani ma da ta kau da kai daga jita-jitar.
Sai dai ta ce dole ta yi magana saboda abin ya shafi mutanen da ta ke girmamawa sosai.
Jarumar ta jaddada cewa ba za ta bari wannan jita-jita ta bata rayuwarta ko t...
Biyo bayan karin kudin kiran waya dana data da kamfanonin sadarwa suka yi, majalisar tarayya ta yunkuro dan dakatar da karin.
Hukumar sadarwa ta kasa, NCC tuni ta amincewa kamfanonin sadarwar su kara kaso 50 cikin 100 na kudin da suke caji.
Saidai kungiyoyin fafutuka da suka hada dana Kwadago, NLC da TUC sun ce basu amince da wannan kari ba.
'Yan majalisar ta wakilai a ranar Talata sun baiwa ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani umarnin ya dakatar da kari kudin kiran wayar inda suka ce 'yan Najeriya ba zasu iya biya ba musamman a wannan yanayi na matsin tattalin arziki.
Sai ranar Litinin me zuwa ne ya kamata a fara yin karin kudin kiran dana data, amma MTN a matsayin kamfanin sadarwa mafi girma a Najeriya Tun a wannan satin sun fara kara kudin kira.
A wata hira da ja...
Masu son kafa kasar Biafra sun nuna Gwamnoni 40 na kasar tasu da suke son kafawa.
An ga bidiyon yanda suke nuna Gwamnonin a kafafen sada zumunta yana yaduwa sosai.
Shuwagabannin kungiyar biyu watau Nnamdi Kanu da Simon Ekpa duka suna hannu inda hukumomi ke zarginsu da aikata laifuka daban-daban.
Kalli Bidiyon anan
Wata me yin abinci sayarwa ta dauki hankula bayan da aka ganta tana yin fitsari a cikin miyar abincin da take sayarwa.
Wani karin abin mamaki shine itace da kanta ta dauki bidiyo yayin da take fitsarin.
Da yawa dai sun alakanta lamarin da sihiri dan neman kasuwa
Kalli bidiyon anan
Wannan sojan Najeriya ne yayin da yake koyon sakkowa daga jirgin sama ta hanyar amfani da Lema da ake cewa Parachute ya ji ciwo a fuskarsa.
Bidiyon lamarin ya dauki hankula inda akai ta masa jaje:
Kalli bidiyon anan
Shugaban kungiyar Kwadago ta NLC, Joe Ajero ya koka da cewa, mafi yawanci gwamnonin Najeriya kan bar jihohinsu su je Abuja su tare.
Yace hakan na faruwane a yayin mutanen jihohin wadannan gwamnonin ke fama da wahalar rayuwa.
Ya bayyana hakane a wajan taron karawa juna sani da ya faru a Lokaja jihar Kogi.
Ajaero ya bayyana cewa, sun ziyarci yankuna 5 na Najeriya amma mafi yawanci duk sun iske gwamnonin basa nan sun tafi Abuja.
An yi taron na NLC ne a Lokoja dan ma'aikatan jihar su bayyana matsalolinsu dan a kaiwa Gwamnan jihar.