Tuesday, March 17
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Na yi nadamar yiwa Tinubu yakin neman zabe, Jama’a ku yafe min kan jawo hankalinku da na yi kuka zabeshi>>Dan Balki Kwamanda

Na yi nadamar yiwa Tinubu yakin neman zabe, Jama’a ku yafe min kan jawo hankalinku da na yi kuka zabeshi>>Dan Balki Kwamanda

Duk Labarai
Dan siyasa a jiar Kano, Dan Balki Kwamanda ya bayyana nadama kan jawo hankalin mutane da yayi suka zabi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaban kasa. Yace yayi nadamar yakin neman zaben da yawa Tinubu. Yace tunda yake a rayuwarsa bai taba yin abinda yayi nadamarsa sosai ba kamar yiwa Tinubu yakin neman zabe. Yace dalili kuwa shine alkawuran da Bola Ahmad Tinubu ya dauka be cika ba kuma mutane na cikin matsananciyar wahala. Ya bayyana hakane a watan hira da gidan Jaridar Daily Trust suka yi dashi inda yace yana neman yafiyar wadanda ya yaudara.
Bìndìgù Sama da Dubu uku sun bace a hannun ‘yansandan Najeriya

Bìndìgù Sama da Dubu uku sun bace a hannun ‘yansandan Najeriya

Duk Labarai
Majalisar tarayya ta tuhumi shugaban 'yansandan Najeriya, (IGP),  Kayode Egbetokun bisa bacewar Bindigu 3,907 a hannun 'yansandan. Hakanan an masa tambayoyi game da aikata ba daidai ba da kudi a shekarar 2019. Shugaban 'yansandan da farko ya baiwa majalisar hakuri kan rashin amsa gayyatar da suka masa. Sannan ya wakilta mataimakinsa, AIG Suleiman Abdul ya wa 'yan majalisar jawabi kan tambayoyin batan kudaden da suke masa. Saida ya kasa bayar da gamsashshiyar amsa game da bacewar Bindigun inda suka nemi a shiga tattaunawar sirri a kori 'yan jarida daga dakin taron. Saidai 'yan majalisar sun ki amincewa da wannan kira inda suka ce shugaban 'yansandan ya kkma ya nemo amsar tambayoyin da suka masa.
Kalli Hotuna: Ana zargin Gwamnan Najeriya da dirkawa wata ‘yar Fim ciki

Kalli Hotuna: Ana zargin Gwamnan Najeriya da dirkawa wata ‘yar Fim ciki

Duk Labarai
Juna-biyun da na ke ɗauke da shi ba shi da alaƙa da wani gwamna - Jaruma Nengi Nengi Hampson, tsohuwar jaruma a shirin fim na gasar Big Brother Naija (BBNaija), ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sadarwa cewa tana dauke da juna biyu da wani gwamna a Najeriya ya yi mata. Jaridar TheCable ta rawaito cewa rahotannin farko sun yi ikirarin cewa jarumar mai shekara 27 ta haifi jariri ga wani gwamna mai shekara 65 kuma har ta zama matarsa ta biyar. A wani rubutu da ta wallafa kwanan nan a shafin X, Nengi ta bayyana takaicinta game da wannan jita-jita, tana mai cewa da ta sani ma da ta kau da kai daga jita-jitar. Sai dai ta ce dole ta yi magana saboda abin ya shafi mutanen da ta ke girmamawa sosai. Jarumar ta jaddada cewa ba za ta bari wannan jita-jita ta bata rayuwarta ko t...
Matsin Tattalin Arziki yayi yawa, ‘Yan Najeriya ba zasu iya biya ba>>Majalisar Tarayya tacewa Ministan sadarwa maza a dakatar da karin kudin kiran waya da ake shirin yi

Matsin Tattalin Arziki yayi yawa, ‘Yan Najeriya ba zasu iya biya ba>>Majalisar Tarayya tacewa Ministan sadarwa maza a dakatar da karin kudin kiran waya da ake shirin yi

Duk Labarai
Biyo bayan karin kudin kiran waya dana data da kamfanonin sadarwa suka yi, majalisar tarayya ta yunkuro dan dakatar da karin. Hukumar sadarwa ta kasa, NCC tuni ta amincewa kamfanonin sadarwar su kara kaso 50 cikin 100 na kudin da suke caji. Saidai kungiyoyin fafutuka da suka hada dana Kwadago, NLC da TUC sun ce basu amince da wannan kari ba. 'Yan majalisar ta wakilai a ranar Talata sun baiwa ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani umarnin ya dakatar da kari kudin kiran wayar inda suka ce 'yan Najeriya ba zasu iya biya ba musamman a wannan yanayi na matsin tattalin arziki. Sai ranar Litinin me zuwa ne ya kamata a fara yin karin kudin kiran dana data, amma MTN a matsayin kamfanin sadarwa mafi girma a Najeriya Tun a wannan satin sun fara kara kudin kira. A wata hira da ja...
Mafi yawancin Gwamnoni na barin jihohinsu ne su je Abuja su tare>>Inji NLC

Mafi yawancin Gwamnoni na barin jihohinsu ne su je Abuja su tare>>Inji NLC

Duk Labarai
Shugaban kungiyar Kwadago ta NLC, Joe Ajero ya koka da cewa, mafi yawanci gwamnonin Najeriya kan bar jihohinsu su je Abuja su tare. Yace hakan na faruwane a yayin mutanen jihohin wadannan gwamnonin ke fama da wahalar rayuwa. Ya bayyana hakane a wajan taron karawa juna sani da ya faru a Lokaja jihar Kogi. Ajaero ya bayyana cewa, sun ziyarci yankuna 5 na Najeriya amma mafi yawanci duk sun iske gwamnonin basa nan sun tafi Abuja. An yi taron na NLC ne a Lokoja dan ma'aikatan jihar su bayyana matsalolinsu dan a kaiwa Gwamnan jihar.