Friday, February 13
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon abin Kunyar da ya faru da gwamnan jihar Adamawa, wanda har sai da jami’in tsaronsa ya fashe da dariya

Kalli Bidiyon abin Kunyar da ya faru da gwamnan jihar Adamawa, wanda har sai da jami’in tsaronsa ya fashe da dariya

Duk Labarai
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya je garin Ganye mahaifar Atiku Abubakar inda yake tallar jam'iyyar PDP. Saidai a wajan yana jawabi ana masa ehon bamayi. Daga baya abin ya bashi haushi ya mayar da martani me zafi. A karshe dai da ya ga jawabin nasa ba zai yiyu ba, sai yace DJ ya saka mai kida, inda ya dan taka rawa, ya kama gabansa, ya fice daga wajan taron. https://twitter.com/i/status/2016237773657649323
Kalli Bidiyon da Duminsa: Shugaban kasa, ji abinda ya faru da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bayan da yayi Tuntube ya fadi a kasar Turkiyya

Kalli Bidiyon da Duminsa: Shugaban kasa, ji abinda ya faru da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bayan da yayi Tuntube ya fadi a kasar Turkiyya

Duk Labarai
Biyo bayan Tuntuben da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi ya fadi a kasar Turkiyya, yayin da yake tafiya shi da shugaban kasar Turkiyyan Recep Erdogan. Fadar shugaban kasa ta fitar da sanarwar cewa, shugaba Tinubu yana cikin koshin Lafiya. Sanarwar wadda ta fito daga bakin me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya bayyana cewa, yanayin yanda aka shimfida kafet din da shugaba Tinubu ke tafiya akai ne bai shimfidu da kyau ba shiyasa yayi Tuntuben. Sanarwar tace shugaba Tinubu bai ji ciwo a faduwar da yayi ba, kuma yanzu haka ya ci gaba da ziyarar aikin da yake a kasar ta Turkiyya. https://twitter.com/i/status/2016166532305273212
Kalli Bidiyon da Duminsa: Yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi Tuntube ya fadi kasa a yayin da yake gaisawa da shugaban kasar Turkiyya

Kalli Bidiyon da Duminsa: Yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi Tuntube ya fadi kasa a yayin da yake gaisawa da shugaban kasar Turkiyya

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi Tuntube ya fadi kasa a kasar Turkiyya yayin da yake tafiya shida shugaban kasar Turkiyyan Recep Erdogan. Shugaba Tinubu na ziyarar aiki ne a kasar ta Turkiyya yayin da lamarin ya faru. Ana daukar lamarin kai tsaye, saidai shugaban na faduwa 'yan Jarida suka yi sauri suka dauke kyamarar daga kansa. https://twitter.com/i/status/2016164862041199036
Da Duminsa:An yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin Mùlkì>>Inji Hukumar sojojin Najeriya

Da Duminsa:An yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin Mùlkì>>Inji Hukumar sojojin Najeriya

Duk Labarai
Hukumar sojojin Najeriya ta tabbatar da cewa an yi yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, Jhuyin Mùlkì. Hakan ya fito ne daga bakin daraktan yada labarai na hukumar ta sojojin Najeriya, AFN Samaila Uba. Ya bayyana cewa an kamma Bincike kuma an tabbatar da cewa sojojin da ake zargi sun yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki ne. Yace dan haka an mikawa hukumomin soji da suka dace lamarin dan a dauki matakin da ya dace,. Sanarwar ta ranar Litinin tace Nan gaba kadan za'a gabatar da sojojin a gaban kotun sojoji dan hukuntasu. A watan October da ya gabata ne dai aka soke faretin ranar 'yanci da aka saba yi, wanda kafafen yada labarai suka ce yunkurin Juyin mulki ne yasa aka yi hakan. Saidai chukwu sojojin a wancan lokacin ta musanta hakan. Amma a sanarwar dat...
Kalli Bidiyon: Abinda Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yawa Ganduje bayan komawa jam’iyyar APC da ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon: Abinda Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yawa Ganduje bayan komawa jam’iyyar APC da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi abin yabo bayan komawarsa jam'iyyar APC. An ganshi ya raka Tsohon gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje zuwa cikin motarsa bayan kammala bikin komawarsa jam'iyyar APC. Da yawa sun bayyana hakan da cewa alamace ta dattako da girmama mutane. https://twitter.com/i/status/2015858819549610426
Kalli Bidiyo Da Duminsa: Kwa Kwankwaso ya bayyana abinda zai faru a 2027 bayan komawar Abba jam’iyyar NNPP

Kalli Bidiyo Da Duminsa: Kwa Kwankwaso ya bayyana abinda zai faru a 2027 bayan komawar Abba jam’iyyar NNPP

Duk Labarai
Komawar Gwamna Abba Kabir Yusuf jam'iyyar APC ta zo da dumamar yanayin siyasa a jihar Kano. Shugaban tafiyar Kwankwasiyya, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa a baya ba'a yo siyasa ba, a yanzu ne za'a yi siyasa a 2027. Wannan kalamai na Kwankwaso na zuwane bayan da Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya koma jam'iyyar APC daga NNPP. https://twitter.com/i/status/2015547430893207978
Kalli Bidiyon: Duk wani dake neman takarar Gwamna a 2027 a APC ya hakura, Abba zai yi takara babu hamayya>>Inji Ganduje

Kalli Bidiyon: Duk wani dake neman takarar Gwamna a 2027 a APC ya hakura, Abba zai yi takara babu hamayya>>Inji Ganduje

Duk Labarai
tsohon Gwamnan Kano kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa duka 'yan takara na 2023 da wanda ke son yin takara a 2027 sun hakura sun barwa Abba. Yace Abba Kabir Yusuf zai yi takara a 2027 ba tare da hamayya ba a jam'iyyar APC. https://twitter.com/i/status/2015855764049478122 Ya bayyana hakane a wajan bikin komawar Gwamna Abba Kabir Yusuf jam'iyyar APC.
Kalli Bidiyon: Dan uwan Kwankwaso na jini, Yahya Musa Kwankwaso ya watsar da NNPP inda yabi Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa APC

Kalli Bidiyon: Dan uwan Kwankwaso na jini, Yahya Musa Kwankwaso ya watsar da NNPP inda yabi Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa APC

Duk Labarai
Dan uwan Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, Yahya Musa Kwankwaso ya fice daga jam'iyyar NNPP. Shima dai ya bayyana goyon bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf inda ya bishi zuwa jam'iyyar APC. An ganshi suna kashewa da abokin Burminsa a wani Bidiyo da ya dauki bankula a kafafen sadarwa. https://twitter.com/i/status/2015797701930008877
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Yanda ma’aikatan Hukumar  kula da Abuja, FCTA suka Bi Wike da gudu yayin da yayi niyyar tserewa ta hanyar baya babu Jiniya a yayin da ma’aikatan ke Zàngà-zàngà

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Yanda ma’aikatan Hukumar kula da Abuja, FCTA suka Bi Wike da gudu yayin da yayi niyyar tserewa ta hanyar baya babu Jiniya a yayin da ma’aikatan ke Zàngà-zàngà

Duk Labarai
An ga ma'aikatan hukumar FCTA dake kula da Abuja sun bi Ministan Abujan, Nyesom Wike da gudu yayin da yayi yunkurin tserewa daga ma'aikatar ta hanyar baya. An ji suna ce masa, Ole, watau Bàràwò. Ma'aikatan dai na zanga-zangar ne dan neman a biyasu hakkokinsu. https://twitter.com/i/status/2015772997563387912