Friday, May 15
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Mun fi ‘yan Najeriya iya turanci, idan ‘yan Najeriya suka yi Turanci sai ka rasa me suke cewa>>Inji Shugaban kasar Kenya, William Ruto

Kalli Bidiyon: Mun fi ‘yan Najeriya iya turanci, idan ‘yan Najeriya suka yi Turanci sai ka rasa me suke cewa>>Inji Shugaban kasar Kenya, William Ruto

Duk Labarai
Shugaban kasar Kenya, William Ruto ya bayyana cewa, 'Yan Najeriya basu iya turanci ba idan suka yi turanci ba'a gane ahinda suke cewa. Yace amma su 'yan Kenya sun fi 'yan Najeriya iya turanci da ilimi. Yayi wannan maganane a matsayin martani bayan da shugaba Tinubu ya yi magana akan tattalin arzikin Kenya wanda yace Na Najeriya ya fishi. https://twitter.com/i/status/2047380466982883737
Kalli Bidiyon yanda matan Kano suka cire dan kamfensu suke Nunawa Duniya suna cewa wai Dankamfai din Tsula

Kalli Bidiyon yanda matan Kano suka cire dan kamfensu suke Nunawa Duniya suna cewa wai Dankamfai din Tsula

Duk Labarai
SIYASAR KANO: An hangi wasu mata magoya bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf suna daga Dan Kamfai na mata suna kiran Dan Kamfen Tsula. Matan da suka bayyana kansu a matsayin yan kungiyar Gida Gida Tiktokers, an jiyo su suna ihu suna kiran Dan Kamfen Tsula. Jama'a da dama A Kano sun nuna alhinin su kan wannan abu a cewar su wannan ba dabiar Kanawa bace, Videon yana comment Meye Raayin ku ? https://twitter.com/i/status/2047331559926087905
Kalli Bidiyon: Na koma gidan tsohon Mijina dana kasa hakuri nace sai ya sakeni, na iske ya auri wata matar wallahi ba zan boye ba na ji kishi da kewa sosai>>Inji Wannan bazawarar

Kalli Bidiyon: Na koma gidan tsohon Mijina dana kasa hakuri nace sai ya sakeni, na iske ya auri wata matar wallahi ba zan boye ba na ji kishi da kewa sosai>>Inji Wannan bazawarar

Duk Labarai
Wannan wata Bazawara ce data daui hankula a kafafen sadarwa bayan da tace ta koma gidan tsohon Mijinta inda ta iske ya auri wata mata. Tace ba zata boye ba, ta ji ba dadi kuma ta yi dana sanin rabuwa dashi. Tace da ta yi hakuri da yanzu itace a gidan. https://www.tiktok.com/@dumdum8109/video/7631477271915744519?_r=1&_t=ZS-95mfrSGn21I
Kalli Bidiyon: Budurwata ta yaudareni na aikata abinda bai dace ba da ita, saidai ina tsaka da aikatawa tace wai in karanta Fatiha>>Inji Wannan Dattijon

Kalli Bidiyon: Budurwata ta yaudareni na aikata abinda bai dace ba da ita, saidai ina tsaka da aikatawa tace wai in karanta Fatiha>>Inji Wannan Dattijon

Duk Labarai
Wannan wani Dattijo ne da ya bayyana a kafafen sada zumunta yana ikirarin cewa, Budurwarsa ta yaudareshi ya aikata abinda bai dace ba da ita. Yace yana tsaka da aikatawa sai tace wai ya karanta Fatiha. Yace anan yaki amincewa, kuma sanadiyyar Rabuwarsu kenan. https://www.tiktok.com/@auwalsuraj4549/video/7631688716901207317?_r=1&_t=ZS-95mYbqFLvLF
Kalli Bidiyon: Shugaban Daliban Najeriya ya jinjinawa shugaba Tinubu saboda a cewarsa dalibai basu taba samun Gwamnatin data kula dasu irin ta Tinubu ba

Kalli Bidiyon: Shugaban Daliban Najeriya ya jinjinawa shugaba Tinubu saboda a cewarsa dalibai basu taba samun Gwamnatin data kula dasu irin ta Tinubu ba

Duk Labarai
Shugaban daliban Najeriya Olushola Oladoja ya jinjinawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda a cewarsa, dalibai basu taba samun kulawa irin ta lokacin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba. Ya bayyana hakane a wata hira da yayi da manema labarai. Yace a lokacin shugaba Tinubu ne aka baiwa dalibai bashi dan su yi karatu sannan a lokacin Tinubu ne aka nada ministan matasa wanda da gaske matashinne https://twitter.com/i/status/2047232829352808550
Kalli Bidiyon: Yawan mutanen da suka je tarar Ministan wutar Lantarki ya baiwa mutane mamaki

Kalli Bidiyon: Yawan mutanen da suka je tarar Ministan wutar Lantarki ya baiwa mutane mamaki

Duk Labarai
Mutane da yawa ne suka je tarar Ministan wutar Lantarki, Adeboye Adelabu filin Jirgin sama na jihar Oyo bayan da ya sauka daga mukaminsa. Adeboye Adelabu ya sauka daga mukaminsa ne dan tsayawa takarar Gwamnan jihar Oyo. Saidai lamarin ya dauki hankula inda da yawa ke tambayar shin wanda suka je tararshi suna samun wuta kuwa? https://twitter.com/i/status/2047271734873592276
Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikawa majalisa bukatar ciwo bashin Dala Miliyan $516

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikawa majalisa bukatar ciwo bashin Dala Miliyan $516

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aikawa majalisar Dattijai da bukatar ciwo bashin dala Miliyan $516. Shugaban ya aika da bukatar ne a yau, Alhamis inda yace za'a yi aikin gina titin Sokoto-Badagry ne da kudaden. Kakakin majalisar, Godswill Akpabio ya bayyana cewa akwai bukatar a gaggauta amincewa da karbo bashin. Ya bayyana cewa, ya baiwa kwamitin kula da bashi na majalisar umarnin su kammala amincewa da bashin cikin sati daya.
Da Duminsa: Da gaskene mun fara karbar Harajin saka Solar a gidaje>>Gwamnati ta tabbatar

Da Duminsa: Da gaskene mun fara karbar Harajin saka Solar a gidaje>>Gwamnati ta tabbatar

Duk Labarai
A jiyane Bidiyo ya yadu sosai bayan da aka ga wani mutum a Legas yana ta fada da jami'an Gwamnati da suka je karbar harajin saka solar da yayi a gidansa. Mutumin dai yace ba zai biya ba. Inda mutane da yawa suka goyi bayansa. Bidiyon ya jawo cece-kuce sosai inda mutane sukai ta bayyana cewa ko da sune ba zasu yadda ba. A martanin Gwamnatin jihar Legas ta bakin me magana da yawun Gwamnan jihar, Wale Ajetunmobi ya bayyana cewa da gaskene akwai harajin sala sola a gida. Yace amma ba ga duka mutanen jihar Legas ba, ana karbar Harajinne kawai a hannun wadanda suke a gidajen Gwamnatin jihar.