Thursday, January 22
Shadow

Duk Labarai

DSS sun hanani ganawa da iyali na da Lauyana>>Inji Abubakar Malami

DSS sun hanani ganawa da iyali na da Lauyana>>Inji Abubakar Malami

Duk Labarai
Tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami ya koka da cewa, Hukumar DSS sun ki barinshi ya gana da iyalansa da lauyansa. Ya bayyana hakane ta bakin lauyansa, Muhammad Doka inda yace tunda DSS suka sake kama Malami bayan an bayar da belinsa, sun hanashi ganawa da kowa. Yace zargin gano Makamai a gidan malami da kuma cewa, wai ana zarginshi da hannu a ayyukan ta'addancy duk karyane. DSS dai sun sake kama malami, jim kadan bayan da aka sakeshi daga gidan Gyara hali na Kuje.
Kalli Bidiyon abinda ya faru tsakanin malamin Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II a jami’ar Northwest University, Kano da sarkin

Kalli Bidiyon abinda ya faru tsakanin malamin Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II a jami’ar Northwest University, Kano da sarkin

Duk Labarai
Bayan kammala karatu, Malamin da ya kotar da Me martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II a jami'ar Northwest University, Kano yaki yadda ya baiwa sarkin Hannu su gaisa. Sarki Sanusi ya tashi inda zai fita daga ajin, ya mikawa Malamin hannu su gaisa, saidai malamin yaki amincewa ya baiwa Sarkin hannu. https://twitter.com/i/status/2013942641537233364 Lamarin ya dauki hankula.
Da Duminsa: An bukaci a saka Rev. Ezekiel Dachomo a Addu’a, Ciwon Hantane ya kamashi shiyasa aka ji shi  shiru ya daina magana akan Mhuzghunawar da akewa Kiristoci a Najeriya

Da Duminsa: An bukaci a saka Rev. Ezekiel Dachomo a Addu’a, Ciwon Hantane ya kamashi shiyasa aka ji shi shiru ya daina magana akan Mhuzghunawar da akewa Kiristoci a Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Filato sun bayyana cewa shahararren Faston nan me magana akan zargin Mhuzghunawa Kiristoci a Najeriya, watau Rev. Ezekiel Dachomo ya kamu da cutar Hanta Wani dan jarida daga jihar me suna, Masara Kim Usman ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ta shafinsa na sada zumunta. Yace Kiristoci su saka Rev. Ezekiel Dachomo a Addu'ar Allah ya bashi lafiya. Dama dai a baya ya taba kamuwa da cutar inda matarsa ta bashi kyautar daya aka dasa masa, saidai yanzu ciwon ya sake dawowa.
Na bayar da gidana kyauta ga Gwamnatin jihar Kano a Gina Islamiya dan amfanin Al’umma>>Inji Malam Bashir Haruna Dorayi Chiranchi

Na bayar da gidana kyauta ga Gwamnatin jihar Kano a Gina Islamiya dan amfanin Al’umma>>Inji Malam Bashir Haruna Dorayi Chiranchi

Duk Labarai
Malam Bashir Haruna Dorayi Chiranchi da akawa iyalansa aika-aika a jihar Kano, Ya bayyana cewa, ya bayar da gidansa kyauta ga Gwamnatin jihar Kano dan a gina Islamiya. Ya bayyana hakane yayin da Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya je masa ziyarar gaisuwa. A wajan Gwamnan Kano yace Gwamnatin jihar Kano ta dauki nauyin rayuwarsa gaba daya.
Ji manya-manyan Alkawura 7 da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yawa Malam Haruna da akawa Iyalansa Aika-aika

Ji manya-manyan Alkawura 7 da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yawa Malam Haruna da akawa Iyalansa Aika-aika

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya jewa Malam Haruna na Chiranchi Dirayi da akawa iyalansa aika-aika gaisuwa. A yayin ziyarar gwamnan ya bayyana cewa Gwamnatin jihar Kano ta dauki nauyin rayuwar Malam Haruna Chiranci Dorayi gaba daya. Sannan an biya masa hajji da Umara, sannan za'a dauki nauyin yi masa aure idan ya samu wadda yake so. Sannan an bashi kyautar gida. Sanna Gwamnan ya sha Alwashin zartas da hukuncin da kotu ta yankewa wanda ake zargi a lamarin. Hakanan yace duk ma wasu da aka samu da hannu a irin wannan abu zai saka hannu a zartas musu da hukunci.
Kalli Bidiyon: A wajan taron Mailidin Katsina, naji wata Murya daga sama tace Na gafarta muku zunubanku>>Inji Alhaji Anisee

Kalli Bidiyon: A wajan taron Mailidin Katsina, naji wata Murya daga sama tace Na gafarta muku zunubanku>>Inji Alhaji Anisee

Duk Labarai
Shahararren dan Darika, Alhaji Anisee ya bayyana cewa, a wajan taron Katsina, ya ji wata murya daga sama tace masa An gafarta muku zunubanku. Yace dan haka duk wanda ya halarci wajan wannan Maulidi an yafe masa zunubansa. Ya ya bayyana hakane a cikin wani Bidiyo daya saki. https://www.tiktok.com/@alhajianisee1/video/7597432798240066836?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7597432798240066836&source=h5_m&timestamp=1768995372&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7568740291232040721&a...