Friday, December 5
Shadow

Duk Labarai

Bai kamata ace an nada Tsohon Shugaban INEC da ya sauka mukamin Jadaka ba, ni dai da nine shugaban kasa ba zan yi haka ba>>Inji Atiku Abubakar

Bai kamata ace an nada Tsohon Shugaban INEC da ya sauka mukamin Jadaka ba, ni dai da nine shugaban kasa ba zan yi haka ba>>Inji Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa bai kamata shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nada tsohon shugaban INEC jakada ba Yace hakan zai sa wasu su yi zargin cewa watakila ya taimakawa Tinubun da magudin zabene shine yake saka masa da mukamin Jakada Yace shi dai da shine shugaban kasa ba zai aikata hakan ba. Farfesa Mahmoud Yakubu tsohon shugaban hukumar zabe me zaman kanta INEC na daga cikin sunayen da shugaba Tinubu yake son baiwa mukamin jakadanci.
Kwanannan cikin gaggawa zaku ga sakamako me kyau>>Sabon Ministan tsaro, Janar Christopher Musa ya bayar da tabbaci

Kwanannan cikin gaggawa zaku ga sakamako me kyau>>Sabon Ministan tsaro, Janar Christopher Musa ya bayar da tabbaci

Duk Labarai
Sabon Ministan tsaro Janar Christopher Musa ya bayar da tabbacin cewa kwanannan cikin gaggawa za'a ga sakamako me kyau. Ya bayyana hakane a ganawa da manema labarai a Abuja bayan rantsar dashi a matsayin Ministan tsaro. Yace zai hada kai da dukkan wadanda suka kamata dan tabbatar da an samar da tsaro a Najeriya. https://twitter.com/NigAffairs/status/1996641245184348248?t=qaH47c5nZFVeSavT_o7s9w&s=19
Majalisar Dattijai zata yi dokar saka ido da kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu

Majalisar Dattijai zata yi dokar saka ido da kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu

Duk Labarai
Majalisar Dattijai na shirin yin sabuwar doka dan kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu. Dayake magana akan muhimmancin wannan doka, Sanata Adams Oshiomhole ya bayyana cewa, an taba sace masa kudi a asusun bankinsa kuma inda aka tura kudaden Opay ne da Moniepoint. Yace kuma basu da rassa a zahiri da mutum zai ce ya shigar da korafi. dan haka akwai bukatar a yi dokar da zata saka ido a ayyukan da suke. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1996645682640265295?t=qvwu4FHmYIHsrWjka2UMqQ&s=19 Ita kuma a nata bangaren, Sanata Natasha Akpoti ta bayyana cewa wai idan aka yi wannan doka zata taimakawa matasan Najeriya dake samun kudi ta yanar gizo su rika samu daidai da takwarorinsu na kasashen waje. https://twitter.com/ChuksEricE/status/19...
Shugaba Tinubu ya aika da sunan Dambazau da karin wasu mutane da zai baiwa Mukamin jakadanci zuwa majalisa

Shugaba Tinubu ya aika da sunan Dambazau da karin wasu mutane da zai baiwa Mukamin jakadanci zuwa majalisa

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura ƙarin sunan mutum 4 ɗoriya a kan waɗanda aka fitar a baya zuwa ga majalisar dattawa domin a tantance su a matsayin jakadun ƙasar da za a tura ƙasashen waje. Mutum huɗu da Tinubu ya tura su ne: Ibok-Ete Ekwe Ibas, tsohon shugaban riƙon-ƙwarya na jihar Rivers da tsohon ministan harkokin cikin gida Abdulrahman Dambazau. Sauran kuma su ne Sanata Ita Enang da tsohon gwamnan jihar Imo Chioma Ohakim. Yanzu dai jimilla shugaban ya tura sunan mutum 65 ke nan da yake buƙatar majalisar ta tantance, inda ake sa ran da zarar an tantance su, zai sanar da ƙasashen da za a tura su.
Kalli Bidiyon ‘yan Arewa daban-daban da suka je cirani jihohin Inyamurai da yarbawa aka kamasu aka ce Tshàgyèràn Dhàjì ne

Kalli Bidiyon ‘yan Arewa daban-daban da suka je cirani jihohin Inyamurai da yarbawa aka kamasu aka ce Tshàgyèràn Dhàjì ne

Duk Labarai
A 'yan kwanakinan kamen 'yan Arewa Hausawa da fulani na karuwa a jihohin Yarbaw da Inyamurai. Ana kama wadanda yawanci 'yan ciranine ana makala musu sunan garkuwa da mutane. Saidai da yawan 'yan kudun dake shahi akan wadanda ake kamawan na bayyana cewa ya kamata a tsananta bincike dan wadanda ake kamawa din basa kama da masu garkuwa da mutane. Lamarin dai ya jawo zazzafar muhawara a kafafen sadarwa. https://twitter.com/Gen_Buhar/status/1996249984149196897?t=4SM6pyVkOcIeSZZfRnaKTg&s=19 https://twitter.com/MFaarees_/status/1996271281671385142?t=ocMhMwwzvF9p541Rj0VJFQ&s=19 https://twitter.com/DrOzitababy/status/1996259267578327213?t=rY8c5tzGEQyd3XIwn_SJJQ&s=19
Peter Obi yayi Allah wadai da rabon motocin yakin neman zaben Tinubu na 2027 yayin da Talakawa ke cikin matsi

Peter Obi yayi Allah wadai da rabon motocin yakin neman zaben Tinubu na 2027 yayin da Talakawa ke cikin matsi

Duk Labarai
Ba Daidai Ba Ne Raba Motocin Kamfen Yayin Da Talakawa Ke Fama Da Yunwa, Obi Ya Soki Gwamnatin Tinubu Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya soki raba motocin alfarma ga wakilan ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors domin shirye-shiryen zaɓen 2027, lamarin da ya danganta ga gwamnatin Tinubu. A sanarwar da ya fitar, Obi ya ce wannan aiki tsananin rashin tausayi ne da cin amana, musamman a lokacin da ƴan ƙasa ke fama da yunwa, rashin aikin yi da matsalolin tsaro. Ya jaddada cewa maimakon kashe kuɗaɗen jama’a kan motocin kamfen, gwamnati ta mayar da hankali kan samar da abinci, kiwon lafiya, ayyukan yi da inganta tsaro.
Kalli Bidiyon: Malamin Addinin Islama Inyamuri ya bayyana cewa ba za iya Qìrgà sau nawa ‘yan Qabilarsa Inyamurai suka Jèfèshì da duwatsu ba saboda yana jawo hankalinsu zuwa a Musulunci

Kalli Bidiyon: Malamin Addinin Islama Inyamuri ya bayyana cewa ba za iya Qìrgà sau nawa ‘yan Qabilarsa Inyamurai suka Jèfèshì da duwatsu ba saboda yana jawo hankalinsu zuwa a Musulunci

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama Inyamuri me suna Sheikh mohammed Chukwuemeka ya bayyana cewa ba zai iya Qirga sau nawa aka jefeshi ba dan yana jawo hankalin Inyamurai 'yan wansa su Musulunta. Yace amma hakan bata sa ya daina wa'azin ba kuma ba zai daina ba Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a BBC. https://twitter.com/7signxx/status/1996439541524451640?t=CB1zsBwOcHDGIi_VG21Gig&s=19