Friday, December 19
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyo: Na bayar da kaina Kyauta ba sai ta biya kudi ba, Ummi Nuhu ta daukeni ‘yar Aiki>>Inji Murja Kunya

Kalli Bidiyo: Na bayar da kaina Kyauta ba sai ta biya kudi ba, Ummi Nuhu ta daukeni ‘yar Aiki>>Inji Murja Kunya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tauraruwar Tiktok, Murja Kunya ta bayyana cewa, ta bayar da kanta kyauta, Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Nuhu ta dauketa 'yar aikin gida. Ta bayyana hakane a shafinta na Tiktok inda ta ke nuna goyon bayanta ga Ummi Nuhu. https://www.tiktok.com/@murjakunya0/video/7533012273762209080?_t=ZS-8yTlHZ6H9qD&_r=1 Ummi Nuhu dai ta dauki hankula sosai bayan hirar da Hadiza Gabon ta yi da ita inda ta bayyana halin matsin rayuwar da take ciki.
Kalli Bidiyon yanda aka yiwa su Mansurah Isa Ba daidai ba a wajan taron siyasa hadda cire kaya a bainar Jama’a

Kalli Bidiyon yanda aka yiwa su Mansurah Isa Ba daidai ba a wajan taron siyasa hadda cire kaya a bainar Jama’a

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah ta bayyana yanda aka wulakantasu a wajan taron siyasa na Sanata Barau I Jibrin. Mansurah Isah a wani Bidiyo data wallafa a shafinta na sada zumunta ta bayar da labarin yanda aka gayyacesu wajan taron siyasar amma da suka je daya daga cikin jami'an tsaron yace fuskar daya daga cikinsu bata mai ba dan haka ya hanasu shiga. Tace saboda cin mutunci hadda tubewa wata kaya a bainar Jama'a. Mansurah ta nemi da sanata Barau I Jibrin ya kwato musu hakkinsu. Kalli Bidiyon anan A wani Bidiyo da ta sake wallafawa kuma, Mansurah Isah tace Barau Jibrin ya mata Alkawarin daukar mataki da kwato mata hakkinta ita da sauran abokan tafiyarta. Mansurah ta bayyana godiyarta da Farin ciki kan kulawar Sanatan. Kalli Dayan Bidiyon anan
Ki yi watsi da masu cewa wai laifin da kika yi a bayane yasa kika shiga rayuwar Wahala, Ba haka bane>>Babiana Ta karfafi Ummi Nuhu

Ki yi watsi da masu cewa wai laifin da kika yi a bayane yasa kika shiga rayuwar Wahala, Ba haka bane>>Babiana Ta karfafi Ummi Nuhu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tauraruwar Tiktok, Babiana ta bayyana shawararta ga tsohuwar jarumar fina-finan Hausa, Ummi Nuhu da ake cece-kuce akan rayuwarta. Babiana tace ba lallai wai irin rayuwar data aikata a bayane yasa ta shiga halin fata shiga ba. Tace wanda Allah ke so ne ma yake Jarabarsa da ya kara matsawa kusa dashi. Kalli Bidiyonta a kasa: https://www.tiktok.com/@queenofthenorth64/video/7532837479620087045?_t=ZS-8yT1P7iL2jh&_r=1
NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Duk Labarai
Babban kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya musanta raɗe-raɗin sayar da matatar mai ta birnin Fatakwal. Shugaban kamfanin Bashiru Ojulari ne ya bayyana haka a wani taron tuntuɓa da kamfanin ya shirya a shalkwatarsa da ke Abuja. Ojulari ya ce NNPCL ba shi da aniyar sayar da wata matata mallakinta, sai dai ma ƙoƙarin gyara su domin yin daidai da zamani. An fara raɗe-raɗin sayar da matatar ne bayan wata hira da shugaban kamfanin ya yi a taron OPEC a birnin Vienna na ƙasar Austria a farkon watannan. A lokacin Ojulari ya yi wata hira da jaridar Bloomberg, kan batun sayar da matatar inda ya ce “komai zai iya faruwa”. Tun daga wancan lokacin ne aka yi ta maganganu game da makomar matatar.
Gwamnatin Najeriya ta ce ta samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Aba

Gwamnatin Najeriya ta ce ta samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Aba

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta ce ta samu duka kuɗin gudanar da aikin gina layin dogo daga birnin Maiduguri na jihar Borno zuwa garin Aba na jihar Abiya. Ministan Sufuri Saidu Alkali ne ya bayana hakan a yau yayin wani taron bita da ake gudanarwa a Kaduna, kamar yadda wata sanarwa daga ofishinsa ta bayyana. "Layin dogon mai tsawon kilomita 1,443 zai ratsa jihohin Borno, da Yobe, da Gombe, da Bauchi, da Filato, da Kaduna, da Nasarawa, da Binuwai," in ji sanarwar da kakakin ministan Rabiu Ibrahim ya fitar. Sai dai sanarwar ba ta bayyana inda gwamnatin ta samo kudin ba. Akasarin manyan ayyuka masu tsada kamar wannan akan yi su ne ta hanyar bashi ko kuma lamuni. Ministan ya kuma bayyana cewa gwamnatin tarayya ta gyara layin dogo na dakon kaya tsakanin Legas zuwa Kano.
Za mu kammala titin jirgin Kaduna zuwa Kano a 2026, in ji gwamnatin tarayya

Za mu kammala titin jirgin Kaduna zuwa Kano a 2026, in ji gwamnatin tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta ce za a kammala aikin titin jirgin ƙasa daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa, kamar yadda Ministan Sufuri Sa'idu Ahmed Alkali ya bayyana. Da yake magana yayin wani taron tuntuɓa tsakanin 'yan ƙasa da gwamnati da ke gudana a jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar, ministan ya ce lokacin da Shugaba Tinubu ya hau mulki kashi 15 cikin 10 na aikin kawai aka kammala. "Amma zuwa yanzu an kammala kashi 53 cikin 100," in ji shi cikin wata sanarwa da ma'aikatar yaɗa labarai ta fitar a yau Laraba. A 2024 gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ta samu rancen kuɗin da za ta kammala aikin daga wani bankin kasuwanci na ƙasar China, abin da ministan ya jaddada a yau din.
Mu ‘yan Arewa bamu yi dana sanin Zaben Tinubu ba>>Inji Ministan tsare-tsare, Atiku Bagudu

Mu ‘yan Arewa bamu yi dana sanin Zaben Tinubu ba>>Inji Ministan tsare-tsare, Atiku Bagudu

Duk Labarai
Ministan tsare-tsare Atiku Bagudu ya bayyana cewa, 'yan Arewa basu yi dana sanin zaben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba. Ya bayyana hakane a wajan taron Arewa House da aka yi na kwanaki biyu tsakanin shuwagabanni da wanda akw Mulka a jihar Kaduna. Ministan yace a lokacin kamin Tinubu ya hau mulki ana ta ciwo bashi ana siyo man fetur daga kasashen waje sannan ana biyan kudin tallafi. Yace amma da Tinubu yazo ya dakatar da duka wannan sannan ya cire tallafin man fetur dana dala. Yace bayan cire tallafin man fetur jihohi sun samu karin kudaden shiga. Dan haka yayi kira ga mutanen Arewa da su daina sauraren masu kokarin hure musu kunne kan cewa wai shugaba Tinubu ya ware Arewa baya mata komai a gwamnatinsa. Yace Gwamnatin Tinubu na tafiya tare da 'yan kasa wajan gudanar da...
Kalli Bidiyo: Anya Rarara ba Asiri yawa A’isha Humaira ta yadda ta aureshi ba?>>Inji Ummi Bamaiyi

Kalli Bidiyo: Anya Rarara ba Asiri yawa A’isha Humaira ta yadda ta aureshi ba?>>Inji Ummi Bamaiyi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wata 'yar Tiktok me suna Ummi Bamaiyi ta bayyana ra'ayinta akan Sabbin hotunan Dauda Kahutu Rarara da matarsa, A'isha Humaira. Ta bayyana cewa, ita a tunaninta akwai yiyuwar Rarara Asiri yawa A'isha Humaira ta yadda ta aureshi. Saidai bayan ta gama sukar tata, ta yi fatan itama Rarara ya aureta. https://www.tiktok.com/@ummimamabamaiyisa/video/7532645228377885958?_t=ZS-8ySlDoE1Vbt&_r=1 Hotunan ma'auratan dai sun dauki hankula inda akai ta yaba musu.
Kuma Dai: Kalli Bidiyon yanda Mamakon ruwan sama ya haifar da anbaliyya a Maiduguri

Kuma Dai: Kalli Bidiyon yanda Mamakon ruwan sama ya haifar da anbaliyya a Maiduguri

Duk Labarai
Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno sun tsere daga gidanjensu bayan wata mummunar ambaliya ta auka wa wasu sassan birnin sakamakon ruwan sama mai ƙarfin gaske. Rahotonni daga birnin sun ce lamarin ya shafi unguwannin Damboa road da Moduganari Ngomari da Bulunkutu Abuja da sauransu. An dai wayi gari da mamakon ruwan sama a faɗin birnin, lamarin da ya haifar da ambaliyar. A shekarar da ta gabata ne aka samu wata mummunar ambaliya da ta raba fiye da mutum miliyan guda da muhallansu a birnin na Maiduguri. https://www.tiktok.com/@._cbn/video/7532832958030351672?_t=ZS-8yShc7SinaK&_r=1
David Mark: ADC ba za ta lamunci kakaba ƴan takara ko cin amanar jam’iyya ba

David Mark: ADC ba za ta lamunci kakaba ƴan takara ko cin amanar jam’iyya ba

Duk Labarai
Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar ADC, David Mark, ya bayyana cewa jam’iyyar ba za ta lamunci kakaba ‘yan takara , cin amanar jam’iyya ko rashin da’a ba a karkashin jagorancinsa. A yayin taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) na jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, David Mark ya sha alwashin jagorantar ADC da gaskiya, adalci da dimokuradiyya. Ya jinjinawa tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu, bisa jajircewarsa da hidimar da ya yi. Mark ya bayyana cewa jam’iyyar ta ware kashi 35 cikin 100 na mukaman shugabanci ga mata, tare da kudurin bai wa matasa ‘yan kasa da shekara 40 mukamai. Ya kuma bayyana cewa sabon shugabancin jam'iyyar na kasa zai sake duba kundin tsarin mulki da manufofin jam’iyyar domin su dace da bukatun ‘yan kasa. Ya kara da cewa jam’iyyar za ta kafa kwamiti...