Friday, February 27
Shadow

Duk Labarai

Muna nan akan Bakanmu, kowa sai ya biya Haraji, ko ta hanyar halarar ya samu kuri ko bata ta hanyar halal ba, Qaruwai, Kwandastan Mota, dama kowace irin sana’a kake nan da 2026 sai ka fara biyan Haraji>>Inji Gwamnatin Tinubu

Muna nan akan Bakanmu, kowa sai ya biya Haraji, ko ta hanyar halarar ya samu kuri ko bata ta hanyar halal ba, Qaruwai, Kwandastan Mota, dama kowace irin sana’a kake nan da 2026 sai ka fara biyan Haraji>>Inji Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, tana nan akan bakanta na cewa, kowa sai ya biya haraji. Shugaban kwamitin Gyaran fasalin kudi na shugaban kasa, Taiwo Oyedele ne ya bayyana haka a wata ganawa da manema labarai. Yace a Duniya gaba daya haka tsarin yake, ko ta wace hanya ka samu kudi sai ka biya Haraji, yace idan ance wanda suka samu kudi ta hanyar Halal ne kadai zasu biya haraji, to sai wasu su koma samun kudi ta hanyar Haram dan su kaucewa biyan Harajin. Yace hukumar karbar Haraji ta kasar Amurka nada taken cewa ko sata kayi sai ka biya Haraji.
Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan na shirin komawa jam’iyyar ADC

Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan na shirin komawa jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan na shirin komawa jam'iyyar ADC. Wasu majiyoyi ne suka fadawa kafar Punchng hakan a asirce daga jam'iyyar ADC din saboda basu da ikon yin magana da yawun jam'iyyar. An jima dai ana rade-radin cewa, tsohon shugaban kasar zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 amma shi bai fito ya tabbatar da hakan a hukumance ba.
Allah ya kawo mu zamanin Wawaye da Jahilai kowa sai fadin abinda yaga dama akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yake>>Inji Sheikh Umar Sani Fage

Allah ya kawo mu zamanin Wawaye da Jahilai kowa sai fadin abinda yaga dama akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yake>>Inji Sheikh Umar Sani Fage

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Umar Sani Fagge ya yi raddi sosai akan masu yin kalamai da basu dace ba akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Malam yace idan aka samu mutum da laifi zai iya kaiwa a dauki hukuncin khisa akansa. https://www.tiktok.com/@mai.6013/video/7557485955301625095?_t=ZS-90I9Vj3gtdp&_r=1
Maganar Gaskiya, Malam Lawal Triumph duk da namune, sai mun fadi gaskiya, Yayi Kuskure kalaman da yayi kan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) kuma ya kamata a hukuntashi>>Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun

Maganar Gaskiya, Malam Lawal Triumph duk da namune, sai mun fadi gaskiya, Yayi Kuskure kalaman da yayi kan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) kuma ya kamata a hukuntashi>>Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun ya bayyana cewa duk da Malam Lawal Triumph yana bangarensu ne amma maganar gaskiya yayi kuskure. Malam ya bayyana cewa maganar Sheikh Lawal Triumph bata dace da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba amma kuma bata fitar dashi daga Musulunci ba. Ya kawo misalin irin hakan data faru a baya inda yace ladabtarwa ce ake wa irin wannan suka yi hakan. https://www.tiktok.com/@mai.6013/video/7557115827904990482?_t=ZS-90I63lDof5M&_r=1
Mu muka rika raka ‘yan siyasa da kudaden da suka sata suna kaisu kauyukansu suna boyewa amma gashi yanzu mun gama aiki an kasa biyanmu hakkokinmu>>Tsohon Dansandan Najeriya ya koka

Mu muka rika raka ‘yan siyasa da kudaden da suka sata suna kaisu kauyukansu suna boyewa amma gashi yanzu mun gama aiki an kasa biyanmu hakkokinmu>>Tsohon Dansandan Najeriya ya koka

Duk Labarai
Tsohon dansandan Najeriya me mukamin DSP ya koka game da yanda yace an kasa biyansu hakkokinsu bayan sun kwashs Shekaru 35 suna aiki. Yace a lokacin da suke aiki, sune suka rika raka 'yan siyasa da kudaden da suka sata zuwa kauyukansu suna boyewa, yace amma gashi sun gama aiki biyansu hakkokinsu ya gagara. Ya bayyana hakane a wajan zanga-zangar neman hakokinsu da suka fito. https://twitter.com/NigeriaStories/status/1974387956904571003?t=Z9OF0PHH9teHjvcwcOcFYg&s=19
Ni gadon Musulunci na yi wajan iyayena, amma matata Fasto ce kuma ban taba ce mata ta zama Musulma ba>>Inji Shugaba Tinubu

Ni gadon Musulunci na yi wajan iyayena, amma matata Fasto ce kuma ban taba ce mata ta zama Musulma ba>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a wajan jana'izar mahaifiyar shugaban jam'iyyar APC, Nana Lynda Yilwatda ya bayyana muhimmancin soyayya sama da kiyayya. Shugaban yace shi gadon Musulunci yayi a wajan iyayensa kuma bai taba neman canja addininsa ba. Yace matarsa Kirista ce, Fasto amma bai taba gaya mata ta zama musulma ba. https://twitter.com/NigeriaStories/status/1974496920312905814?t=mxOlc0UaOBW-ijj_RgXGRA&s=19