Wednesday, May 21
Shadow

Duk Labarai

Babu wata data fita daga Musulunci zuwa Kirista>>Gwamnatin Jihar Zamfara

Babu wata data fita daga Musulunci zuwa Kirista>>Gwamnatin Jihar Zamfara

Duk Labarai
Gwamnatin Zamfara ta karyata labarin dake cewa wata me suna Zainab ta fita daga Musulunci zuwa Kirista a jihar. Me magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar. Yace sun yi bincike ta hanyar kiran Alkalin Alkalai na jihar da kiran dukkan masu ruwa da tsaki na jihar kan bangaren shari'a duk sun tabbatar musu babu wata me suna Zainab data canja addini. Dan haka ya bayyana cewa labarin karyane wadda wata kafar yada labarai ta yanar gizo ta wallafa dan neman mabiya.
Shugaba Tinubu zai fara duba ayyukan Ministoci dan ganin wanne yafi kokari

Shugaba Tinubu zai fara duba ayyukan Ministoci dan ganin wanne yafi kokari

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai fara duba ayyukan Ministocinsa dan ganin wanne yafi kokari a cikinsu. Hakan ya bayyana ne daga wata majiya dake kusa da fadar shugaban kasar. Za'a duba kokarin ministocinne a cikin watanni 3 na farko na shekarar 2015. Hukumar CDCU wadda Hadiza Bala Usman ke jagoranta ce ke tattaro bayanan ministocin. Rahoton Punchng yace Tuni Ministocin da basu yi kokari ba sun fara tunanin me zai je ya dawo.
Sarkin Saudiyya, Salman bin Abdulaziz Al Saud ya ce a dauko Falasdiynawa 1000 wanda aka kàshè ‘yan uwansu, ko aka jikkata ‘yan uwansu ko aka kama ‘yan uwansu a kaisu su yi aikin Hajji Kyauta, zai biya kudin daga Aljihunsa

Sarkin Saudiyya, Salman bin Abdulaziz Al Saud ya ce a dauko Falasdiynawa 1000 wanda aka kàshè ‘yan uwansu, ko aka jikkata ‘yan uwansu ko aka kama ‘yan uwansu a kaisu su yi aikin Hajji Kyauta, zai biya kudin daga Aljihunsa

Duk Labarai
Me alfarna sarkin Saudiyya Salman bin Abdulaziz Al Saud ya bayar da umarnin dauko Falasdiynawa 1000 a kaisu aikin Hajji kyauta zai biya kudin daga Aljihunsa. Yace a zabo wadanda aka kashewa 'yan uwa ko aka jikkata musu 'yan uwa ko aka kama 'yan uwansu sune zai dauki nauyi. Ba wannan ne karin farko da Sarkin ya taba yin irin wannan abu ba, ko da a shekarun 2023 da 2024 duk ya bayar da irin wannan tallafi. Kasar Israyla dai ta kashe Falasdiynawa da yawa a ci gaba da yakin da tace tana yi da kungiyar Hàmàs. Salman bin Abdulaziz Al Saud
Kamfanonin Rarraba wutar Lantarki ne ke bamu matsala wajan magance matsalar rashin wuta>>Gwamnatin Tarayya

Kamfanonin Rarraba wutar Lantarki ne ke bamu matsala wajan magance matsalar rashin wuta>>Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ta koka da cewa, Kamfanonin raba wutar Lantarki, Discos ne ke kawo mata cikas wajan samar da ingantacciyar wutar lantrki a Najeriya. Ministan Wutar Lantarkin Adebayo Adelabu ne ya bayyana haka yayin ganawa da kwamitin majalisar Dattijai dake kula da makamashi. Yace kamfanonin rarraba wutar basa zuba hannun jari da ya kamata a cikin harkar dan inganta aikinsu. Me magana da yawun Ministan, Bolaji Tunji ne ya bayyana haka inda yace wannan halin rashin ko in kula da kamfanonin Discos din na taimakawa wajan rashin raba wutar yanda ya kamata a Najeriya
Ba a zaɓe mu don mu yi fada da shugaban ƙasa ba – Akpabio

Ba a zaɓe mu don mu yi fada da shugaban ƙasa ba – Akpabio

Duk Labarai
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa 'yan Majalisar Dokoki ta Kasa ba a zabe su bane domin su yi takaddama da bangaren zartarwa na gwamnati, sai dai don su inganta manufofin da ke kara ci gaban kasa. Shugaban Majalisar Dattawan ya yi wannan bayani ne a wani taron kaddamar da wani fim da za a saki domin bikin cika shekaru biyu da mulkin Bola Tinubu. A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun fadar shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata, Akpabio ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin bangaren majalisa da na zartarwa, inda ya ce: “Lokacin da aka zabe ka zuwa Majalisar Dokoki, ko dai a Majalisar Dattawa ko Wakilai, al’ummarka ba za su ba ka safar dambe ba. Ba gasa ce ta dambe ba. An tura ka ne domin ka yi aiki cikin hadin kai don amfani...
Tuni ƴan Najeriya su ka dawo daga rakiyar ɓangaren shari’a – El-Rufai

Tuni ƴan Najeriya su ka dawo daga rakiyar ɓangaren shari’a – El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce mutane da dama a Najeriya sun daina yarda da bangaren shari’a wajen samun adalci. Mista El-Rufai ya kuma zargi bangaren shari’ar da cin hanci da rashawa, yana cewa wasu alkalai da lauyoyi sun sauka daga abinda ke kansu ta hanyar karkata ko karɓar rashawa wajen yanke hukunci. Tsohon gwamnan ya bayyana haka ne yayin makon shari’a na kungiyar lauyoyi ta Najeriya (Nigerian Bar Association), reshen Bwari, da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin. Ya bayyana cewa rashin amincewar jama’a ga shari’a na da nasaba da yawan jinkiri wajen yanke hukunci da kuma shawarwarin da ake ganin sun samo asali daga son rai ko tasirin wasu masu hannu da shuni a waje. “A gefe guda, bangaren shari’armu—wanda ya kamata ya zama ginshikin adalci —yana fuskan...
Sabon Shèkàu ya fito tare da barazana ga CDS, sojoji da malaman addini

Sabon Shèkàu ya fito tare da barazana ga CDS, sojoji da malaman addini

Duk Labarai
Wani kwamandan Boko Haram da ya kira kansa da cewa shi ne sabon “Shekau,” ya yi barazana ga babban hafsan hafsoshin Najeriya, CDS, Christopher Musa, da malaman addinin Musulunci, da jami’an tsaro, da kuma al’ummomin da ke goyon bayan ayyukan gwamnati na yaki da ta’addanci. Barazanar ɗan ta’addan ba ta rasa nasaba ga gargadin da Musa ya yi tun farko a cikin harshen Hausa, inda ya yi kira ga yan ta’addan da su mika wuya ko kuma su fuskanci fushin sojojin Najeriya. A wani sabon faifan bidiyo da kafar yada labarai ta PRNigeria ta samu kuma ta fassara daga Hausa zuwa turanci, maharin ya mika sakon ban tsoro ga Janar Musa, inda ya bukaci shi da rundunar sojojin Najeriya da su yi watsi da yakin da suke yi da kungiyar. Ya yi ikirarin cewa, kamar magabatan sa, Musa ba zai yi nasarar murkus...
Majalisar Wakilai ta umarci a bada tsaro na tsawon shekaru 10 ga ɗan jaridar da ya bankado badakalar digiri dan kwatano

Majalisar Wakilai ta umarci a bada tsaro na tsawon shekaru 10 ga ɗan jaridar da ya bankado badakalar digiri dan kwatano

Duk Labarai
Majalisar Wakilai ta amince da bada kariya ta tsaro na tsawon shekaru 10 ga wakilin DAILY NIGERIAN mai binciken ƙwaƙwaf, Umar Audu, biyo bayan fallasa yadda ake baƙalar kwali digiri a Kwatano, amhuriyar Benin. Binciken da Audu ya yi a boye ya bankado wani gungun mutane da ke taimaka wa ‘yan Najeriya siyan kwallon digiri da ba su yi karatun ba, wadanda da yawa aka sahale musu aiki a ma'aikatun gwamnati, ciki har da ma’aikatar ilimi suka wanke su ta hanyar damfara. A halin yanzu dai kwamitin majalisar tarayya mai kula da jami’o’i, da fasaha, da harkokin cikin gida, da harkokin kasashen waje, da kuma ci gaban matasa, na binciken badakalar. A zaman sa a yau Litinin, shugaban kwamitin, Abubakar Fulata, ya sanar da umarnin majalisar tare da yin kira ga rundunar ‘yan sandan Najeriya da s...
Hukumar tace fina-finai da dab’i ta jihar Kano, ta janye dakatarwar da ta yi daga haska wasu finafinai 22 a jihar

Hukumar tace fina-finai da dab’i ta jihar Kano, ta janye dakatarwar da ta yi daga haska wasu finafinai 22 a jihar

Duk Labarai
Freedom Radio ta rawaito cewa hukumar tamince da ci gaba da haska fina-finan da ta dakatar a masana'antar Kannywood domin kada masu samar da su, su tafka asara. A wata sanarwa da kungiyar masu shirya fina-finai ta jihar Kano MOPPAN karkashin shugabanta Ado Ahmad gidan Dabino ta fitar ta ce sun yi zama da shugabannin hukumar tace fina finan ta jihar Kano. Sanarwar ta ruwaito cewa, matsayar da aka cimma ta hada da ci gaba da haska fina finan da aka dakatar, tare da bayar da wa'adin mako guda ga masu shirya fina finan su mika duk wani shirin su a gaban hukumar domin tantancewa.