Monday, April 20
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Za’a mayar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai gidan gyara hali na Kaduna bisa sabbin zarge-zargen da ake masa

Da Duminsa: Za’a mayar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai gidan gyara hali na Kaduna bisa sabbin zarge-zargen da ake masa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa hukumomi na shirin mayar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai jihar Kaduna dan ci gaba da tsareshi a can. Hakan na zuwane yayin da ake shirin fara shari'ar sa akan wasu sabbin zarge-zargen da ake masa. Hakan ya fito ne daga Sahara Reporters inda tace ta samu rahoton daga majiya me karfi. Saidai bata bayyana sabbin zarge-zargen da akewa El-Rufai ba. Majalisar jihar ta Kaduna dai ta bayyana yin bincike da gano aikata ba daidai ba a zamanin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na Gwamnan Kaduna. A yanzu dai malam Nasiru Ahmad El-Rufai na tsarene a hannun Hukumar ICPC.
Da Duminsa:Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya aikawa kotu da korafi kan wata Mugunta da take hakkinsa da ake masa a ofishin ICPC

Da Duminsa:Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya aikawa kotu da korafi kan wata Mugunta da take hakkinsa da ake masa a ofishin ICPC

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya aikewa da kotun Magistrate dake Abuja da korafin cewa, ana kokarin take masa hakkinsa a matsayinsa na dan kasa. ElRufai yayi zargin cewa, shugaban Hukumar ICPC din Musa Adamu Aliyu ta hannun wasu yaransa ya bayyana masa cewa sharadin sakinsa shine sai idan ya amince zai daina shiga harkar siyasa. El-Rufai ta hannun Lauyansa yace wannan kokarine na take masa hakkinsa a matsayinsa na dan kasa wanda ba zai lamunta ba. Zuwa yanzu dai Hukumar ta ICPC bata ce uffan ba kan zargin da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya mata.
Tauraruwar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj zata maka wani dan Najeriya a kotu saboda ya ce mata tsohuwa

Tauraruwar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj zata maka wani dan Najeriya a kotu saboda ya ce mata tsohuwa

Duk Labarai
Tauraruwar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj ta bayyana shirin maka wani dan Najeriya a kotu saboda ya ce mata tsohuwa. Nicki Minaj ta bayyana hakane bayan da mutumin me suna Dr. Penking ya bayyana ta a matsayin 'yar shekaru 43 wadda kuma ta tsufa. Inda ya kara da cewa ya kamata ta daina waka. https://twitter.com/i/status/2032753621310283913 Saidai abin bai mata dadi ba Da farko dai ta yiwa Lauyanta magana inda tace zasu saka dan Najeriyar cikin wanda zasu yi kararsu, saidai daga baya ko mi ta gani sai ta goge sakon. Saidai shi dan Najeriyar yace a shirye yake ya fuskanceta a kotu dan yana da 'yancin fadar Albarkacin bakinsa kuma ra'ayinsa ya bayyana. https://twitter.com/i/status/2033095286499770596