Sunday, February 15
Shadow

Duk Labarai

Wata Sabuwa: Kalli Abinda Dan Damben Najeriya, Anthony Joshua yayi bayan Khàdàrìn daya rutsa dashi da abokansa biyu inda abokan suka rasu da ya sa aka fara zarginsa

Wata Sabuwa: Kalli Abinda Dan Damben Najeriya, Anthony Joshua yayi bayan Khàdàrìn daya rutsa dashi da abokansa biyu inda abokan suka rasu da ya sa aka fara zarginsa

Duk Labarai
Wani Bidiyo ya bayyana da ya nuna dan Damben Najeriya, Anthony Joshua yana waya tare da dayan dan damben Najeriyar, Kamaru Usman bayan Khadarin motar da ya rutsa dashi da abokansa. A Bidiyon an ga yanda Kamaru Usman kewa Anthony Joshua jaje inda yake ce masa ya girgiza mutanen Duniya. An ga Anthony Joshua yana dariya a Bidiyon. Saidai Bidiyon ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa me zai sa Anthony Joshua ya rika dariya ko dai tsafi yayi da abokan nasa biyu da suka rasu a hadarin? Wasu kuma sun bayyana cewa bai kamata ace an dauki Bidiyon wayar da suka yi din ba. https://twitter.com/i/status/2009171100836524346 Saidai bayan da cece-kucen da Bidiyon ya jawo, Kamaru Usman ya fito ya bayar da hakuri. Yace shine ke da laifi domin akan daukar Bidiyon domin a lokacin yana sh...
A yau ko Gobe zamu biya Super Eagles hakokinsu>>Inji Gwamnatin tarayya

A yau ko Gobe zamu biya Super Eagles hakokinsu>>Inji Gwamnatin tarayya

Duk Labarai
Bayan da Kungiyar kwallon kafar Najeriya, Super Eagles suka fito suka ce ba zasu buga wasan Algeria a gasar AFCON da ake bugawa a kasar Morocco ba saboda hakkokinsu da ba'a biya ba. Gwamnatin tarayya tace an shirya tsaf dan biyan hakkokin na 'yan wasan kuma zasu ya fara ganin Alert yau ko gobe. Karamar Ministar kudi, Doris Nkiruka Uzoka Anite ce ta bayyana hakan a sanarwar data fitar. Tace CBN ya fitar da kudin kuma an canjasu zuwa dala za'a Turawa kowane dan wasa zuwa Asusunsa na banki na Dala.
Majalisar Jihar Kano ta ce tana goyon bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma APC hakanan kuma suma zasu bishi zuwa APC din

Majalisar Jihar Kano ta ce tana goyon bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma APC hakanan kuma suma zasu bishi zuwa APC din

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Majalisar jihar Kano ta goyi bayan Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya koma jam'iyyar APC. Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini ne ya bayyana hakan a ganawa da manema labarai inda yace ba zai yiyu su ci gaba da zama a jam'iyyar NNPP ba saboda rikicin dake cikin jam'iyyar yayi yawa. Yace ba zasu yadda abinda ya faru a jihar Zamfara ya faru dasu ba. Ya kara da cewa suna goyon bayan Hadda Kwankwaso su canja jam'iyya saboda rikicin jam'iyya ya mamaye jam'iyyar NNPP.
Da Duminsa: ‘Yan APC da magoya bayan Tinubu sun fito zanga-zangar neman Shugaba Tinubu ya sauke Wike a matsayin Ministan Abuja

Da Duminsa: ‘Yan APC da magoya bayan Tinubu sun fito zanga-zangar neman Shugaba Tinubu ya sauke Wike a matsayin Ministan Abuja

Duk Labarai
Wasu 'yan Jam'iyyar APC magoya bayan Tinubu da Shettima sun fito zanga-zangar neman shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kori Ministan babban birnin tarayya, Abuja Nyesom Wike. Sun bayyana hakan ga manema labarai a budaddiyar wasika. Sun mikawa shugaban jam'iyyar APC, Prof. Nentawe Goshwe Yilwatda wasikar inda suka bukaci ya mikawa shugaba Tinubu. Sun Zargi Wike da sukar jam'iyyar APC da yi mata zagon kasa.
A A Rano ya bude gidan mai na farko wanda babu me zuba man fetur wanda zai rika aiki ba dare ba rana

A A Rano ya bude gidan mai na farko wanda babu me zuba man fetur wanda zai rika aiki ba dare ba rana

Duk Labarai
Alhaji Auwalu Abdullahi Rano, me kamfanin A A Rano ya bude gidajen man fetur na farko da zasu rika aiki awanni 24, ba dare ba rana kuma babu me zuba mai. Mutum ne da kansa zai shiga da abin hawansa gidan man ya sa katinsa na ATM ya biya ya kuma zuba man ya kara gaba. A A Rano sun hada kai da kamfanin Petrosoft Limited ne dan samar da wannan tsari. Ya bayyana cewa, hakan zai saukakawa Kwastomominsu shan man sannan kuma zai saukaka musu aiki suma. A A Rano yace sabbin gidajen man zasu fara aiki a watan Janairu.