Friday, February 13
Shadow
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda Mahaifi ya fito ya bayar da hakuri kan Bidiyon da bai dace ba da diyarsa ta wallafa a shafinta

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda Mahaifi ya fito ya bayar da hakuri kan Bidiyon da bai dace ba da diyarsa ta wallafa a shafinta

Duk Labarai
Wannan Wani Mahaifi ne da ya fito ya baiwa Duniya Hakuri kan Bidiyon da diyarsa ta wallafa wanda ya nuna tsiraicinta. Ya bayyana cewa, sun mata fada sannan ta musu alkawarin ba zata sakw aikata hakan ba. Yace yana baiwa masu bibiyarta Hakuri. https://www.tiktok.com/@bilkis_muktar/video/7600063502614564117?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7600063502614564117&source=h5_m&timestamp=1769681441&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7568740291232040721&share_link_id=547fa81c-79a3-...
Wani Dan Jarida yace Babu kwarewa a yanda ma’aikaciyar BBCHausa, Madina Maishanu ta yi hira da Kwankwaso

Wani Dan Jarida yace Babu kwarewa a yanda ma’aikaciyar BBCHausa, Madina Maishanu ta yi hira da Kwankwaso

Duk Labarai
Wani Dan Jarida ya bayyana cewa, Babu Kwarewa game da yanda Madina Maishanu, ma'aikaciyar BBCHausa ta yi hira da jagoran Kwankwasiyya, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso. Ya bayyana cewa, akwai 'yan jarida da yawa na Duniya wanda suka yi hira da manyan mutane kuma sun rika dariya suna tattaunawa irin yanda ya kamata amma hakan bai sa sun sabawa dokar aikinsu ba. https://twitter.com/i/status/2016564987553104217
Inna LILLAHI wa inna ilaihi raji’un, Kalli Bidiyon yanda aka yi barin whùtà sosai a babban birnin Niamey na kasar Nijar

Inna LILLAHI wa inna ilaihi raji’un, Kalli Bidiyon yanda aka yi barin whùtà sosai a babban birnin Niamey na kasar Nijar

Duk Labarai
A daren jiya, an samu barin wuta sosai a babban birnin Niamey dake kasar Nijar. An ga yanda makamai ke harba abubuwa sama. A wani Bidiyo daya watsu sosai a kafafen sada zumunta, an ji mutane nata salati da hailala. Wasu rahotanni sun ce wani abune aka gani yana shawagi a sararin samaniyar kasar wanda ba'a san dashi ba. A filin jirgin kasar ma, an ga yanda mutane suka kidime kowa nata kansa. https://twitter.com/i/status/2016664645579178146 https://twitter.com/i/status/2016673272427901204 https://twitter.com/i/status/2016671216329691255
An fara: Ji shaguben da Hadimin Gwamnan Kano yawa Kwankwaso da ya dauki hankula sosai

An fara: Ji shaguben da Hadimin Gwamnan Kano yawa Kwankwaso da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Me baiwa Gwamnan Kano shawara akan harkokin kafafen sada zumunta, Salisu Yahaya Hotoro ya yi wani Rubutu da ake zargin da Kwankwaso yake, duk da bai kira suna ba. Ya rubuta cewa, Kwanannan mutane zasu fahimci wanene ya ci amanar mutanen Kano kuma wanene ya tsaya tare dasu yake kare muradinsu. Yace dambarwa irin ta Novemed, data Scholarship, da dambarwar sayar da filaye, dambarwar tsaftace ruwan Kano, da sauran rikita-rikitar cin hanci da Rashawa sune suka kawo mu matsayin da ake yanzu. Kamar yanda Imran U. Wakili ya ruwaito(@IU_Wakilii) https://twitter.com/i/status/2016428116692849077
Kasuwar Onitsha zata ci gaba da kasancewa a kulle har na tsawon sati daya>>Inji Gwamna Soludo

Kasuwar Onitsha zata ci gaba da kasancewa a kulle har na tsawon sati daya>>Inji Gwamna Soludo

Duk Labarai
Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya sake nanata cewa, Kasuwar Onitsha zata ci gaba da kasancewa a kulle har na tsawon sati daya. Yace idan kuma litinin ta zo 'yan kasuwar suka ki budewa, kamar yanda suka saba, zai sake kulleta na tsawon sati biyu. Yace tunda hutu suke so, zai taimaka musu su huta da kyau. Hakanan yace idan aka ci gaba da kulle kasuwar, zai kwace shagunan masu kulle shagonsu ya baiwa wadanda suka shirya yin kasuwanci. https://twitter.com/i/status/2016503952573862074 Hakan na zuwane yayin da 'yan kasuwar suka fito suka tare babbar gadar Onitsha suka hana shiga da fita daga garin.
Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un: Jirgin saman Sojojin Najeriya ya kara yin kuskure akan farar Hula

Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un: Jirgin saman Sojojin Najeriya ya kara yin kuskure akan farar Hula

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Naija na cewa, jirgin sojin saman sojojin Najeriya ya sake kuskurewa akan farar hula a jihar Naija. Lamarin ya farune a Kurgi dake karamar hukumar Kuriga. Lamarin ya farune ranar 25 ga watan Janairu wanda ya yi sanadiyyar jikkatar mutane da dama. An jima dai ana samun irin wannan kuskuren akan farar Hula a Najeriya.
Kalli Bidiyon matakin da ‘yan Kasuwar Onitsha suka dauka bayan da Gwamnan jihar ya kulle kasuwar saboda suna kin fitowa kasuwa ranar Litinin

Kalli Bidiyon matakin da ‘yan Kasuwar Onitsha suka dauka bayan da Gwamnan jihar ya kulle kasuwar saboda suna kin fitowa kasuwa ranar Litinin

Duk Labarai
A jiyane da muka kawo muku Rahoton cewa, Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya kulle kasuwar Onitsha na tsawon sati daya. Dalili shine 'yan kasuwar na biyewa tshageran dake hanasu bude shaguna ranar Litinin. A martanin 'yan kasuwar, sun je gadar Onitsha inda suka ajiye motocinsu suka hana shiga da fita garin dan nuna fushinsu da matakin da gwamnan ya dauka. https://twitter.com/i/status/2016412406876897514