Sunday, January 11
Shadow
Direban Motar su Anthony Joshua yace da Anthony Joshua ne ke zaune a gaban Motar amma yace yana kare masa Madubi ya koma baya, abokinsa ya koma zama gaban motar

Direban Motar su Anthony Joshua yace da Anthony Joshua ne ke zaune a gaban Motar amma yace yana kare masa Madubi ya koma baya, abokinsa ya koma zama gaban motar

Duk Labarai
Direban motar da ta yi hadari da dan damben Najeriya, Anthony Joshua inda har abokansa 2 suka rasu yace da Anthony Joshua ne ya zauna a gaban motar. Yace amma daga baya sai yace yana kare masa madubin gefe ya koma baya abokinsa ya dawo gaban motar. Abokan Anthony Joshua biyu dai duka sun rasu a hadarin inda shi kuma ciwuka ba masu tsanani ba yaji.
An yi min wahayin cewa, Tinubu ko shine da kansa zai zama shugaban INEC ba zai ci zaben 2027 ba muddin ya dage sai ya karbi Haraji a hannun ‘yan Najeriya>>Inji Fasto Ayodele

An yi min wahayin cewa, Tinubu ko shine da kansa zai zama shugaban INEC ba zai ci zaben 2027 ba muddin ya dage sai ya karbi Haraji a hannun ‘yan Najeriya>>Inji Fasto Ayodele

Duk Labarai
Fasto Ayodele ya bayyana cewa, ko Tinubu ne zai zama shugaban INEC, ba zai ci zaben shekarar 2027 ba muddin ya dage akan sai ya karbi kudin Haraji a hannun 'yan Najeriya. Ya bayyana hakane a cocinsa ga mabiyansa. https://twitter.com/i/status/2007162007884313013 Hakan na zuwane yayin da shugaba Tinubu yace maganar karbar Haraji ba gudu ba ja da baya.
Sabbin Bayanai sun fito game da jirgi marar Matuki da ya fadi a jihar Naija

Sabbin Bayanai sun fito game da jirgi marar Matuki da ya fadi a jihar Naija

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Wani Jirgi marar Matuki ya fadi a dajin jihar Naija. Lamarin ya dauki hankula da saka fargaba a zukatan mutane. Musamman ma saboda harin da kasar Amurka ta kawo Najeriya a jihar Sokoto a kwanakin baya. Saidai sabbin bayanan da ake samu game da jirgin shine cewa, na sojojin saman Najeriya ne dake tattara bayanai daga Tshàgyèràn Dhàjì. Me magana da yawun hukumar sojojin saman Najeriya, Air Commodore Ehimen Ejodame ya tabbatar da hakan. Yace jirgin yana tattara bayanai ne daga Tshàgyèràn Dhàjì a yayin da ya fadi inda yace amma bai kashe kowa ba ko jikkata kowa ba. Yace amma cikin hadin gwiwa da sauran abokan aikinsu, an dauko jirgin daga inda ya fadi.
Da Duminsa: Bayan Khàdàrìn da ya faru da Anthony Joshua inda abokansa 2 suka rasa ransu, Wani cikin wanda suka taru dan taimaka musu ya sace wayar Anthony Joshua

Da Duminsa: Bayan Khàdàrìn da ya faru da Anthony Joshua inda abokansa 2 suka rasa ransu, Wani cikin wanda suka taru dan taimaka musu ya sace wayar Anthony Joshua

Duk Labarai
Rahotanni sun kara fitowa game da hadarin mota da dan Damben Najeriya, Anthony Joshua yayi da abokansa 2 Wanda abokan suka rasu. Kawun Anthony Joshua yace bayan faruwar Hadarin, wadanda suka taru dan taimakawa Anthony Joshua an samu wani ya sace masa waya. Lamarin ya baiwa mutane mamaki musamman ganin cewa, Mutum na cikin halin tashin hankali irin wannan a samu wani ya masa sata?
An dauke Wuta a wani sashe na kasar Amurka inda sama da mutane 300,000 suka fada Duhu

An dauke Wuta a wani sashe na kasar Amurka inda sama da mutane 300,000 suka fada Duhu

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Amurka na cewa, an dauke wutar lantarki a kasar wanda ya jefa mutane 350,000 cikin Duhu. Lamarin ya farune dalilin ruwa me tsanani da iska da aka yi a yankin Michigan. Mahukunta sun yi gargadin cewa, mutane su kiyaye akwai yiyuwar ci gaba da ruwan da kankara. Saidai wannan labarin yasa hukumar kula da wutar lantarki mamaki, inda har suka saka alamar ido a bude sosai a kafar X, watau Alamar abin ya basu mamaki kenan. Da yawan 'yan Najeriya sun ji haushin wannan lamarin inda suke cewa ai dauke wutar ba irin na Najeriya bane da ake yi kullun. https://twitter.com/i/status/2007087923242443090
Da Duminsa: Sabbin Bayanai sun fito game da shirin komawar Gwamna Abba Jam’iyyar APC

Da Duminsa: Sabbin Bayanai sun fito game da shirin komawar Gwamna Abba Jam’iyyar APC

Duk Labarai
Rahotonni nata kara karfi kan shirin komawar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf jam'iyyar APC. Sabbin Rahotannin da ake samu shine cewa nan da ranar Litinin in Allah ya kaimu, Gwamna Abba Kabir Yusuf a hukumance zai koma jam'iyyar APC. Hakan na zuwane yayin da siyasar Kano ke ci gaba da daukar Dumi. Ana ganin wannan komawar ta Gwamna Abba jam'iyyar APC zata iya kawo baraka tsakaninsa da Dr. Rabiu Musa Kwankwaso.
Kalli Bidiyon abinda wani dan Kungiyar Kwallon Kafa ta Al Ahli yawa Ronaldo a filin wasa da ya baiwa Ronaldon Haushi

Kalli Bidiyon abinda wani dan Kungiyar Kwallon Kafa ta Al Ahli yawa Ronaldo a filin wasa da ya baiwa Ronaldon Haushi

Duk Labarai
Bayan wasan da aka buga tsakanin Al Ahli da Alnasr da aka tashi Al Ahli ta yi nasara da 3-2, wani abu ya faru tsakanin Ronaldo da wani ma'aikacin Kungiyar ta Al Ahli. Yayin da Ronaldo ya ke fita daga filin wasan, ma'aikacin kungiyar Al Ahli, ya zo ya wuceshi yana fadar Messi, Messi. Abin yawa Ronaldo Haushi, har sai da Ronaldon ya je ya sameshi. Lamarin ya dauki hankula sosai. https://twitter.com/i/status/2007178627436437564
Na baku kwana 3, ko dai ku sakeni, ko kuma zaku nenemi ku rasa>>Faston nan na asar Ghana da yace za’a yi tashin Qiyama ranar Kirsimeti amma ba’a yi ba

Na baku kwana 3, ko dai ku sakeni, ko kuma zaku nenemi ku rasa>>Faston nan na asar Ghana da yace za’a yi tashin Qiyama ranar Kirsimeti amma ba’a yi ba

Duk Labarai
Fasto Ebo Noah wanda ya ce wai an masa wahayi za'a yi tashin Qiyama ranar Kirsimeti, 25 ga watan Disamba amma ba'ayi ba, ya gargadi hukumomin kasar Ghana da suka kamashi. Faston dai an kamashine saboda wannan abu da yayi ya dauki hankulan Duniya. Saidai ya gargadi hukumomin kasar Ghana da cewa ya basu kwanaki 3 ko dai su sakeshi ko ya bace daga gidan yarin da ake tsare dashi.
Kalli Bidiyon: Magoya bayan Kungiyar Kwallon kafa na kasar Senegal na ta shan Yabo saboda yanda suka tsaya bayan kammala wasa suka share filin wasan

Kalli Bidiyon: Magoya bayan Kungiyar Kwallon kafa na kasar Senegal na ta shan Yabo saboda yanda suka tsaya bayan kammala wasa suka share filin wasan

Duk Labarai
Magoya bayan kungiyar kwallon kafa na kasar Senegal sun tsaya bayan an kammala wasa suka share filin tas. Hakan ya jawo musu yabo sosai da wannan hali na tsafta da suka nuna. https://twitter.com/i/status/2007138542506725416 A gasar cin kofin Duniya, magoya bayan kwallon kafa na kasar Japan sun rika yin irin wannan abu. A jiya ne dai Hutudole ya kawo muku cewa suma 'yan kwallon kafar na kasar Senegal sun dauki hankula bayan da aka gansu sun tafi yin Sallar Juma'a.
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda Dan Danben Najeriya, Anthony Joshua yake sauraren Qur’ani kamin Khàdàrìn da ya rutsa dashi da abokansa

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda Dan Danben Najeriya, Anthony Joshua yake sauraren Qur’ani kamin Khàdàrìn da ya rutsa dashi da abokansa

Duk Labarai
An ga Anthony Joshua yana sauraren Qur'ani a cikin mota kamin Hadarin motar da ya rutsa dashi da abokansa. An ji yana cewa, yana rokon Allah ya taimakeshi, ya bashi nasara ya kuma daukakashi. https://twitter.com/i/status/2007203246549721523 Anthony Joshua da abokansa sun yi Khàdàrì inda abokan nasa biyu suka rigamu gidan gaskiya amma shi ya ji rauni. Tuni dai an sallameshi daga Asibiti.