Saturday, December 13
Shadow
Kalli Bidiyo: Buhari ya gama sukar Marigayi ‘Yar’adua amma shima gashi a Landan ya rigamu gidan gaskiya>>Inji Malam

Kalli Bidiyo: Buhari ya gama sukar Marigayi ‘Yar’adua amma shima gashi a Landan ya rigamu gidan gaskiya>>Inji Malam

Duk Labarai
Malam ya soki tsohon shugaban kasa, Marigayi, Muhammadu Buhari kan yanda ya rasu a Landan. Yace haka lokacin 'yaradua ya rika sukarshi bayan ya rasu a Asibitin kasar Saudiyya kuma gidajen jaridu sun buga. Yace yana fatan Allah yawa shugaba Buhari Rahama amma maganar gaskiya abinda shuwagabannin Najeriya ke yi na kasa kula da bangaren lafiya bai kamata ba. https://www.tiktok.com/@sheik.lawan.trium/video/7531105454777339192?_t=ZM-8yLFWs7rgJx&_r=1
Bamu Yadda ba: Kungiyar Malaman Jami’a ta Najeriya, ASUU za ta kai karar shugaba Tinubu Kotu saboda sakawa jami’ar UNIMAID dake Maiduguri sunan Muhammad Buhari

Bamu Yadda ba: Kungiyar Malaman Jami’a ta Najeriya, ASUU za ta kai karar shugaba Tinubu Kotu saboda sakawa jami’ar UNIMAID dake Maiduguri sunan Muhammad Buhari

Duk Labarai
Kungiyar malaman Jami'a ta ASUU tace zata kai karar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kotu saboda sakawa jami'ar UNIMAID dake Maiduguri sunan tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari. Kungiyar tace ta cimma wannan matsaya ne bayan taron data gudanar wanda ya hada hadda wakilan kungiyar dalibai. Sanarwar bayan taron da aka fitar ranar Juma'a wadda ta samu amincewar shugaban kungiyar Abubakar Mshelia da mataimakin sakatare na kungiyar, Peter Teri tace basu amince da wannan mataki ba. Hakanan sanarwar tace an dauki wannan mataki ne ba tare da tuntubar ma'aikatan jami'ar da kungiyar ta ASUU ba da kuma kungiyar daliban da suka kammala makarantar a baya ba. Sanarwar tace canja sunan zai shafin tarihin da makarantar ta kafa na tsawon shekaru 50 da suka gabata. Dan haka ace ...
Kalli Bidiyo: Mai Shadda ma ya zubar da hawaye saboda Ummi Nuhu

Kalli Bidiyo: Mai Shadda ma ya zubar da hawaye saboda Ummi Nuhu

Duk Labarai
Ba zan iya tuna rabon da kwalla ta fito a idona sai jiya. Wallahi akwai rashin hankali sosai a cikin rayuwar nan. Yawancin matan da muke sakawa a film da kuma matan da suke ganin sun waye sosai, ko kuma gangar daukaka tana buga musu to Ina son suje su bibiyi rayuwa da tashen da UMMI NUHU tayi a harkar Kannywood da kuma Fagen Daukaka. Rayuwar “ya mace gajera ce, domin duk kyanki duk daukakarki ba zaki taba kai shekara ashirin da duka wadannan abubuwan ba. Ya Allah ka shiryemu, kasa muyi kyakkyawan karshe.Wasu daga cikin matan da suke ganin babu wanda ya isa ya basu shawara, ko kuma ya fadamusu GASKIYA please Kuje Shafin GABON TALK SHOW ku Kalli hirar da da UMMI NUHU, na tabbatar sai jikinki yayi sanyi. Allah ya shiryemu baki daya, Ameen summa Ameen. Kalli Bidiyon anan https:...
Kalli Bidiyo: Sanata Abdul Ningi ya zama sanata daya Tilo da yace bai yadda a baiwa Gwamnatin Tinubu damar ciwo bashin Dala Biliyan $21 saboda akwai rufa-rufa a lamarin

Kalli Bidiyo: Sanata Abdul Ningi ya zama sanata daya Tilo da yace bai yadda a baiwa Gwamnatin Tinubu damar ciwo bashin Dala Biliyan $21 saboda akwai rufa-rufa a lamarin

Duk Labarai
Sanata Abdul Ningi ya bayyana cewa bashin da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta aikewa da majalisar bukatar ciwoshi akwai matsala Yace babu cikakkun bayanai karara da suka fadi yanda za'a kashe kudin bashin da suka kai Dala Biliyan $21 komai an yi shi a dukunkunene. Saidai duk da wannan korafi na Sanata Ningi bai hana majalisar amincewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ciwo bshin ba. https://twitter.com/ArewaFactsZone/status/1948698363433812057?t=5IVqsMrpMxG7niOUkzijSw&s=19
Kalli Bidiyo: Dansandan Najeriya ya koka da bashi Naira Miliyan 2.8 a matsayin kudin sallama bayan kammala aikin da ya shafe tsawon shekaru 35 yana yi, yace wannan rashin adalci be ba zai karbaba

Kalli Bidiyo: Dansandan Najeriya ya koka da bashi Naira Miliyan 2.8 a matsayin kudin sallama bayan kammala aikin da ya shafe tsawon shekaru 35 yana yi, yace wannan rashin adalci be ba zai karbaba

Duk Labarai
Wani tsohon dansandan Najeriya da yayi ritaya aka bashi Naira Miliyan 2.8 a matsayin kudin Sallama yace ba zai karbaba. A bidiyonsa da aka gani yana jawabi yace ya shafe shekaru 35 yana aiki amma a bashi Naira Miliyan 2.8 a matsayin kudin sallama, yace wannan cin fuska ne. Yayi kira ga shugaban 'yansanda da ya shiga lamarin. https://twitter.com/SaharaReporters/status/1948867610335941109?t=RtUE1n8GUawT5YULtv8BnA&s=19
Kalli Abincin da ake baiwa sojojin Najeriya, sun koka ba naka ko kifi a ciki

Kalli Abincin da ake baiwa sojojin Najeriya, sun koka ba naka ko kifi a ciki

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wannan shine kalar abincin da ake baiwa sojojin Najeriya da suka koka. Sojojin dake Yaki a jihar Borno na fama da rashin abinci me kyawu wanda suka ce ba nama ba kifi, kuma abincin kanshi kamar na 'yan gidan Firizin. Da yawa dai sun yi kiran ya kamata a gyara.
Da Duminsa: Aliko Dangote ya sauka daga shugabancin kamfaninshi na Simintin Dangote dan mayar da hankali kan Matatar mansa

Da Duminsa: Aliko Dangote ya sauka daga shugabancin kamfaninshi na Simintin Dangote dan mayar da hankali kan Matatar mansa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Dangote ya sauka daga shugabancin kamfanin sa na Siminti inda zai mayar da hankali kan matatar mansa. Me magana da yawun kamfanin nasa na Siminti, Anthony Chiejina ne ya bayyana hakan. Yace an nada Emmanuel Ikazoboh a matsayin sabon shugaban kamfanin simintin na Dangote. Yace hakanan an baiwa Hajiya Mariya Aliko Dangote mukamin daga daga cikin masu gudanarwa na kamfanin.