Friday, February 13
Shadow
Kudaden da Abubakar Malami ya sata sun fi wanda EFCC ta gano yawa>>Inji Abdurashid Maina

Kudaden da Abubakar Malami ya sata sun fi wanda EFCC ta gano yawa>>Inji Abdurashid Maina

Duk Labarai
Tsohon shugaban hukumar Fansho ta kasa, Abdulrashid Maina yayi zargin cewa kudaden da tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami ya sata sun fi Naira Biliyan 212 da EFCC ta gano yawa. Yace yasan hakane saboda shi aikinsa ne gano kudaden sata. Ya nemi a bashi aikin binciken Malami inda yace sai ya gano kudaden da ya sata duka. Yace amma Biliyan 212 ba komai bane cikin kudaden da Malami ya sace. https://twitter.com/i/status/2014358615449096320
An fara Magudun zaben shekarar 2027>>Atiku Abubakar ya koka

An fara Magudun zaben shekarar 2027>>Atiku Abubakar ya koka

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya koka da cewa, an fara magudin zaben shekarar 2027. Ya bayyana hakan a shafinsa na sada zumunta inda yace an fara hakannne ta hanyar kaucewa gyaran dokar zabe. Ya zargi majalisar tarayya da kaucewa gyara dokar zabe wadda zata sa kada a maimaita kuskuren da aka tafka a zaben shekarar 2023. Atiku yace idan ba'a gyara dokar zaben ba ba lallai a samu sakamakon zabe sahihi a zaben shekarar 2027 ba.
Kalli Bidiyon: A yau ma, Sarkij Kano, Muhammad Sanusi II ya je aji a jami’ar Northwest University, Kano inda ya ci gaba da daukar Darasi

Kalli Bidiyon: A yau ma, Sarkij Kano, Muhammad Sanusi II ya je aji a jami’ar Northwest University, Kano inda ya ci gaba da daukar Darasi

Duk Labarai
A yau ma me martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya sake komawa aji a jami'ar Northwest University, Kano inda ya ci gaba da daukar Darasi. An ga sanda yake shiga ajin. Sannan an ga yanda yake hira da abokan karatunsa. https://twitter.com/i/status/2014317025535901951 Hakanan an ga yanda 'yan matan ajin nasu suka rika daukar hoto dashi. https://twitter.com/i/status/2014336141416173841
Kalli Bidiyon: Ya kamata Atiku ta taimaki Najeriya kada ya tsaya takarar shugaban kasa a 2027>>Inji Hakim Baba Ahmad

Kalli Bidiyon: Ya kamata Atiku ta taimaki Najeriya kada ya tsaya takarar shugaban kasa a 2027>>Inji Hakim Baba Ahmad

Duk Labarai
Tsohon Hadimin shugaban kasa kuma daya daga cikin dattawan Arewa, Hakeem Baba Ahmad ya baiwa Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar shawarar kada ya tsaya takarar shugaban kasa a 2027. Ya bayyana cewa wannan shine abu daya mafi muhimmanci da ya ragewa Atiku yawa Najeriya. Ya bayyana hakane a wata Hira da aka yi dashi. https://twitter.com/i/status/2014262376405602354
Kalli Bidiyon yanda matasan yarbawa suka rika rokon Shahararren me amfani da Kafar Sada zumunta na Amurka, Ishowspeed kudi yayin da ya kawo ziyara Najeriya

Kalli Bidiyon yanda matasan yarbawa suka rika rokon Shahararren me amfani da Kafar Sada zumunta na Amurka, Ishowspeed kudi yayin da ya kawo ziyara Najeriya

Duk Labarai
Bidiyon matasan Yarbawa na rokon Shahararren me amfani da kafafen sadarwa na kasar Amurka, Ishowspeed da ya kawo Najeriya kudi ya dauki hankula. An gansu suna bin motarsa suka mika masa hannu suna cewa ya basu kudi. https://twitter.com/i/status/2013984153230774513 Lamarin ya jawo musu suka sosai inda da yawa ke cewa sun jawowa Najeriya abin kunya a Idon Duniya. Wasu 'yan Arewa sun rika cewa, kada wani ya kara zagin Arewa da cewa suna da Almajirai mabarata, tunda dai ta bayyana kowa yana roko. https://twitter.com/i/status/2014084512108380663
DSS sun hanani ganawa da iyali na da Lauyana>>Inji Abubakar Malami

DSS sun hanani ganawa da iyali na da Lauyana>>Inji Abubakar Malami

Duk Labarai
Tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami ya koka da cewa, Hukumar DSS sun ki barinshi ya gana da iyalansa da lauyansa. Ya bayyana hakane ta bakin lauyansa, Muhammad Doka inda yace tunda DSS suka sake kama Malami bayan an bayar da belinsa, sun hanashi ganawa da kowa. Yace zargin gano Makamai a gidan malami da kuma cewa, wai ana zarginshi da hannu a ayyukan ta'addancy duk karyane. DSS dai sun sake kama malami, jim kadan bayan da aka sakeshi daga gidan Gyara hali na Kuje.
Kalli Bidiyon abinda ya faru tsakanin malamin Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II a jami’ar Northwest University, Kano da sarkin

Kalli Bidiyon abinda ya faru tsakanin malamin Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II a jami’ar Northwest University, Kano da sarkin

Duk Labarai
Bayan kammala karatu, Malamin da ya kotar da Me martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II a jami'ar Northwest University, Kano yaki yadda ya baiwa sarkin Hannu su gaisa. Sarki Sanusi ya tashi inda zai fita daga ajin, ya mikawa Malamin hannu su gaisa, saidai malamin yaki amincewa ya baiwa Sarkin hannu. https://twitter.com/i/status/2013942641537233364 Lamarin ya dauki hankula.
Da Duminsa: An bukaci a saka Rev. Ezekiel Dachomo a Addu’a, Ciwon Hantane ya kamashi shiyasa aka ji shi  shiru ya daina magana akan Mhuzghunawar da akewa Kiristoci a Najeriya

Da Duminsa: An bukaci a saka Rev. Ezekiel Dachomo a Addu’a, Ciwon Hantane ya kamashi shiyasa aka ji shi shiru ya daina magana akan Mhuzghunawar da akewa Kiristoci a Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Filato sun bayyana cewa shahararren Faston nan me magana akan zargin Mhuzghunawa Kiristoci a Najeriya, watau Rev. Ezekiel Dachomo ya kamu da cutar Hanta Wani dan jarida daga jihar me suna, Masara Kim Usman ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ta shafinsa na sada zumunta. Yace Kiristoci su saka Rev. Ezekiel Dachomo a Addu'ar Allah ya bashi lafiya. Dama dai a baya ya taba kamuwa da cutar inda matarsa ta bashi kyautar daya aka dasa masa, saidai yanzu ciwon ya sake dawowa.