Tuesday, December 16
Shadow
‘Yan majalisar Dattijai sun tafi hutun wata biyu

‘Yan majalisar Dattijai sun tafi hutun wata biyu

Duk Labarai
'Yan majalisar Dattijai sun tafi hutun watanni biyu da suka saba yi duk shekara. Sai nan da watan Satumba 23 sannan zasu dawo daga hutun. Saidai kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa, sauran kwamitin majalisar zasu ci gaba da aiki a yayin da ake hutun. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1948374536266580176?t=DTCiNO-EVCw7S31bP4O4IA&s=19
Sabon shugaban APC ya ce zai janyo ƙarin gwamnonin PDP zuwa cikin jam’iyyar

Sabon shugaban APC ya ce zai janyo ƙarin gwamnonin PDP zuwa cikin jam’iyyar

Duk Labarai
Sabon shugaban jam'iyyar APC, Nentawe Yilwatda, ya ɗau alwashin ɗaukar matakai don ganin ya ƙara janyo gwamnonin babbar jam'iyyar adawa ta PDP zuwa cikin jam'iyyar mai mulki. Yilwatda ya bayyana haka ne yayin tattaunawa a cikin shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, jim kaɗan bayan zama shugaban APC. Ya ce baya ga ƴan jam'iyyar PDP da zai janyo zuwa APC, har da wasu ƴaƴan jam'iyyun adawa. "Abun da na fi mayar da hankali a yanzu shi ne ganin haɗin kan jam'iyyar mu," in ji shi - inda ya ce zai tabbatar da cewa jam'iyyar ta yaɗa manufofinta yadda ya kamata. Sabon shugaban jam'iyyar ta APC ya ce duba da irin tarihi da yake da shi a fannoni daban-daban, yana da ƙwarewar da ta kamata wajen jagorantar jam'iyyar mai mulki.
Tinubu yayi watsi da Arewa, kudu yake ta rayawa>>Inji Kwankwaso

Tinubu yayi watsi da Arewa, kudu yake ta rayawa>>Inji Kwankwaso

Duk Labarai
Tsohon gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Bola Ahmad Tinubu. Kwankwaso yace Tinubu ya mayar da hankali wajan kai abubuwan ci gaba kudu yayi watsi da Arewa. Kwankwaso ya bayyana bakane a yayin taron masu ruwa sa tsaki na jihar Kano inda ake tattauna batun gyaran kundin tsarin mulki. Yace da ya je Abuja ta jirgi ya so ya dawo amma sai aka samu matsala ya dawo ta Mota, yace titin Abuja zuwa Kaduna bashi da kyau ko kadan Kwankwaso yace amma Gwamnatin Tinubu na gina titi daga jihohin Yarbawa zuwa jihohin Inyamurai. Yace basa sukar yiwa jama'a aiki a kowane sashe na Najeriya amma a mayar da hankali wajan yiwa wani bangare aiki yayin da aka yi watsi da wani bangare hakan bai kamata ba.
Kalli Bidiyo: Tabbas Allah na yafe hakki ko da me hakkin bai yafe ba, Albanin Gombe ya goyi bayan Sheikh Asadussunnah

Kalli Bidiyo: Tabbas Allah na yafe hakki ko da me hakkin bai yafe ba, Albanin Gombe ya goyi bayan Sheikh Asadussunnah

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama da akewa lakabi da Albanin Gombe ya goyi bayan Sheikh Musa Asadussunnah kan ikirarin da yayi cewa ko da wanda aka zalinta bai yafe ba Allah na yafewa. Sheikh Musa Asadussunnah ya bayyana cewa Allah na yafe hakki ko da me hakki bai yafe ba inda take magana akan masu cewa Basu yafewa Buhari ba. Shima dai Albanin Gombe yace Annabi yace idan aka samu wanda basa shirka mutum 40 sukawa mutum Sallah, Allah yana yafewa matacce. Kalli Bidiyon anan https://www.tiktok.com/@janbiro_s4704ii/photo/7530456341895482680?_d=secCgYIASAHKAESPgo81wvmZLZhOW%2FalYNmSADG68FO1wPuQ%2BrxyO%2FgDW7AESJ1AhQBvOedrJgndnoxjTvEKhr7uopg8fsgo6X%2BGgA%3D&_r=1&_svg=1&aweme_type=150&checksum=200f6657f05b5a8e62a0977611db0df16620ec45b9becff5a913e6329659b214&link_reflow_popup...
Kalli Yanda Murna ta barke a Jos bayan tabbatar da Professor Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban APC

Kalli Yanda Murna ta barke a Jos bayan tabbatar da Professor Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban APC

Duk Labarai
Rahotanni daga Jos babban birnin jihar Flato na bayyana cewa, an barke da murna bayan da aka tabbatar da Professor Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam'iyyar APC. A yau ne dai aka bayyana Professor Nentawe Yilwatda a matsayin shugaban APC wanda ya maye gurbin Dr. Abdullahi Umar Ganduje. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1948410580412330452?t=I4o5VkpTFz11AhTXPakAmg&s=19 https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1948408360300163227?t=xnbcHp8N-7vTnVDC_j7UKw&s=19
Ku jikawa ‘yan Najeriya anta saboda naji anata korafin Yunwa>>Shugaba Tinubu ga Gwamnoni

Ku jikawa ‘yan Najeriya anta saboda naji anata korafin Yunwa>>Shugaba Tinubu ga Gwamnoni

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa gwamnonin Najeriya umarnin su yiwa talakawa yayyafin Alheri saboda a cewarsa ana ta korafi. Shugaban kasar ya bayyana cewa shine ke jagorantar kawo Chanji a Najeriya sannan kuma zasu ci gaba da yiwa 'yan Najeriya aiki tukuru. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1948399213571612900?t=VBsNxPK2FkRkrD-zPNnggA&s=19
Bidiyo Da Duminsa: Kalli yanda aka rantsar da Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam’iyyar APC

Bidiyo Da Duminsa: Kalli yanda aka rantsar da Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam’iyyar APC

Duk Labarai
https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1948382291501158620?t=JPwMiXjVE8kYlCeL9TdQVg&s=19 Jam’iyyar APC ta naɗa Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam’iyyar na ƙasa, bayan taron da aka gudanar a Abuja tare da shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnonin jam’iyyar. Yilwatda, wanda ya fito daga jihar Filato, ya maye gurbin Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya yi murabus a watan Yuni 2025 saboda dalilan lafiya. Kafin naɗinsa, Yilwatda na rike da mukamin Ministan Jin ƙai da Rage Talauci a gwamnatin Tinubu. Farfesa Nentawe ya kasance ɗan takarar gwamna a jihar Filato a zaɓen 2023 karkashin APC. Hakanan, ya taba zama kwamishinan zaɓe na hukumar INEC daga 2017 zuwa 2021, inda ya jagoranci harkokin zaɓe a jihohi da dama. Naɗin nasa ya zo ne da nufin ƙarfafa haɗin kai da dai...
Kalli Bidiyo:Malamai na Allah wadai da abinda wasu bata gari sukawa A’isha Buhari bayan Rashin Mijinta, Shugaba Muhammadu Buhari

Kalli Bidiyo:Malamai na Allah wadai da abinda wasu bata gari sukawa A’isha Buhari bayan Rashin Mijinta, Shugaba Muhammadu Buhari

Duk Labarai
An samu wasu suna saka hoton matar tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari, watau A'isha Buhari suna cewa ga bazawara idan akwai me so. Saidai malamai sun yi Allah wadai da hakan inda suka ce ya sabawa koyarwar addini. Malaman sun ce matar dakw cikin Takaba bai kamata a mata haka ba. https://www.tiktok.com/@hayatudden.jafar/video/7529164978113465605?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7529164978113465605&source=h5_m&timestamp=1753360461&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7510327615027545862&am...