Saturday, December 13
Shadow
Kalli yanda uwa ke zane diyarta saboda diyar tawa uwar kwacen saurayi

Kalli yanda uwa ke zane diyarta saboda diyar tawa uwar kwacen saurayi

Duk Labarai
Fada saboda saurayi ya zama ruwan dare musamman tsakanin dalibai 'yan mata a makarantun jami'a. Ko da a farkon watannan na Yuni da muke ciki, sai da aka ga wani Bidiyo yanda aka ci zarafin wata budurwa, 'yan mata da yawa suka taru akanta suna duka saboda saurayi. Abin takaici shine yanda aka dauki Bidiyon faruwar lamarin aka watsa shi a kafafen sada zumunta kowa yaga irin abinda akawa budurwar. Lamarin ya farune a jihar Ogun, kuma kawayen budurwar sun bayyana cewa da sanin mahaifiyarsu suka aikata wannan danyen aiki dan haka basa shakkar wani ya gani. Tuni dai hukumar 'yansandan jihar ta sanar da fara binciken kan lamarin. Saidai ko da an hukunta wadanda sukawa wannan Budurwa wannan cin zarafi, ba za'a iya goge tozarcin da suka mata ba. Uwa na dukan 'yarta saboda zata ma...
Bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira Tiriliyan N149.39tn

Bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira Tiriliyan N149.39tn

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira Tiriliyan N149.39tn. An tattaro bayanan yawan bashin da ake bin Najeriya har zuwa watan March 31, 2025 inda daga nan ne aka samu wadannan bayanai. A shekarar data gabata, 2024 dai yawan bashin da ake bin Najeriya Naira Tiriliyan N121.67tn ne wanda hakan ke nufin a yanzu bashin ya karu da Naira Tiriliyan N27.72tn ko ace da kaso 22.8 cikin 100. Ofishin dake kula da bashin da Najeriya ke ciyowa DMO ne ya fitar da wadannan bayanai ranar Juma'a. Yawan bashin da ake bin Najeriya na karuwa ne saboda kara cin bashin da gwamnatin tarayya take da kuma faduwar darajar Naira da sauransu. Gwamnatin tarayyar Najeriya dai na dogaro da bashi dan gudanar da ayyukanta, kuma tana cin bashin ne daga cikin gida Najeriya d...
Yayin da Wutar Lantarki ta gagari Gwamnatin tarayya gyarawa, Shugaba Tinubu yayi sabuwar doka da ta baiwa Jihohi ragamar samar da wutar Lantarki a Najeriya

Yayin da Wutar Lantarki ta gagari Gwamnatin tarayya gyarawa, Shugaba Tinubu yayi sabuwar doka da ta baiwa Jihohi ragamar samar da wutar Lantarki a Najeriya

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa sabon daftarin doka hannu wanda ya baiwa jihohin Najeriya damar samarwa da rarraba wutar Lantarki a jihohinsu. Tun a shekarar 2024 daftarin dokar ya wuce amincewar 'yan majalisa inda ake jiran shugaba Tinubu ya saka hannu amma bai saka ba sai a yau. Masana sun ce hakan ya canja kula da wutar lantarki a Najeriya wanda a baya yake hannun Gwamnatin tarayya, a yanzu jihohi ne zasu rika samar da wutar. Hakanan ana tsammanin wannan sabuwar dokar zata jawo masu zuba jari a harkar sannan zata karfafa gasa tsakanin jihohin wanda hakan zai inganta samar da wutar Lantarkin.
Ji sabon mukamin da Shugaba shugaba Tinubu ya baiwa Ganduje bayan sauka daga shugaban APC

Ji sabon mukamin da Shugaba shugaba Tinubu ya baiwa Ganduje bayan sauka daga shugaban APC

Duk Labarai
Rahotanni sun ce shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shirin baiwa tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje sabon mukami. Hakan na zuwane kwana daya da saukat Ganduje daga mukamin shugaban jam'iyyar APC. Wata majiya ta bayyanawa jaridar Vanguard cewa, Shugaban kasa Bola Tinubu kwanannan zai bayyana Ganduje a matsayin jakadan Najeriya zuwa kasar waje. A kwanakin baya dama an yada rade-radin cewa, Shugaba Tinubu na shirin baiwa Ganduje mukamin jakadanci amma maganar ta lafa. Wasu majiyoyi sun ce Ganduje a wancan lokacin ya ki karbar mukamin jakadane saboda yana jan zarensa a matsayin shugaban jam'iyyar APC wanda yana ganin kujerar shugaban jam'iyya tafi karfin ta Jakada. Da yawa a wancan lokaci sun yi mamakin irin karfin da Ganduje ke dashi a gwamnatin Tinubu ...
Mun yi babban rashi>>Shugaba Tinubu ya gayawa yi jimamin rasuwar Dantata

Mun yi babban rashi>>Shugaba Tinubu ya gayawa yi jimamin rasuwar Dantata

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi jimamin rasuwar Aminu Dogo Dantata a sakon da ya fitar ta bakin kakakinsa, Bayo Onanuga. Shugaban yace wannan rashi ne da Najeriya ta yi baki daya. Yace za'a tuna Dantata da kasuwancin da yayi da kuma taimakawa da yayi wajan hadin kan Najeriya ta wajan bayar da tallafin da ya amfani mutane da yawa. Tinubu ya bayyana Dantata a matsayin mutumin da ya bashi gudummawa wajan shawara me kyau. A karshe ya mikawa iyalan mamacin sakon ta'aziyya.
Dalori ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaban APC na riƙo

Dalori ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaban APC na riƙo

Duk Labarai
Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar Dalori ya maye gurbin Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam'iyyar na riƙo. Wannan na zuwa ne bayan tsohon gwamnan na jihar Kano ya ajiye muƙamin a ranar Juma'a, sannan aka naɗa Dokta Ali Bukar Dalori a matsayin wanda zai riƙe muƙamin, kafin a kai ga zaɓen wanda zai maye gurbinsa. Mutane dai sun yi zargin ruwa ba ya tsami banza, ko kuma dai da walakin goro a miya amma uwar jam'iyyar ta yi watsi da wannan hasashe. Bala Ibrahim shi ne daraktan yaɗa labarai na jam'iyyar ta APC, ya ce "Game da batun wanda zai maye gurbin shugaban jam'iyyar da sauka, dama jam'iyya na da kundin tsarin mulki wanda ya yi tanadi irin wannan wanda idan shugaban jam'iyya ya sauka daga muƙaminsa to za a zaɓi ɗaya daga cikin mataimakansa biyu...
Ji dalilin da ya sa yawanci shugabannin jam’iyyu a Najeriya ke sauka ba girma ba arziki?

Ji dalilin da ya sa yawanci shugabannin jam’iyyu a Najeriya ke sauka ba girma ba arziki?

Duk Labarai
A ranar Juma'a ne shugaban jam'yyara APC na Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya a jiye muƙaminsa na jangorancin jam'iyyar. Tsohon gwamnan jihar Kanon ya sauka da muƙamin nasa ne bayan shafe kusan shekara biyu riƙe da shugabancin jam'iyyar a matsayin riƙo bayan saukar Sanata Abdullahi Adamu. Wasu majiyoyi daga fadar shugaban Najeriya sun tabbatar wa BBC cewa Ganduje ya ajiye muƙamin ne bayan da fadar shugaban ƙasa ta umarce shi da yin hakan. "Da gaske ne Ganduje ya sauka tun ranar Alhamis aka ba shi umarnin ya rubuta takardar murabus, a ranar Juma'a da safe miƙa takardar," in ji majiyar. Kusan a iya cewa ya zama al'ada a tsarin siyasar Najeriya kusan duka mutanen da suka jagoranci manyan jam'iyyun ƙasar ba sa wanyewa lafiya da muƙaman nasu. Wasu daga cikinsu ana dakatar da su...
Karanta Jadawalin tsaffin shuwagabannin jam’iyyar APC da aka taba yi

Karanta Jadawalin tsaffin shuwagabannin jam’iyyar APC da aka taba yi

Duk Labarai
Wannan jadawalin shuwagabannin jam'iyyar APC ne da aka taba yi daga shekarar 2013 zuwa yanzu. 1. Chief Bisi Akande: 2013 - 20142. Chief John Odigie-Oyegun: 2014 - 20183. Comrade Adams Oshiomhole: 2018 - 20204. Mai Mala Buni: 2020 - 20225. Senator Abdullahi Adamu: 2022 - July 20236. Senator Abubakar Kyari (Acting). July 2023 - Aug 20237. Dr. Abdullahi Ganduje: 2023-2025.