Friday, December 5
Shadow
Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ce Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya koma jihar Kebbi da zama har sai an kubutar da dalibai ‘yan mata

Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ce Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya koma jihar Kebbi da zama har sai an kubutar da dalibai ‘yan mata

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle umarnin komawa jihar Kebbi da zama har sai an kubutar da dalibai mata da aka yi Gharkùwà dasu. Ana taammanin nan da ranar Juma'a ne Bello Matawalle zai koma jihar Kebbin da zama dan ya jagoranci kubutar da 'yan matan. Yara mata 25 ne dai aka sace daga makarantunsu inda kuma aka Khashye daya daga cikin malamansu Lamarin ya jawo Allah wadai da kiraye-kirayen a dauki mataki.
Shirmenshi ne kawai, Majalisar mu Bata amincewa Trump ya kawo Khari Najeriya ba>>Inji ‘Yar Majalisar Kasar Amurka, Sara Jacobs

Shirmenshi ne kawai, Majalisar mu Bata amincewa Trump ya kawo Khari Najeriya ba>>Inji ‘Yar Majalisar Kasar Amurka, Sara Jacobs

Duk Labarai
'Yar majalisar kasar Amurka, Sara Jacobs ta bayyana cewa babatun da shugaban kasar, Donald Trump ke yi na cewa, zai kawo Hari Najeriya shirme ne kawai. Tace dalili kuwa sai majalisa ta amince kuma majalisar bata amince maza ba. Tace sannan wannan magana ta rashin dacewa da Trump yayi maimakon ta taimaka, sai ma kara dagula lamura ta yi tsakanin Kiristoci da Musulmai a Najeriya Tace kuma kawo Hari a Najeriya ba tare da amincewar gwamnatin Najeriyar ba abune wanda zai sabawa dokar kasa da kasa. Tace kuma kawo Hari zai shafi fararen hula da yawa. Tace dan haka abinda yafi shine a bi hanyar Diplomasiyya dan warware wannan matsala.
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon yanda wasu dakw magana da Hausa ke Gassa naman Mhutaney suna ciy

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon yanda wasu dakw magana da Hausa ke Gassa naman Mhutaney suna ciy

Duk Labarai
Wani Bidiyo da ya bayyana a kafafen sada zumunta ya tayar da hankula sosai Bidiyon dai an bayyana cewa, wai 'yan Bìndìgà ne inda aka gansu suna magana da yaren Hausa, da alama kamar daga Zamfara ko Sokoto ne sannan akwai yanatin cewa akwai fulani a cikinsu. An ga yanda suke Gassa naman wani mutum suna Yhanka suna ci. Lamarin ya dauki hankula sosai inda akai ta Allah wadai da lamarin. Danna nan dan kallon Bidiyon
Ba Musulmai bane suka kai Khariy cocin jihar Kwara ba>>Inji Oyemyke

Ba Musulmai bane suka kai Khariy cocin jihar Kwara ba>>Inji Oyemyke

Duk Labarai
Wani dan kudu kuma Kirista me suna Oyemyke ya bayyana cewa, shi bai yadda ace musulmai ne suka kai Harin cocin jihar Kwara ba. Harin cocin jihar Kwara wanda ya faru a Bidiyo kai tsaye, ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda akaita Allah wadai dashi. Saidai Oyemyke yace ba musulmai bane, yace yayi hulda da musulmai da yawa yasa ba zasu rika aikata irin wannan abu ba. Yace 'yan siyasa ne kawai ke aikata wadannan abubuwan dan cimma burinsu. https://twitter.com/_hafsat_paki/status/1991216129579049005?t=V9dOA5OXCqSHb0eHlJiB9g&s=19
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda sojan Najeriya me suna Muhammad yace a taimaka masa Tun shekarar 2017 yake son ajiye aikin soja amma na sama dashi sun hanashi

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda sojan Najeriya me suna Muhammad yace a taimaka masa Tun shekarar 2017 yake son ajiye aikin soja amma na sama dashi sun hanashi

Duk Labarai
Wani Sojan Najeriya me suna Muhammad ya koka da cewa, tun shekarar 2017 yake ta son ya ajiye aiki amma an hanashi. Ya jawo hankalin shuwagabannin sojoji da ministan tsaro da Shugaban kasa da 'yan majalisa a cikin Bidiyon nasa inda yace su taimaka masa ya ajiye aikin. Yace a duk sanda yayi yunkurin ajiye aikin sai a rika masa hanyahanya. Yace wata matsalar iyali ce ta sanyashi gaba shiyasa ya ke son ajiye aikin. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1991469773134217657?t=jdDEOLrY8CfIk1WCceCelA&s=19
Da Duminsa: Kotu ta daurewa Nnamdy Khanu hukuncin daurin rai da rai

Da Duminsa: Kotu ta daurewa Nnamdy Khanu hukuncin daurin rai da rai

Duk Labarai
Rahotanni daga babbar kotun tarayya dake Abuja na cewa, Kotun ta daure shugaban kungiyar ÌPÒB dake son kafa kasar Biafra, Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai. Kotun tace ta sassauta masa ne maimakon hukuncin Khisa shine ta yanke masa hukuncin daurin rai da rai. Mai shari'a Justice James Omotosho ne ya yanke wannan hukunci inda yace laifin da ake zargin Nnamdi Kanu dashi yayi muni sosai shiyasa.
Matasa ga dama ta samu: Hukumar sojojin Najeriya ta sanar da shirin daukar Sabbin sojoji har guda dubu ashirin da hudu dan magance matsalar tsaro

Matasa ga dama ta samu: Hukumar sojojin Najeriya ta sanar da shirin daukar Sabbin sojoji har guda dubu ashirin da hudu dan magance matsalar tsaro

Duk Labarai
Hukumar sojojin Najeriya ta sanar da daukar matasa guda 24,000 a cikin watanni 6 masu zuwa dan magance matsalar tsaron data addabi Najeriya. Hakan ya fito daga bakin shugaban sojojin kasa,  Lieutenant General Waidi Shaibu ne a yayin ziyarar da ya kai rundunar sojoji ta 1 dake kaduna ranar Laraba. Ya bayyana cewa, zasu yi amfani da guraren horas da sojoji guda 3 da ake dasu wajan horaa da sojojin. Ya bayyana bukatar karin sojoji dan magance matsalar tsaro da ake fama da ita.
Kalli Karin Hotuna da Bidiyo na abinda tshageran Dhaji sukawa sojojin Najeriya da suka je ceto daliban jihar Kebbi

Kalli Karin Hotuna da Bidiyo na abinda tshageran Dhaji sukawa sojojin Najeriya da suka je ceto daliban jihar Kebbi

Duk Labarai
A wani Bidiyo da ya kara bayyana, an ga yanda tsageran daji suka yiwa sojojin Najeriya kwantan Bauna suka jikkata da yawa daga cikin sojojin. An ji wani soja yana cewa, Albashin nawa akw biyanshi duka duka inda yace ba zai iya ba. Danna nan dan kallon Bidiyon Jaridun Leadership da na Sahara Reporters duk sun tabbatar da wannan harin kwantan bauna da 'yan Bindiga suka kaiwa tawagar sojojin da suka tafi kubutar da 'yan mata 'yan makarantar jihar Kebbin. Babu dai wata sanarwa a hukumance da aka fitar.
Inada masaniya kan Inda ake tsare da ‘yan mata ‘yan makaranta na jihar Kebbi>>Inji Sanata Garba Maidoki

Inada masaniya kan Inda ake tsare da ‘yan mata ‘yan makaranta na jihar Kebbi>>Inji Sanata Garba Maidoki

Duk Labarai
Sanata Garba MaiDoki daga jihar Kebbi ya bayyana cewa suna da masaniya kan inda 'yan Bindiga suka boye 'yan mata 'yan makaranta da suka sace. Ya bayyana hakane a wata ganawa da aka yi dashi a Channels TV inda yace ba'a fita da 'yan matan daga yankin Kebbi ta kudu ba. Ya kuma bayar da tabbacin nan da kwanaki 1 zuwa 2 za'a dawo da 'yan matan. 'Yan mata 'yan makaranta su 25 ne dai aka sace daga Maga jihar Kebbi.
Mun samu nasara sosai akan tshageran Dhaji amma kalaman Shugaban Amurka, Trump ya sa suka samu karfin Gwiwar dadowa har suka dauke daliban jihar Kebbi>>Inji Gwamnatin tarayya

Mun samu nasara sosai akan tshageran Dhaji amma kalaman Shugaban Amurka, Trump ya sa suka samu karfin Gwiwar dadowa har suka dauke daliban jihar Kebbi>>Inji Gwamnatin tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana rashin jin dadi kan kalaman shugaban kasar Amurka, Donald Trump na cewa zai kawowa Najeriya hari. Gwamnatin tace wadannan kalaman ne suka karfafa 'yan ta'dda har suka dawo suka kai hari makarantar 'yan mata ta jihar Kebbi. Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume ne ya bayyana hakan ranar Laraba. Yace sun samu nasara sosai akan 'yan Bindigar amma kalaman na Trump yasa suka dawo har suke samun kara fadada ayyukansu. Yace sojojin Najeriya na da kwarewa kuma a baya sun samu nasara sosai akan tsageran dajin dan sun kwato wasu garuruwa dake hannun tsageran dajin. Yace abinda Najeriya ke bukata ba wai wata kasa ta shigo ta yaki 'yan ta'adda ba, tana neman hadin gwiwa ne ta hanyar bayanan sirri da makamai da sauran su musamman daga kasashe irin su Amur...