Tuesday, January 13
Shadow
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya je jihar Benue inda zai halarci daurin auren dan sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya je jihar Benue inda zai halarci daurin auren dan sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya je jihar Benue inda yake wakiltar shugaban kasar wajan daurin auren dan sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume. Za'a daura aurenne tsakanin Samuel Aondoakura da Deborah Ershim. Sakataren Gwamnatin tarayyar, George Akume da Gwamnan jihar Benue, Dr. Hyacinth Alia da sauransu ne suka tarbi shugaban kasar. Sanarwar ta fito ne daga bakin me magana da yawun mataimakin shugaban kasar, Stanley Nkwocha. https://twitter.com/stanleynkwocha_/status/2005293036863951309?t=RoKQyzd2KaV_tPhYXc4C1g&s=19 Hakan na zuwane kasa da sati daya bayan da shima sakataren Gwamnatin Tarayyar, George Akume ya auri matarnan me yawan auren manyan mutane watau Zainab wadda ta tabata auren gwamna, Sanata, Basaraken Yarbawa da Wani Balarabe dan gidan sarau...
Kalli Bidiyon: Mun roki Allah kuma ya amsa mana shiyasa Donald Trump ka kawo Khàry Najeriya>>Inji Bishop David Oyedepo

Kalli Bidiyon: Mun roki Allah kuma ya amsa mana shiyasa Donald Trump ka kawo Khàry Najeriya>>Inji Bishop David Oyedepo

Duk Labarai
Malamin Kirista, Bishop David Oyedepo ya bayyana cewa Kharin da kasar Amirka ta kawo Najeriya, Allah ne ya amsa addu'ar da suka dade suna yi. Ya bayyana cewa Kharin ya rushe shirin musuluntar da Najeriya da aka dade anayi. Yace kuma Najeriya ba zata taba zama kasar Musulmi ba. https://twitter.com/GeneralSnow_/status/2005289455553491192?t=D25rl84hDQWyykxOxgZKvQ&s=19
Ya dauki Hankula bayan da ya auri mata 2 a shekara daya

Ya dauki Hankula bayan da ya auri mata 2 a shekara daya

Duk Labarai
Wannan mutumin ya dauki hankula bayan da ya auri mata 2 a shekara 1. Ta farko ya aureta a watan Janairu inda kuma a watan Disamba ta haifa masa 'yan Biyu, yayin da ta biyun kuma sati daya da haihuwar matarsa ya aureta. Saidai mata da yawa na cewa bai wa uwar gidan adalci ba, saboda ya kara aure yayin da take jego. https://twitter.com/Nawas_masood/status/2004508575738073477?t=nX9rDTU-pI-BGJGJs71Bkg&s=19
Kalli Bidiyon yanda Fasto Chris Okafor ya durkusa a gaban mutanen cocinsa yana neman Afuwarsu inda yace zargin da Doris Ogala ta mai gaskiyane amma yana neman Afuwa

Kalli Bidiyon yanda Fasto Chris Okafor ya durkusa a gaban mutanen cocinsa yana neman Afuwarsu inda yace zargin da Doris Ogala ta mai gaskiyane amma yana neman Afuwa

Duk Labarai
Fasto Chris Okafor ya durkusa gwiwoyi biyu a kasa yana rokon mabiyan cocinsa su yafe masa kan dambarwar data faru tsakaninsa da Doris Ogala. Fasto Okafor yace yasan ya aikata kuskure amma yana rokon su yafe masa. Doris Ogala dai tace sun buga soyayya da Fasto Chris Okafor inda tace ya mata alkawarin zai aureta amma kwatsam sai ganinshi ta yi da wata za'a daura musu aure. Tace daga baya ya aikata mata kudi dala 10,000 dan kada ta tona masa asiri, saidai duk da haka bata fasa ba. https://twitter.com/NigeriaStories/status/2005231117558014427?t=N7Otu61ZCaM5aQFe-Mz0Zw&s=19
Kalli Bidiyon: Sojan Najeriya ya dauki hankula sosai bayan da yace kullun yana zuwa cire Naira dubu 7 a asusunsa na banki, yace sai me gadi ya tambayeshi me zai hana ya cire kudin duka ya huta?

Kalli Bidiyon: Sojan Najeriya ya dauki hankula sosai bayan da yace kullun yana zuwa cire Naira dubu 7 a asusunsa na banki, yace sai me gadi ya tambayeshi me zai hana ya cire kudin duka ya huta?

Duk Labarai
Wannan wani sojan Najeriya ne da mutane da yawa suka tausayawa rayuwarsa. Yace kullun yana zuwa ya cire Naira dubu 7 daga asusunsa na banki. Yace me gadi ya tambayeshi me zai hana ya cire kudin sa gaba daya ya huta? Sai yace masa lambar wayar mahaifiyarsa ce akan Asusun bankin, kuma duk sanda ya cire kudi daga asusun bankin tana jin alert. Ta hakane take gane cewa har yanzu yana raye bai mùtù ba. https://twitter.com/AsakyGRN/status/2005244588911452490?t=mW7jOcKEFiFLhwQEFjO51Q&s=19