Bidiyon wani Fasto na watsawa mabiyansa ruwan tsarki dan tsekakesu ya jawo cece-kuce.
A Bidiyon an ga yanda Faston ya dauko ruwan a cike da bokiti ya watsa akan mabiyansa.
Kiristoci da yawa sun ce ba haka ya kamata yayi ba, kamata yayi a yi abin a tsanaki.
Kalli Bidiyon anan
Shirin jam'iyyun Adawa na hadewa waje daya dan yin galaba akan jam'iyyar APC a zaben shekarar 2027 ya fara saun tangarda saboda komawa jam'iyyar APC me mulki da 'yan Adawa dayawa ke yi.
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne ke jagorantar wannan tafiya ta 'yan adawa.
Duk da kokawar da 'yan Najeriya ke yi na tsadar rayuwa amma jam'iyyar APC me mulki sai kara samun manyan 'yan Adawa take suna komawa cikin ta.
A baya dai an yi tsamanin Shugaba Tinubu da jam'iyyar APC zasu sha wahala wajan cin zabe Wanda su kansu 'yan Adawar abinda suka yi amfani dashi kenan wajv fara wannan tafiya tasu amma gashi lamarin na son dagule musu.
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnonin Jam'iyyar PDP sun kira wani taro na musamman da zai tattauna rikicin dake cikin jam'iyyar da yasa mutane ke ta fita daga cikinta.
Gwamnonin sun kira tsaffin Gwamnonin Jam'iyyar da tsaffin shuwagabannin majalisun tarayya da sauran masu ruwa da tsaki a jam'iyyar dan tattaunawa kan yanda za'a shawo kan wannan matsala.
Jam'iyyar PDP na fama da matsalar ficewar da yawa daga cikin membobinta zuwa jam'iyyar APC me mulki.
Na baya-bayannan sune komawar Gwamnan Jihar Delta,b Sheriff Oborevwori da Tsohon Gwamnan jihar kuma tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa, Ifeanyi Okowa zuwa jam'iyyar APC.
Hakanan duka sanatocin jihar Kebbi su 3 suma sun fice daga jam'iyyar PDP zuwa APC da sauransu.
Tsadar rayuwa tasa masu motocin Alfarma masu tsada ciki hadda sojoji da ma'aikatan banki da sauransu sun koma yin haya da motocin nasu dan samun sauki.
Tun da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta cire tallafin man fetur, tsadar rayuwa ta kara kazancewa a Najeriya.
An zanta da wasu daga cikin ma'aikatan Gwamnati da suka koma daukar fasinja dan samun saukin rayuwa.
Jaridar Punchng tace wakiliyarta a Legas ta zanta da wasu daga cikin masu irin wannan sana'ar.
Akwai soja akwai ma'aikatan banki akwai ma 'yan kasuwa da Sauransu wadanda jaridar ta zanta dasu inda suka bayyana cewa sukan dauki fasinjoji ne dan samun saukin musaman kudin Ma fetur, wasu kuma sun ce suna hakanne dan samun karin kudin da zasu kula da iyalinsu saboda albashi baya isarsu.
A baya da mun ga yanda...
Malamin Darika, Sheikh Ahmad Jarinkhauri ya bayyana cewa, Sheikh Tijjani ya taba tayar da matacce.
Ya bayyana hakane a wani wa'azinsa da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda abin ya baiwa mutane mamaki.
https://twitter.com/Ameenertu_/status/1921229379813646740?t=7NvtOl30NSQQDqSiq-Q9fw&s=19
Da yawa dai sun karyatashi.
Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike yace makaho ne kawai zai ce shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu baya kokari.
Wike ya bayyana hakane yayin da yake ran gadin wasu ayyukan da ake gudanarwa a Abuja.
Yace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kawo ayyuka masu kyau da inganci Abuja inda yace kowa ya shaida hakan. Abuja ta canja.
Ya karkare da cewa, Makaho ne kadai zai ce Tinubu bai yi kokari ba.
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false}
Wasu 'yan mata sun bayyana inda suke bayar da labarin yanda fastonsu ya dirka musu cikkunan shege.
Daya daga cikisu hadda kuka inda take cewa yayi amfani da ita ya yadda ta.
https://twitter.com/ChuksEricE/status/1921285781336768975?t=xDvA9rkk_pR8tdhOvXOFCw&s=19
Lamarin dai ya baiwa mutane mamaki.
Rahotanni sun bayyana cewa, 'yan Bindiga a jihar Zamfara sun kai hari unguwar Galadanci a garin Anka kusa da fadar sarkin garin inda suka yi garkuwa da mutane 9 duka mata.
Rahoton yace kusan kullun sai an kai irin wannan harin garin.
YANZU-YANZU: El-Rufai da Peter Obi Sun Tattauna a Gefen Taron Cambridge Africa Together a Birtaniya.
An hango tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, na tattaunawa da ɗan takarar Shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Mista Peter Obi, a gefen taron shekara-shekara karo na 11 na Cambridge Africa Together Conference (ATC), wanda ke gudana a Jami’ar Cambridge, ƙasar Birtaniya.
Taron, wanda ke ɗaya daga cikin manyan taruka da ke haɗa shugabanni, masana da matasa daga sassa daban-daban na nahiyar Afirka da duniya, ya kasance dandali na musayar ra’ayoyi, tattaunawa kan ci gaban Afirka, shugabanci da sabbin dabaru na magance matsalolin da ke fuskantar nahiyar.
El-Rufai da Peter Obi, wadanda dukkansu sanannu ne a harkar siyasar Najeriya, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen ...