Thursday, March 12
Shadow
Gobarar Amurka: Yayin da suke tsaka da fama da mahaukaciyar gobara an kuma samun girgizar kasar a California ta kasar Amurka

Gobarar Amurka: Yayin da suke tsaka da fama da mahaukaciyar gobara an kuma samun girgizar kasar a California ta kasar Amurka

Duk Labarai
Girgizar kasa me maki 3.7 ta auku a jihar California ta kasar Amurka yayin da jihar ke kan fama da matsalar mahaukaciyar gobara data kone gidaje sama da dubu 10. Girgizar kasar ta farun da safiyar ranar Juma'a a San Francisco Bay kuma sama da mutane dubu biyar sun ce sun ji wannan girgizar kasa. Girgizar ta farune a garin dake da nisan mil 350 da garin Loas Angeles. A kalla mutane 16 ne hukumomi suka tabbatar sun mutu gobarar Los Angeles.
Talauci alamace ta yawan zunubi da rashin tsoron Allah>>Inji Pasto Komayya

Talauci alamace ta yawan zunubi da rashin tsoron Allah>>Inji Pasto Komayya

Duk Labarai
Pastor Korede Komaiya ya bayyana cewa, talauci alamace ta rashin tsoron Allah da yawan zunubi. Faston ya bayyana hakane ga mabiyansa a cikin cocinsa. Yace a rubuce yake cewa, wadanda suka bi Allah, zasu samu rayuwa ta jin dadi. Dan haka yace talauci alamace ta rashin tsoron Allah da yawan zunubi. Bidiyon da yake wannan magana ya yadu sosai a kafafen sda zumunta inda akai ta masa raddi. Yace yawanci ba'a sanin ainahin halin mutum sai idan ya samu kudi. Ya kara da cewa, yawanci talakawan da zaka ga suna kankan da kai, dama ce basu samu ba.
Obasanjo da Yakubu Gowon sun goyi bayan kungiyar su shekarau dake son kwace mulki daga hannun Tinubu  shekarar 2027

Obasanjo da Yakubu Gowon sun goyi bayan kungiyar su shekarau dake son kwace mulki daga hannun Tinubu shekarar 2027

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar su tsohon Gwamnan Kano kuma sanata Ibrahim Shekaru me suna LND dake son rikidewa zuwa ta siyasa, ta samu goyon bayan tsaffin shuwagabannin Najeriya, Yakubu Gowon da Olusegun Obasanjo. Kungiyar dai na ci gaba da tuntubar manyan 'yan siyasa dga yankunan Kudu maso yamma da kudu maso kudu da kudu maso gabas dan cimma burinta. Shugaban kungiyar, Dr Umar Ardo ya tabbatar da komawarta ta siyasa dan samar da Jam'iyya me karfi da hadin kai da zata karade kowane yanki a kasarnan. Duka shuwagabannin biyu, Yakubu Gowon da Olusegun Obasanjo sun yi na'am da wannan tafiya inda suka bayar da shawarar mayar da ita ta kasa baki daya.
A karin farko, Shugaba Tinubu ya sakawa dokar haramtawa sojojin Najariya yin Luwadi, Madigo da shan giya

A karin farko, Shugaba Tinubu ya sakawa dokar haramtawa sojojin Najariya yin Luwadi, Madigo da shan giya

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa dokar haramta yin luwadi, Madigo da daudu ko saka kayan mata, da yin zane a jiki wanda aka fi sani da Tattoo a gidan soja. Hakanan kuma dokar ta haramtawa sojojin huda jikinsu, irin su hudar kunne ko hanci da sauransu, sannan ba'a yadda soja ya sha giya a bakin aiki ko kuma ko da baya bakin aiki. Wannan na kunshene a cikin sabuwar dokar aikin soja da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanyawa hannu a watan Disamba na shekarar 2024. Hakanan sabuwar dokar ta haramtawa sojojin shiga kungiyar asiri ko kuma harkar siyasa.
Gwanin Ban Tausai: Ji yanda kananan ‘yan matan da aka yi gàrkùwà dasu aka sakosu suka koma yin karuwanci saboda ‘yan Bìndìgàr sun saba musu da làlàtà

Gwanin Ban Tausai: Ji yanda kananan ‘yan matan da aka yi gàrkùwà dasu aka sakosu suka koma yin karuwanci saboda ‘yan Bìndìgàr sun saba musu da làlàtà

Duk Labarai
Lawan Wakilbe, kwamishinan ilimi, da kimiyya da fasaha, da kirkire-kirkire a Jihar Borno, ya yi gargadi kan yawaitar karuwanci tsakanin tsofaffin wadanda kungiyar B0k0 Hàràm ta sace. TheCable ta rawaito cewa Kwamishinan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar ban girma da Hamsatu Allamin, shugabar cibiyar Allamin Foundation for Peace, ta kai masa a jiya Juma’a a Maiduguri. Wakilbe ya ce an fi samun irin waɗannan matsalolin a ƙananan hukumomin Bama, Banki, da Gwoza. Ya kara da cewa wasu daga cikin wadanda Boko Haram din su ka saki na fuskantar cin zarafi ta hanyar lalata da su saboda sun fuskanci hakan tun a lokacin da raunin da su ke hannun ƴan ta’addan. Ya yi kira ga haɗa hannu waje ɗaya domin ceto ire-iren yaran.
Na kwashe shekaru ashirin ina fim a Amurka amma har yanzu a talauce na ke – Djimon Hounsou

Na kwashe shekaru ashirin ina fim a Amurka amma har yanzu a talauce na ke – Djimon Hounsou

Duk Labarai
Shahararren jarumin Hollywood din nan Djimon Hounsou ya bayyana cewa ya na ci gaba da fuskantar matsin tattalin arziki duk da sana'ar fim da ya ke yi sama da shekaru ashirin. A wata hira da CNN a wani shirin su na matasan Afirka, a yau Asabar, Hounsou ya bayyana cewa ya na ganin cewa ana yi masa ƙwange a albashi kuma har yanzu ya na fama da talauci. "Har yanzu ina fama yanayi a rayuwa. Na kasance cikin harkar shirya fina-finai sama da shekaru ashirin, tare da lashe lambobin girma na Oscar guda biyu da fina-finai da yawa, amma duk da haka, har yanzu ina fama da rashin kuɗi. Babu shakka ƙwangen albashi ake yi min," inji shi. Wannan tonon silili ya ba wa mutane da yawa mamaki, ganin irin nasarorin da ya samu, gami da lashe lambar yabo ta Academy sakamakon kwazon saba fim din 'Blood D...
Kamfanin mai na kasa, NNPCL ya karkatar da makudan kudade Naira Tiriliyan N2.68tn, da dala Miliyan $9.77m kuma an gayyaceshi dan a yi bincike yaki zuwa

Kamfanin mai na kasa, NNPCL ya karkatar da makudan kudade Naira Tiriliyan N2.68tn, da dala Miliyan $9.77m kuma an gayyaceshi dan a yi bincike yaki zuwa

Duk Labarai
A ci gaba da zargin karkatar da kudaden kasa da suka saka Najeriya cikin halin kaka nikayi, ana zargin kamfanin mai na kasa, NNPCL da karkatar da Naira Tiriliyan N2.68tn, da dala Miliyan $9.77m a cikin shekaru 4 da suka gabata. Babban me binciken hada-hadar kudi na kasa ne yayi wannan zargi bayan kammala bincike akan yanda kamfanin na NNPCL ya gudanar da ayyukansa. Tuni babban me binciken na kasa ya aikewa da majalisar tarayya da sakamakon bincikensa inda yace abinda kamfanin man na kasa, NNPCL ya aikata ya sabawa dokar kasa data haramta karkatar da kudaden kasa. Duk da wadannan zarge-zargen, kamfanin man na kasa, NNPCL har yanzu yaki ya yi magana ko ya bayar da amsa akan zarge3da ake masa.
Duk da ciyo bashin Dala Biliyan $3.2 Najeriya ta kasa samar da ingantacciyar wutar Lantarki

Duk da ciyo bashin Dala Biliyan $3.2 Najeriya ta kasa samar da ingantacciyar wutar Lantarki

Duk Labarai
A cikin shekaru 4 da suka gabata, Najeriya ta ciyo bashin Dala Biliyan $3.2 dan gyaran wutar lantarki amma duk da haka ta kasa samar da wutar me karfin da yafi 4,500mgwt da zata wadatar da mutanen kasar. Bankin Afrika da Bankin Duniya da Bankin Japan ne suka baiwa Najeriya wadannan kudade. Saidai duk da wadannan makuda kudade babu alamar canji kan matsalar wutar. Har yanzu dai wuta me karfin Megawatts 4,743MW ne Najeriya ke samarwa wanda tun shekaru 3 da suka gabata haka lamarin yake bai canja ba. A shekarar 2024, sau 12 tashoshin wutar lantarkin Najeriya na samun matsala.