Friday, April 24
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon: Aure nake so kuma wallahi ba da wasa nake ba, duk me sona da gaske yamin magana>>Inji Fatima

Kalli Bidiyon: Aure nake so kuma wallahi ba da wasa nake ba, duk me sona da gaske yamin magana>>Inji Fatima

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok me suna Fatima ta bayyana cewa aure take son yi. Ta bayyana hakane a shafinta ta Tiktok a Bidiyon guda biyu data yi inda a na farko tace aure take so. Daga baya kuma ta sake fitowa ta jaddada bukatarta. Tace duk me sonta ya mata DM, inda ta kara da cewa, a garin Kaduna take. https://www.tiktok.com/@khadeejamuhammed8/video/7627679047144705300?_r=1&_t=ZS-95TIWzXn8fQ
DSS na binciken hadiman Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf guda 5 saboda zargin batawa Kwankwaso suna

DSS na binciken hadiman Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf guda 5 saboda zargin batawa Kwankwaso suna

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan farin kaya ta DSS na binciken Hadiman gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf su 5 bayan korafin da tsohon Gwamnan jihar, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya shigar inda yake zarginsu da bata masa suna. Wadanda aka kama din sune me taimakawa Gwamna Abba ta bangaren kafafen sadarwa, Sanusi Bature, Dawakin Tofa, da shugaban matasa na APC, Salisu Yahya Hotoro, sai Ibrahim Adam wanda shine ke baiwa Gwamna Abba Shawara kan yada labarai sannan tsohon Hadimin Kwankwaso ne, Sai Nuhu Dambazau da Mukhtar S. Yahuza. Rahoton yace dukansu da kansu suka kai kansu ofishin DSS bayan gayyatar da aka musu. Kwankwaso ne da kansa ya sakawa takardar korafin hannu inda ya zargesu da ci masa mutunci da bata masa suna a kafafen sada zumunta.
Bayan da aka shafe kwana da kwanaki ana neman matar auren nan, a karshe dai an iske ta a dakin Otal ita da Qartonta suna shakatawa

Bayan da aka shafe kwana da kwanaki ana neman matar auren nan, a karshe dai an iske ta a dakin Otal ita da Qartonta suna shakatawa

Duk Labarai
Wata matar aure me suna Mrs Tilewa Olatunde Funke 'yar kimanin shekaru 42 ta bace ana ta nemanta. Lamarin ya farune a garin Ilara-Mokin na jihar Ondo. Saidai da bincike ya tsananta, 'yan sanda sun ganota a dakin otal da wani me suna Isa Alaba dan kimanin shekaru 55 a dakin otal suna shakatawa. Hukumar 'Yansandan ta bayyana cewa matar da kanta ta kai kanta wajan mutumin ba garkuwa yayi da ita ba kuma an warware matsalar cikin ruwan sanyi. Hukumar 'Yansandan ta yi kira ga mutane dasu daina yada labaran da basu inganta ba kan lamarin.
Da Duminsa: Sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda wani babban mutum shima ya maka su David Mark da Aregbesola a kotu yace ba halastattun shugabannin jam’iyyar bane

Da Duminsa: Sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda wani babban mutum shima ya maka su David Mark da Aregbesola a kotu yace ba halastattun shugabannin jam’iyyar bane

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai, Leke Abejide wanda dan jam'iyyar ADC ne ya maka shuwagabannin jam'iyyar na riko David Mark, da Rauf Aregbesola a kotu inda yace kotu ta saukesu. Hakan na zuwane a yayin da ake tsaka da fama da rikicin Nafiu Bala. Ya shigar da karar ne a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja inda kotun ta tsayar da ranar 13 ga watan Afrilu dan yanke hukunci. Jam'iyyar ADC na fuskantar kalubale kala-kala inda take zargin hannun APC a lamarin.
Haduwata ta farko da Atiku ya bani kyautar Naira Miliyan 20>>Inji Fati Muhammad

Haduwata ta farko da Atiku ya bani kyautar Naira Miliyan 20>>Inji Fati Muhammad

Duk Labarai
Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Muhammad ta bayyana cewa, ta hadu da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar kuma ya bata kyautar Naira Miliyan 20. Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita, wadda Ali Jita ya jagoranta. Saidai tace kudin bata yi wani abun azo a gani dasu ba yawanci mutane ta rika saiwa kyautuka. https://www.tiktok.com/@amanardondaalbishir/video/7626912177827400981?_r=1&_t=ZS-95RhhfRixJB
Ji Sautin Murya: Tinubu ba kudi ya bani na masa yakin neman zabe ba, tunda na sanshi ba ko ruwan Fiya wata bai taba bani kudi na siya ba>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Ji Sautin Murya: Tinubu ba kudi ya bani na masa yakin neman zabe ba, tunda na sanshi ba ko ruwan Fiya wata bai taba bani kudi na siya ba>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ba kudi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bashi ya masa yakin neman zabe ba. Yace shi tunda yasan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bai taba bashi ko sisi ba ko da kudin siyen Pure Water. Yace amma ba zai iya rantsuwa akan sauran wadanda sukawa Tinubu yakin neman zabe ba amma shi dai ba'a bashi ko sisi ba. https://twitter.com/i/status/2042551635289739358
INEC ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC

INEC ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Lauyan David Mark, Realwan Okpanachi ya tabbatar da cewa a takardar rantsuwa da hukumar zabe me zaman kanta, INEC ta gabatarwa da kotu. Ta tabbatar da cewa, David Mark ne halastaccen shugaban jam'iyyar ADC hakanan Rauf Aregbesola shine halastaccen sakataren jam'iyyar. Ya bayyana hakane ga manema labarai bayan zaman kotun. A yanzu dai kotu ce za'a jira ta yanke hukunci kan karar. https://twitter.com/i/status/2042698761843912756