Sunday, January 11
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon abinda Gwamnan Bauchi yawa shugaban karamar hukuma da ya zauna kujera daya da sarkin Bauchi

Kalli Bidiyon abinda Gwamnan Bauchi yawa shugaban karamar hukuma da ya zauna kujera daya da sarkin Bauchi

Duk Labarai
A wani Bidiyo da yake yawo a kafafen sada sumunta, An ga Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Muhammad ya cewa wani da ya zauna a kusa da Me Martaba Sarkin Bauchi ya tashi. Gwamnan ya cewa wanda ya zauna din me zai sa ya zauna kujera daya da Sarkin Bauchi? Yacewa Sarkin yana wasa da kujerar Sarauta. https://twitter.com/i/status/2007746894899138776 Gwamnan ya fadi maganar cikin tsawa. Wasu dai sun ce Gwamnan bai kyautawa mutumin ba inda wasu ke bayyana cewa, shugaban karamar hukuma ne.
Bankunan Najeriya sun rufe rassa 229 saboda mutane sun rage zuwa

Bankunan Najeriya sun rufe rassa 229 saboda mutane sun rage zuwa

Duk Labarai
Wani Rahoto da babban bankin Najeriya, CBN ya fitar yace, Bankukan Najeriya sun rufe rassa 229 a fadin kasar saboda raguwar yawan mutanen dake zuwa bankunan. Rahotan yace yawanci mutane na zuwa POS ne dan cirewa ko saka kudi maimakon su shiga Banki. Rahoton ya kara da cewa, an saka kudi sau 5,373 a shekarar 2023 inda a shekarar 2024 kuma aka saka kudi sau 5,144 wanda hakan ke nuna cewa yawan kudaden da ake sakawa a Bankuna sun ragu.
Kalli Bidiyon: Abinda Musbahu M. Ahmad yayi akan komawar Abba APC da mutane ke ta cewa ashe hankalinsa kadanne

Kalli Bidiyon: Abinda Musbahu M. Ahmad yayi akan komawar Abba APC da mutane ke ta cewa ashe hankalinsa kadanne

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Musbahu M. Ahmad ya bayyana a wani bidiyo yana ihu yana fadar cewa Gwamnatin Kano zata yi jifar Gafiyar Baidu saboda komawar Gwamna Abba jam'iyyar APC. Saidai wannan abu da yayi, ya dauki hankulan mutane inda wasu ke cewa, hakan bai kamata ba. Wasu sun rika bayyana cewa, da sun dauki Musbahu me hankali amma yanzu ya fadi ba nauyi a wajansu. https://www.tiktok.com/@misbahumahmad/video/7591184674844675348?_t=ZS-92mvgyQjbRh&_r=1
Kalli Bidiyon: Kudi ne Biliyan 1 aka baiwa Sheikh Khalifa Sani Zaria akan ayi Tsàfy dan Jhuyin mulkin da aka shirya yiwa shugaba Tinubu yayi nasara,Shiyasa aka kamashi>>Inji Sheikh Lawal Triumph

Kalli Bidiyon: Kudi ne Biliyan 1 aka baiwa Sheikh Khalifa Sani Zaria akan ayi Tsàfy dan Jhuyin mulkin da aka shirya yiwa shugaba Tinubu yayi nasara,Shiyasa aka kamashi>>Inji Sheikh Lawal Triumph

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Lawal Triumph ya bayyana cewa Biliyan 1 ce aka baiwa Sheikh Khalifa Sani Zaria akan ayi tsafi dan a yi nasarar yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki. Yace dalili kenan da yasa aka kamashi. Malam yace yasan da hakane ta hanyar kiran waya jihar Abinda ya faru, watau, Kaduna inda aka bashi wannan labari. Duk da yake malam bai bayyana sunan malamin da yake nufi ba, da yawa sun fassara cewa, da malam Sheikh Khalifa Sani Zaria yake. Yace irin wannan abinne ba za'a taba ganin dan Izala a ciki ba. https://www.tiktok.com/@sobman_fans_pantami/video/7591237341218442514?_t=ZS-92mrwD8jpNh&_r=1
Allah Sarki: A yau, Lahadi ne za’a yi jana’izar Abokan Dan Damben, Anthony Joshua su 2 a masallacin Birnin Landan

Allah Sarki: A yau, Lahadi ne za’a yi jana’izar Abokan Dan Damben, Anthony Joshua su 2 a masallacin Birnin Landan

Duk Labarai
Rahotanni sun ce a yau Lahadi, 4, ga watan Janairu na shakerar 2026 ne za'a yi jana'izar abokan dan Damben Najeriya, Anthony Joshua 2 da suka rasu a hadarin mota da ya rutsa dasu a Najeriya. Za'a yi jana'izar ne a masallacin Landan. Hakan zai baiwa 'yan Uwa da abokan arziki damar halartar sallar Jana'izar tasu a yau. Rahotanni sun ce Anthony Joshua ya koma Landan din.
Kada ADC su yadda Kwankwaso ya koma cikinsu, Ina zargin Tinubu zaiwa aiki>>Inji Chinonso Charles

Kada ADC su yadda Kwankwaso ya koma cikinsu, Ina zargin Tinubu zaiwa aiki>>Inji Chinonso Charles

Duk Labarai
Wani Inyamuri me suna Chinonso ya yi kira ga jam'iyyar ADC cewa, kada su amince da Dr. Rabiu Musa Kwankwaso inda yace yana zargin zai je jam'iyyar ne dan yawa Tinubu aiki. Ya bayyana cewa shi ko fadan Kwankwaso da Abba yana ganin shiri ne kawai. https://twitter.com/i/status/2007561248528052420 Jaridar Thisday tace ana tattaunawa tsakanin Kwankwaso da jam'iyyar ADC inda yake shirin komawa can yayin da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ke shirin komawa APC. Hakanan shima a jawabinsa, Kwankwaso yace akwai jam'iyyar da suke tattaunawa da ita yake son komawa amma kuma yana son a bashi takarar shugaban kasa ko ta mataimakin shugaban kasa. j