Saturday, February 14
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon da gidan Talabijin din Channels TV suka yi inda suka nuna Mabarata da yawa a titunan Kano, wanda ya jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon da gidan Talabijin din Channels TV suka yi inda suka nuna Mabarata da yawa a titunan Kano, wanda ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
Sabon rahoton da gidan Talabijin din Channels TV suka yi akan Al'adar bara a titunan Kano ya jawo cece-kuce. Da yawa sun bayyana cewa, ko sati ba'a yi ba aka ga matasan Kano na rokon shahararren dan Amurka, Ishowspeed da ya je Legas kuka Duniya ta gansu. Da yawa sun ce amma Channel TV bata yi rahoto akan su ba ahine take nuna Mabarata a kano. https://twitter.com/i/status/2015076409408995360 Rahoton dai bai yiwa mutane da yawa dadi ba inda wasu ke cewa, Channels TV din kamar tana ramuwa ne game da Bidiyon matasan da aka ga suna rokon Ishowspeed kudi.
Ganin dan gidan Ministan babban birnin tarayya, Abuja Joaquin Wike sanye da takalmin Naira Miliyan N3,705, 000 ya dauki hankula sosai

Ganin dan gidan Ministan babban birnin tarayya, Abuja Joaquin Wike sanye da takalmin Naira Miliyan N3,705, 000 ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Rayukan 'yan Najeriya ya baci sosai ana ta cece-kuce bayan ganin dan gidan Ministan babban birnin tarayya Abuja, Joaquin Wike sanye da takalmin da aka yi kiyasin kudinsa sun kai Dala $2,370, watau kwatankwacin sama da Naira N3,705, 000. Ya saka takalmin ne a wajan bikin kammala karatun da yayi daga Kings College dake Birnin Landan na kasar Ingila. Da yawa dai na tambayar inda dalibi wanda yanzu ne ya kammala karatu baya aikin komai dan shekaru 25 ya samu kudin sayen takalmin Naira Miliyan 3? https://twitter.com/i/status/2015035207745769884
Kalli Bidiyon: Bazan ci Amana ba, kuma ba zan bi Butulu ba, Na ajiye aiki na koma bangaren Kwankwaso>>Inji me baiwa a Gwamnan Kano shawara kan harkar siyasa

Kalli Bidiyon: Bazan ci Amana ba, kuma ba zan bi Butulu ba, Na ajiye aiki na koma bangaren Kwankwaso>>Inji me baiwa a Gwamnan Kano shawara kan harkar siyasa

Duk Labarai
Me baiwa gwamnan Kano shawara akan harkar siyasa, Sanusi Sirajo Kwankwaso ya bayyana cewa, ya ajiye aikinsa. Ya bayyana cewa ya ajiye ne dalilin fitar da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi daga jam'iyyar NNPP yana shirin komawa APC. Yace shi ba zai ci amana ba kuma ba zai bi Butulu ba. Yace ya kai takardar ajiye aikin an ki karba shine yace bari ya fito kafar sada zumunta ya sanar da ajiye aikin nasa. https://twitter.com/i/status/2014830525203050720
Bankin First Bank ya yi kuskuren Tura masa Naira Biliyan 1.5, saidai maimakon ya mayarwa da bankin, yayi wadaka da kudin

Bankin First Bank ya yi kuskuren Tura masa Naira Biliyan 1.5, saidai maimakon ya mayarwa da bankin, yayi wadaka da kudin

Duk Labarai
Wannan mutumin sunansa Ojo Eghosa Kingsley dan jihar Edo. Kuma a watan Yuni na shekarar 2026 bankin First Bank sun tura masa Naira Biliyan 1.5 a matsayin kuskure. Saidai maimakon ya mayarwa da bankin kudin, ya yi ta wadaka dasu inda ya rabasu zuwa asusun ajiyar bankin Mahaifiyarsa dana kanwarsa. Da aka kamashi, EFCC ta kwace 1.1 Bidiyon daga hannunsa inda ya zama saura Naira Miliyan 272 wadda kotu ta ce ya biya bankin. Saidai rahotanni sun bayyana cewa, ya ce ya zabi zama a gidan yari maimakon ya mayarwa da bankin kudin.
Kalli Bidiyon: Yawancin Mu Zawarawa ba mutanen Arziki bane, abinda muka saba dashi a gidan Mijin mu bama iya hakura idan auren mu ya mutu sai mun yi>>Inji Wannan Bazawarar

Kalli Bidiyon: Yawancin Mu Zawarawa ba mutanen Arziki bane, abinda muka saba dashi a gidan Mijin mu bama iya hakura idan auren mu ya mutu sai mun yi>>Inji Wannan Bazawarar

Duk Labarai
Wannan wata Bazawara ce data bayyana cewa, matan aure su daina sha'awar rayuwar zawarci. Tace yawanci zawarawa basa iya hakura da mu'amalar da mijin su ke musu kamin aurensu ya mutu, ko da aurensu ya mutu suna ci gaba da bin maza. https://www.tiktok.com/@najaatu228/video/7597429080467754260?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7597429080467754260&source=h5_m&timestamp=1769261707&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7568740291232040721&share_link_id=5059b349-729d-439b-a169-fd837891...
Kalli Bidiyon: Budurwarka idan kana son Mallaketa kada wani ya kwace ta to ka rika bata kyautar akalla Naira Dubu 10 duk sati>>Inji malam Abdulrahman Umar Sautussunnah

Kalli Bidiyon: Budurwarka idan kana son Mallaketa kada wani ya kwace ta to ka rika bata kyautar akalla Naira Dubu 10 duk sati>>Inji malam Abdulrahman Umar Sautussunnah

Duk Labarai
Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah ya baiwa matasa shawarar cewa idan suna son mallake zuciyar 'yan matansu, sai sun hada da yin kyauta. Ya bayyana cewa, akalla, idan kana son ka mallake Zuciyar budurwar ka to ka rika mata kyautar Naira Dubu 10 duk sati, ko kuma kyautar Naira dubu 5 duk sati idan baka da karfi. https://www.tiktok.com/@abdurrahmanumarr/video/7598266443578346772?_r=1&_t=ZS-93L1vpv8sld Yace idan kuwa baka yi, za'a samu wani da zai rika mata kyauta ta maka kwace.
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: An gano wata mùmmùnàr aika-aika da Umar Yayi kamin wadda yawa Matar aure da ‘ya’yanta

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: An gano wata mùmmùnàr aika-aika da Umar Yayi kamin wadda yawa Matar aure da ‘ya’yanta

Duk Labarai
A yayin da akw ta jimami da Alhinin Abinda Umar yawa matar aure da 'ya'yanta, wani ya fito ya bayyana wasu abubuwa da Umar ya aikata a baya. Ya bayyana cewa, dama can Umar ba mutumin kirki bane, a danginsu dama ba sonsa ake ba saboda halayensa marasa kyau. Ya bayyana cewa Umar ya taba zakewa kanwarsa, ya chyre mata Ido sannan yayi sanadiyyar rabata da Duniya Sannan yace an rufe abinne aka barshi tsakanin dangi ba'a gayawa Kowa ba dan a rufa asiri. https://www.tiktok.com/@mmgfishferming/video/7598586443207953671?_r=1&_t=ZS-93Kz4TSaWw5
Rashida Mai Sa’a ta jawo cece-kuce bayan cewa duk me sukar dan makullin da take sayarwa matan aure dake hana mazansu neman mata a waje Màzìnàchìnè

Rashida Mai Sa’a ta jawo cece-kuce bayan cewa duk me sukar dan makullin da take sayarwa matan aure dake hana mazansu neman mata a waje Màzìnàchìnè

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Rashida Mai Sa'a Ta dauki hankula sosai bayan da ta bayyana cewa masu sukar dan makullin da take sayarwa matan aure dake hana mazansu neman mata a waje mazinata ne. Rashida ta samu Raddi daga masu fadakarwa a kafafen sada zumunta irin su Baffa Hotoro da Dr. Hussain Kano inda suka bayyana abinda take yi da cewa shirkane. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7598550126881230091?_r=1&_t=ZS-93KuwLDRdVQ https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7597922764925783352?_r=1&_t=ZS-93KxHaK0AID