Tuesday, January 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Sarauta Sai Arewa: Bidiyon wani basaraken Kudu sanye da sarkar Gwal yana rawa da ‘yanmata ya dauki hankula

Sarauta Sai Arewa: Bidiyon wani basaraken Kudu sanye da sarkar Gwal yana rawa da ‘yanmata ya dauki hankula

Duk Labarai
An ga Bidiyon wani basaraken Yarbawa sanye da sarkar Gwal yana rawa tare da wasu mata. Bidiyon ya jawo muhawara da yawa inda wasu ke cewa, bai kamata a matsayinsa na basarake hakan bai dace ba. Wasu kuma na tambayar ina ya samu kudin sayen Sarkar Gwal. https://twitter.com/1RitaSunshine/status/2005549299430752395?t=gF5Tucd-GJy750yqYWeidQ&s=19
Wata Sabuwa: An gano cewa Naira Biliyan 200 da EFCC ke zargin Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami da sacewa, ya samesu ne daga Bashin Manoma da CBN suka bayar Lokacin Buhari, da Kudaden Abacha da aka dawo dasu da kuma Paris Club

Wata Sabuwa: An gano cewa Naira Biliyan 200 da EFCC ke zargin Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami da sacewa, ya samesu ne daga Bashin Manoma da CBN suka bayar Lokacin Buhari, da Kudaden Abacha da aka dawo dasu da kuma Paris Club

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Naira Biliyan 200 da EFCC ke zargin Tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami da sacewa, ya samesu ne daga kudaden bashin da babban bankin Najeriya, CBN ya baiwa manoma bashi lokacin Buhari. Da kuma kudin Abacaha da aka dawo dasu Najeriya da kuma kudin Paris Club watau bashin da Gwamnatin Tarayya da gwamnoni suka ciwo. Kafar The Cable tace ta samu cewa Abubakar Malami ya sa matarsa me suna Hajiya Bashir Asabe ta ci bashin na manoma har Naira Biliyan 4 wanda kuma bata biya ba. A yanzu dai EFCC sun sakata cikin wadanda za'a gurfanar dasu a gaban kotun tare, a baya dai Hutudole ya kawo muku cewa akwai dan Abubakar Malami da shima yanzu EFCC ke tuhuma. A bangaren Kudaden Abacha da aka karbo, lauyoyi turawa aka dauka suka yi aiki, amma rahotan yace Abubaka...
Shugaban kasa Bola Tinubu ya yafewa kamfanin mai na kasa, NNPCL bashin dala Biliyan $1.42 da Naira Tiriliyan 5.57 daya kamata su biya Gwamnatin Tarayya

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yafewa kamfanin mai na kasa, NNPCL bashin dala Biliyan $1.42 da Naira Tiriliyan 5.57 daya kamata su biya Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yafewa Kamfanin mai na kasa, NNPCL bashin dala Biliyan $1.42 da Naira Tiriliyan 5.57 da ya kamata NNPCL din su biya a asusun Gwamnatin tarayya. Hakan na kunshene a cikin bayanan da hukumar kula da man fetur ta kasa, Nigerian Upstream Petroleum Regulatory Commission suka futar. Rahoton yace fadar shugaban kasa ta bayar da umarnin yafe bashin da kuma gogeshi daga cikin takardun da aka rubutashi.
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda wannan Inyamurar Musulma ke kokawa da irin abinda Inyamurai Kiristoci ke mata

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda wannan Inyamurar Musulma ke kokawa da irin abinda Inyamurai Kiristoci ke mata

Duk Labarai
Wannan wata inyamura musulma ce da a dauki hankula a kafafen sadarwa saboda abinda tace Inyamurai Kiristoci na mata. Ta bayana cewa, suna mata Bhàràzànà inda tace da tana kawar da kai ama abin sai karuwa yake. Ta bayyana cewa tana a garin Nsukka ne kuma garinsu akwai zaman lafiya amma wasu na son kawo matsala. Tace kiristanci bai koya abinda Kiristocin ke mata ba dan haka bata san inda suka samo irin abinda suke mata ba. Tace kuma me ya shafesu da addinin da take yi? Da yawa dai sun yi kira ga hukumomi da su dauki matakan da suka dace dan baiwa wannan matashiya kariya kada wani abu ya sameta. https://twitter.com/muslimnews_NG/status/2005394522042425410?t=7dOqfLtTUE8YtGbNytmUcQ&s=19
Wannan Bidiyon na Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma Wakili tana Rawa tare da Rùngùmàr wani ya dauki hankula

Wannan Bidiyon na Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma Wakili tana Rawa tare da Rùngùmàr wani ya dauki hankula

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma Wakili ta dauki hankula bayan da aka ganta tana rawa tare da rungumar wani a Bidiyo. Wasu dai sun rika cewa danta ne inda wasu ke cewa kaninta ne saboda yanda suka yi kama dashi. Bidiyon ya jawo muhawara sosai. https://www.tiktok.com/@asmee.wakili286/video/7588808148765658389?_t=ZS-92cX8MbQt85&_r=1
Sowore Wanda Kirista ne yace bai yadda da ikirarin shugaban kasar Amurka, Donald Trump ba na cewa yana son ceton Kiristocin Najeriya ba

Sowore Wanda Kirista ne yace bai yadda da ikirarin shugaban kasar Amurka, Donald Trump ba na cewa yana son ceton Kiristocin Najeriya ba

Duk Labarai
Mawallafin Jaridar Sahara reporters kuma dan fafutuka, Omoyele Sowore ya bayyana cewa, bai yadda da ikirarin shugaban kasar Amurka, Donald Trump ba na cewa, wai yana son ceton Kiristocin Najeriya ba. Yace ta yaya Trump zai ce yana son ceton Kiristocin Najeriya amma ya hanasu shiga kasar Amurka? Shugaba Donald Trump dai ya saka tsatstsauran mataki kan 'yan Najeriya dake son shiga kasar Amurka ba tare da banbance musulmi ko Kirista ba. https://twitter.com/sowore/status/2005397646861607248?t=QYuZlJd_H9UzyTcFGdQJ8g&s=19
Kalli Bidiyon yanda Cristiano Ronaldo ya ce Insha Allah zai cimma burinsa

Kalli Bidiyon yanda Cristiano Ronaldo ya ce Insha Allah zai cimma burinsa

Duk Labarai
Cristiano Ronaldo ya lashe gasar gwarzon dan kwallo na gabas ta tsakiya sau 3 a jere. A wajan taron bada kyautar da aka bashi, a cikin jawabinsa, yace insha Allahu zai cimma burinsa. Fadar wannan kalma tasa mutane da yawa, musamman Musulmai jin dadin hakan da fatan cewa Allah yasa wataran ya karbi kalmar Shahada. https://twitter.com/utdnarmi/status/2005358913739485656?t=fgdm3zKLWW8YzOOAStk1yQ&s=19
Da Duminsa: Rashin Lafiyace tasa Shugaba Tinubu ya tafi Turai>>Inji Sowore

Da Duminsa: Rashin Lafiyace tasa Shugaba Tinubu ya tafi Turai>>Inji Sowore

Duk Labarai
Mawallafin jaridar Sahara reporters, Omoyele Sowore yayi zargin cewa, Rashin Lafiya ce tasa aka fitar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zuwa Turai. Hakanan yayi zargin cewa, kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio shima bashi da lafiya. Yace bai kamata ace su rika tatsar kudin Najeriya ba suna kula da lafiyarsu. https://twitter.com/sowore/status/2005368009347461144?t=yby3RtkrB5QOTgwPfMZCiA&s=19
Gwamna Abba Kabir Yusuf zai koma jam’iyyar APC ba tare da Kwankwaso ba

Gwamna Abba Kabir Yusuf zai koma jam’iyyar APC ba tare da Kwankwaso ba

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf na shirin komawa jam'iyyar APC. Hakan ya fito ne daga jaridar Daily Nigerian. Jaridar tace ana tsammanin Abba zai koma APC ne a makon farko na shekarar 2026. Hakanan jaridar tace an yiwa Kwankwaso tayin komawa APC din amma yace ba zai koma ba. Jaridar tace akwai shirin tsige mataimakin gwamnan jihar ta Kano inda za'a baiwa Sulen Garo mataimakin Gwamnan. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2005346746399130068?t=r3jZ53BXohJbwR7aq94qxA&s=19 A wani ci gaba da aka samu game da lamarin, Du 'yan jam'iyyar NNPP musamman masu aiki a gidan Gwamnatin jihar ta Kano sun sanar da cewa sun amince Kwankwaso da Abba su jasu zuwa APC.