Sunday, December 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Da Duminda: Kananan yara sun rigamu gidan Gaskiya bayan Tàrwàtsèwàr wani abu a Borno

Da Duminda: Kananan yara sun rigamu gidan Gaskiya bayan Tàrwàtsèwàr wani abu a Borno

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Borno na cewa kananan yara 4 ne suka rigamu gidan gaskiya bayan fashewar Bàm a garin Banki dake karamar hukumar Bama a jihar ta Borno. Kakakin 'yansandan jihar,Nahum Daso ne ya tabbatar da hakan inda yace bam din ya tashine a tashar motar dake garin. Yace yaran na wasa sa Bam dinne bayan sun daukoshi daga daji kamin ya fashe dasu. Yace yaran da lamarin ya rutsa dash sune kamar haka: Awana Mustapha, 15; Malum Modu, 14; Lawan Ibrahim, 12 da Modu Abacha, 12.
Gwamnatin Tarayya tace ba zata iya gano inda Tshàgyèràn Dhàjì masu nuna kudi da màkàmàì a Tiktok suke ba

Gwamnatin Tarayya tace ba zata iya gano inda Tshàgyèràn Dhàjì masu nuna kudi da màkàmàì a Tiktok suke ba

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, ba zata iya bibiyar inda tshageran Dhajin masu nuna kudi da makamai a Tiktok suke ba. Me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala ne ya bayyana hakan a wata hira da aka yi dashi a gidan Rediyo me suna Nigerian Info. Yace duk wani me amfani da yanar gizo a fadin Najeriya sun san inda yake zasu iya bibiya da zuwa inda yake dan a kamashi. Yace amma su tshageran Dhajin suna amfani da manhajar yanar gizo ta Starlink ce wadda gwamnati bata iya bibiyarta shiyasa.
Ji yanda wani ya Hàllàqà mahaifiyarsa saboda ya gaji da yi mata Hidima kuma ta tsufa sosai

Ji yanda wani ya Hàllàqà mahaifiyarsa saboda ya gaji da yi mata Hidima kuma ta tsufa sosai

Duk Labarai
Hukumomi a birnin Tokyo na kasar Japan sun kama wani mutum me suna Masato Watabe dan kimanin shekaru 79 bayan da ya hallaka mahaifiyarsa. Mahaifiyar tasa nada shekaru 100 a Duniya kuma shine ke kula da ita. Hukumomin birnin sun ce ya hallakata ne ya hanyar rufe mata baki. Mutumin dai da kansa ya kirawo 'yansanda. Kasar Japan na fama da karancin matasa inda manyan mutane masu yawan shekaru dole sune ke kula da iyayensu da shakeru suka kamasu.
Wannan wane irin rashin Tausai ne haka, Kalli Bidiyon Me gida ya watsar da kayan wani mutum da aka yi Ghàrkùwà dashi bayan kudin haya sun kare

Wannan wane irin rashin Tausai ne haka, Kalli Bidiyon Me gida ya watsar da kayan wani mutum da aka yi Ghàrkùwà dashi bayan kudin haya sun kare

Duk Labarai
Wannan Bidiyon ya dauki hankula a kafafen sadarwa inda ya nuna yanda wani me gidan haya ya watsawa wani mutuk kaya waje bayan da kudin hayarsa suka kare. Saidai abinda ya fi baiwa mutane mamaki shine mutumin na can a hannin Tshàgyèràn Dhàjì ana faman yanda za'a karboshi. Kuma me gidan ya sani amma yace ba ruwansa. https://twitter.com/General_Somto/status/1996932969584300229?t=0pcRTvihw2CAQImSneLNBA&s=19
Kalli Bidiyon yanda jami’in tsaron Civil Defence ke tonawa wani na hannun daman Gwamna Asiri cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake hana mutane zàmàn Lafiya

Kalli Bidiyon yanda jami’in tsaron Civil Defence ke tonawa wani na hannun daman Gwamna Asiri cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake hana mutane zàmàn Lafiya

Duk Labarai
Wannan wani jami'in Hukumar Civil Defence ne a jihar Imo da ya bayyana wani me suna, Chinasa Nwaneri da cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake aikata ayyukan Ashsha na hare-hare a jihar. Chinasa Nwaneri daya ne daga cikin masu taimakawa gwamnan jihar Imo na musamman akan ayyukansa. Wannan zargi dai yayi nauyi inda mutane ke cewa ya kamata a bincikeshi. https://twitter.com/General_Somto/status/1996841460642308532?t=d9ydlNYqHeWR7BwvdL3Ujg&s=19
Allah Sarki, Kalli Bidiyon yanda wani dan Najeriya ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta saboda murnar shugaba Tinubu ya nada janar Christopher Musa Ministan tsaro

Allah Sarki, Kalli Bidiyon yanda wani dan Najeriya ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta saboda murnar shugaba Tinubu ya nada janar Christopher Musa Ministan tsaro

Duk Labarai
Wannan wani matashi dan Najeriya ne da yace yana tsaka ds tafiya zuwa wani gari amma da yaji labarin an baiwa Janar Christopher Musa mukamin Ministan tsaro. Shine ya tsaya a wani kauye ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta. Yayi fatan cewa Allah ya baiwa sabon Ministan nasara ya kawo karshen matsalar tsaron Najeriya. https://twitter.com/ZagazOlaMakama/status/1996917787412025722?t=PFhCXZrlhsAi_5EPBBrEGA&s=19
Wata Sabuwa: Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno sun bude gidan Rediyo suna yada shirye-shiryensu da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci

Wata Sabuwa: Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno sun bude gidan Rediyo suna yada shirye-shiryensu da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Borno na cewa kungiyar dake ikirarin Jihadi ta ÌŚWÀP ta fadada ayyukan gidan rediyonta inda take yada shirye-shiryenta da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci. Saidaj ba kaitsaye gidan Rediyon ke aiki ba, suna dauka ne sai a rika turawa kamar yanda ake tura waka ko fim, kamar yanda masanin harkar tsaro, BrantPhilip ya ruwaito. Ya kuma wallafa Sautin muryar daya daga cikin shirye-shiryen kungiyar da aka nada wanda aka yadashi da Turanci. https://twitter.com/BrantPhilip_/status/1996857715600007465?t=XK7ddJaXBlEmU-7-7FOPsg&s=19 Wannan lamari dai ya zowa mutane da mamaki inda da yawa suka rika tunanin yaushe Kungiyar har ta samu nutsuwar yin abubuwa haka?
Kalli karin Bidiyon giwayen da suka bayyana a jihar Borno

Kalli karin Bidiyon giwayen da suka bayyana a jihar Borno

Duk Labarai
A jiyane dai muka samu Rahoton cewa, Giwaye sun bayyana garin Kala Balge na jihar Borno inda mutane suka taru suna kallonsu. Zagazola Makama yace giwayen sun rika cinye amfanin gona inda yayi kira ga mahukunta dasu kaiwa jama'a dauki. Bidiyon da hotunan giwayen sun ci gaba da yaduwa a kafafen sada zumunta Wasu rahotanni sun ce giwayen sun shiga garin ne daga kasar Chadi. https://www.tiktok.com/@umarfaruq6966/video/7579953257259339029?_t=ZS-91y7VEZ0NGa&_r=1