Sunday, February 15
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Wata Sabuwa: An baiwa Shugaba Tinubu shawarar yayi kokari tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya koma APC in ba haka ba zai kawo mai tangarda a zaben 2027

Wata Sabuwa: An baiwa Shugaba Tinubu shawarar yayi kokari tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya koma APC in ba haka ba zai kawo mai tangarda a zaben 2027

Duk Labarai
Dan takarar Gwamnan jihar Kebbi a jam'iyyar APC, Mallam Salihu Isa Nataro ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar ya yi kokarin mayar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai jam'iyyar APC. Yace masa, El-Rufai na da karfin fada aji sosai musamman a siyasar Arewa maso yamma. Yace kuma komawarsa jam'iyyar APC zata sa talakawa da yawa su dawo suna son Tinubu din. Yace kada a bari rashin jituwa tsakanin shuwagabannin jam'iyya da El-Rufai yasa a kyaleshi. Ya bayyana cewa ya kamata a yi kokari El-Rufai ya koma APC kamin zaben 2027.
Watan mu 6 bamu da wutar Lantarki>>Inji Wannan matar dake zaune a birnin New York City na kasar Amirka

Watan mu 6 bamu da wutar Lantarki>>Inji Wannan matar dake zaune a birnin New York City na kasar Amirka

Duk Labarai
Kristy Hallowell 'yar shekaru 44 dake zaune a Greenwood Lake, New York City na kasar Amurka tace watansu 6 kenan basu da wutar Lantarki. Ta bayyana cewa a watanni 6 na karshe na shekarar 2025 basu da wuta. Tace ta rasa aikinta kuma an kara kudin wuta, dan haka ta kasa biya, tace gas ma basu dashi. Tana zaunene ita da 'ya'yanta da mahaifiyarta. Inda tace dole saidai janareta suka rika amfani dashi. Saidai an samu irin kungiyoyin masu taimakawa mutane sun biya mata rabin kudin kuma an sakw hada musu wutar amma har yanzu basu da gas. Saidai tace har yanzu akwai yiyuwar a sake yanke mata wutar dan bashin da ake binta ya kai na sala $3000.
Kalli Bidiyon: Amsar da Riyad Mahrez ya bayar da aka tambayeshi ko yana ganin Rafali ne ya cinsu?

Kalli Bidiyon: Amsar da Riyad Mahrez ya bayar da aka tambayeshi ko yana ganin Rafali ne ya cinsu?

Duk Labarai
Bayan wasan da Algeria ta buga da Najeriya jiya wanda Najeriya ta ci Algeria 2-0, An tambayi Tauraron dan kwallon Algeria, Riyad Mahrez ko me zai ce kan Rafali. Yace tabbas Rafali ba dari bisa dari yake ba amma kuma baya zarginsa, yace Najeriya sun fisu kokari ne kawai Game da ritaya, Mahrez yace wannan shine wasan karshe da zai buga na kasar AFCON. https://twitter.com/i/status/2010273589153661373
Shugaban Yahudawan Najeriya sun kaiwa Nnamdy Khanu ziyara a gidan yarin Sokoto

Shugaban Yahudawan Najeriya sun kaiwa Nnamdy Khanu ziyara a gidan yarin Sokoto

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban Yahudawan Najeriya, daga jihohin Inyamurai ya kaiwa Nnamdy Khanu ziyara a gidan yarin Sokoto. Rahoton yace, Sun kai masa ziyarar ne ranar 10 ga watan Janairu. Shugaban Yahudawan yace sun dade suna yiwa Khanu addu'ar Allah ya kubutar dashi. Saidai da yawan 'yan Najeriya sun yi mamakin cewa dama akwai Yahudawa bakake kuma a Najeriya?
A yayin da yake shirin komawa jam’iyyar APC: Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi ganawar sirri da Kwankwaso

A yayin da yake shirin komawa jam’iyyar APC: Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi ganawar sirri da Kwankwaso

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir ya gana da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a kasar Faransa. Bayan da ya dawo gida Najeriya, ya kuma ganawa da Dr. Rabiu Musa Kwankwaso wanda Tinubu ne ya aikashi ya roki Kwankwaso ya koma APC. An yi ganawar ne ranar Talata, kamar yanda kafar Daily Nigerian. Babu dai tabbacin matsayar da Kwankwaso ya dauka.