Wednesday, January 14
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kasar Ghana ta koro ‘yan Najeriya 42 da suka je cirani kasar

Kasar Ghana ta koro ‘yan Najeriya 42 da suka je cirani kasar

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Ghana na cewa, kasar ta koro 'yan Najeriya 42 da suka je chirani kasar. Kasar ta kori jimullar 'yan kasashen waje 68 daga yankin Ashanti bayan da aka samesu da aikata miyagun laifuka, irin su Qaruwanchi, da sauransu. Hukumomin kasar sun ce sun dauki wannan mataki ne dan tsaftace kasarsu da kuma kiyaye al'ummarsu daga miyagun laifukan da bakin ciranin ke yi.
Da Duminsa: Musulmai 12 dake kan hanyar zuwa wajan Maulidi sun bace a kauyen Zak dake jihar Filato

Da Duminsa: Musulmai 12 dake kan hanyar zuwa wajan Maulidi sun bace a kauyen Zak dake jihar Filato

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Filato na cewa, Musulmai 12 dake kan hanyar zuwa Maulidi a Karamar hukumar Wase jihar Filato sun bace. rahotanni sun wasu Tshàgyèràn Dhàjì Kiristoci ne suka yi garkuwa dasu. Garkuwar ta farune ranar 21 ga watan Disamba a daidai kauyen Zak. Wani shaida ne ya kai rahotan faruwar lamarin. Kafar Zagazola Makama tace jami'an tsaro sun je wajan inda aka fara neman wanda aka dauke din.
Bayan kammala makarantar Sakandare taki zuwa Jami’a inda ta cewa iyayenta Qur’ani take son haddacewa

Bayan kammala makarantar Sakandare taki zuwa Jami’a inda ta cewa iyayenta Qur’ani take son haddacewa

Duk Labarai
Matashiya, Nabila Ibrahim Makama ta ki zuwa jami'a bayan kammala makarantar Sakandare inda ta gayawa iyayenta cewa, Qur'ani take son haddacewa. Ta haddace Qur'ani, amma duk da haka tace a barta tana son rubutashi da ka kamin ta shiga jami'a, kuma ta yi hakan. Bayan nan ne ta shiga jami'ar Maryam Abacha American University inda ta karanci kimiyyar bayanai. Ta kammala da sakamako mafi kyawu a ajinsu, kuma jami'ar ta ce mata ta zabi duk makarantar da take so a Duniya zata dauki nauyin karatun ta zuwa can dan ta ci gaba da karatu.
Kalli Bidiyon: Yanda aka yi saukar Qur’ani da addu’o’i a jihar Kebbi dan Rokon Allah ya tsare tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami daga sharrin EFCC

Kalli Bidiyon: Yanda aka yi saukar Qur’ani da addu’o’i a jihar Kebbi dan Rokon Allah ya tsare tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami daga sharrin EFCC

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kebbi na cewa Al'ummar Jihar sun taru inda aka sauke Qur'ani da kuma yiwa Tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami Addu'ar Allah ya tsareshi daga sharrin EFCC. Abubakar Malami dai yana tsare a hannun hukumar EFCC biyo bayan zargin da take masa na aikata ba daidai ba da kudaden kasa. Tuni hukumar ta fara killace wasu kadarorinsa. https://twitter.com/ADCVanguard_/status/2003206191288401976?t=lEPGJwFhRQF4LEFA7XVJBA&s=19
Da Duminsa: Bayan da kasar Amurka ta saka kasar Nijar cikin kasashen data Haramtawa shuga kasarta, Hukumomin Nijar din sun ce suma sun haramtawa ‘yan Amurkar shiga kasarsu

Da Duminsa: Bayan da kasar Amurka ta saka kasar Nijar cikin kasashen data Haramtawa shuga kasarta, Hukumomin Nijar din sun ce suma sun haramtawa ‘yan Amurkar shiga kasarsu

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Nijar na cewa, kasar ta Haramtawa 'yan kasar Amirka shiga kasarta da basu Visa. Hakan na zuwane biyo bayan saka kasar Nijar cikin kasashen da Amirka ta haramtawa shiga kasarta. Amirka ta saa hadda Najeriya da sauran wasu kasashe data kira Matalauta cikin kasashen data haramtawa shiga kasarta.
Hukumar jirgin kasa ta Najeriya ta sanar da rage kudin tikitin jirgin da kaso 50 saboda bukukuwan karshen shekara

Hukumar jirgin kasa ta Najeriya ta sanar da rage kudin tikitin jirgin da kaso 50 saboda bukukuwan karshen shekara

Duk Labarai
Hukumar jirgin kasa ta Najeriya, The Nigerian Railway Corporation ta sanar da rage farashin Tikitin jirgin da kaso 50 saboda bukukuwan karshen shekara. Hukumar tace ragin zai fara aiki ne a yau, Talata. A ranar 25 ga watan Disamba ne za'a yi bikin Kirsimeti sannan akwai bikin karshen shekara na 1 ga watan Janairu wanda duka Gwamnati ta bayar da hutu.
Gwanin Burgewa, Kalli Bidiyon yanda ‘yan kwallon kasar Egypt suka karanta Fatiha da Suratul Ikhlas sau 3 dan neman nasara kamin wasansu da Zimbabwe

Gwanin Burgewa, Kalli Bidiyon yanda ‘yan kwallon kasar Egypt suka karanta Fatiha da Suratul Ikhlas sau 3 dan neman nasara kamin wasansu da Zimbabwe

Duk Labarai
'Yan Kwallon kasar Misra/Egypt sun karanta Fatiha da suratul Ikhlas sau 3 a dakin canja kaya kamin wasansu da kasar Zimbabwe a ci gaba da gasar AFCON. Bidiyon nasu ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda musamman musulmai suka rika musu fatan Nasara. https://twitter.com/SalahUpdates/status/2003266206233755890?t=sRHJ59Q3V0Hiw2pwduOocA&s=19 Kuma sun yi nasara a wasan inda Egypt taci 2 Zimbabwe taci 1
Kalli Bidiyon: A yayin da ya rage saura kwanaki 2 a tashi Duniya kamar yanda faston kasar Ghana yace, Mabiyansa da suka yadda dashi sun sayar da kadarorinsu sun koma wajansa da zama

Kalli Bidiyon: A yayin da ya rage saura kwanaki 2 a tashi Duniya kamar yanda faston kasar Ghana yace, Mabiyansa da suka yadda dashi sun sayar da kadarorinsu sun koma wajansa da zama

Duk Labarai
Faston nan na kasar Ghana da ya ce wai an masa Wahayi Duniya zata tashi ranar Kirsimeti watau 25 ga watan Disamba kuma wai an ce masa ya kera jiragen ruwa 8 dan ya kwashi mutane a ciki saboda za'a yi ruwa irin na Dufana a yanzu ya fito yanawa mabiyansa bankwana. Rahotanni sun ce wadanda suka yadda dashi tuni suka sayar da kadarorinsu suka koma wajansa da zama inda suke jiran ranar 25 ga wata tazo. An ganshi ya fito yanawa mabiyan nasa bankwana. https://twitter.com/OzorNdiOzor/status/2003172382266290185?t=OmsYRbBH1RqQiyr_YeBMRQ&s=19