Friday, March 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kungiyar Masu Hako danyen Man fetur a Najeriya sun gargadi Gwamnati akan baiwa ‘yan kasuwa lasisin shigo da man fetur Najeriya

Kungiyar Masu Hako danyen Man fetur a Najeriya sun gargadi Gwamnati akan baiwa ‘yan kasuwa lasisin shigo da man fetur Najeriya

Duk Labarai
Kungiyar kamfanonin dake hako danyen man fetur a Najeriya, CORAN ta gargadi Gwamnatin tarayya ta yi hankali da baiwa 'yan kasuwa lasisin shigo da man fetur daga kasashen waje. Hakan na zuwane a yayin da baraka ta faru tsakanin 'yan kasuwar da Matatar man fetur ta Dangote inda aka shiga kotu, 'yan kasuwar na neman a basu lasisin shigo da man fetur din daga kasar waje saboda sun ce man fetur din Dangote yayi tsada amma shi kuma yana neman kada a basu lasisin saboda a cewarsa zasu shigo da man fetur din da bai da inganci wanda gurbataccene. A sanarwar da kungiyar CORAN ta fitar ta bakin Sakataren yada labaranta, Eche Idoko tace abin damuwa ne yanda 'yan kasuwar suka nace sai sun shigo da man fetur din daga kasar waje. Yace 'yan kasuwar suna son mayar da Najeriya wajan kawo man fetur ...
Ku daina Rige-Rigen zuwa kasashen waje neman aiki, Ku tsaya mu gyara kasa>>Shugaba Tinibu ya roki Matasa

Ku daina Rige-Rigen zuwa kasashen waje neman aiki, Ku tsaya mu gyara kasa>>Shugaba Tinibu ya roki Matasa

Duk Labarai
Shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ya roki matasan Najeriya da su daina rige-rigen fita kasashen waje neman aiki. Shugaban ya roki matasa da su tsaya a gyara kasa dan kuwa Najeriya ma zata iya zama kamar kasashen da suke mafarkin zuwa. Tinubu ya bayyana hakane a wajan taron yaye daliban Jami'ar Uyo inda shugaban jami'ar Port Harcourt, Prof. Owunari Georgewill ya wakilceshi. Ya jawo hankalin matasan akan su yi amfani da ilimin da suke dashi wajan warware matsalolin da ake dasu a Najeriya.
Yawan ‘yan Najeriya dake daukar Albashin kasa da Dubu 100 sun karu

Yawan ‘yan Najeriya dake daukar Albashin kasa da Dubu 100 sun karu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa yawan 'yan Najeriya dake daukar Albashin kasa da Naira Dubu 100 sun kai kaso 42 cikin 100. Saidai a shekarar data gabata ta 2023,mutanen da suke karbar albashin kasa da dubu 100 a wata kaso 26 ne. Hakanan faduwar darajar Naira tasa 'yan Najeriyar masu daukar kasa da Naira dubu 100 suke shan wahala wajan biyan bukatansu na yau da kullun Hakanan wanda basu da hanyar samun kudi a yanzu aun kari zuwa kaso 28 cikin 100.
‘Yansandan Kano sun kama waɗanda ake zargi da garkuwa da mutane

‘Yansandan Kano sun kama waɗanda ake zargi da garkuwa da mutane

Duk Labarai
Rundunar 'yansandan jihar Kano ta ce ta kama wasu mutane da take zargi sun shiga jihar ne da nufin yin yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa. Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, kakakin rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce an kama mutanen a garin Kwanar Dangora, kuma yanzu suna hannun 'yansanda, bayan da ya ya ce sun shiga jihar da nufin yin garkuwa da mutane. Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce ''wannan kasuwancin fa na satar mutane ba zai yi tasiri a Jihar Kano ba Insha Allah''. Ya kuma gode wa al'ummar jihar bia addu'o'in da ya ce suna yi a koyause. Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, ba ta cikin jihohin yankin da ke fama da masu garkuwa da mutane, kodayake ana ɗan samu jifa-jifa, amma ba kamar sauran wasu jhohin yankin, da matsalar ta yi ƙa...
Na yi mamakin sauke ni daga muƙamin minista – T Gwarzo

Na yi mamakin sauke ni daga muƙamin minista – T Gwarzo

Duk Labarai
Tsohon ƙaramin ministan gidaje na Najeriya, Abdullahi Tijjani Gwarzo ya ce ya yi mamakin sauke shi da a aka yi daga muƙaminsa. Yayin wata hira da BBC kwanaki bayan sauke shi , T Gwarzo ya ce babu wani laifi da ya yi, wanda ya janyo aka sauke shi daga muƙamin nasa, sabod a cewarsa ya yi iya baƙin ƙoƙarinsa a muƙamin da aka ba shi. ''Batun ya zo min da mamaki, domin ba na tunanin wani abu mai kama da wannan zai faru da ni'', in ji shi. Ya ƙara da cewa Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi la'akari da tarayyarsu tun ta da can wajen naɗa shi muƙamin. Ya ce fiye da shekara 14 suna tare da Tinubu tun a jam'iyyar ACN, shi da Nuhu Ribadu da Sanata George Akuwam - da ke riƙe da muƙamin sakataren gwamnati a yanzu. Sai dai ya ce Allah ne ke ba da mulki, kuma ya karɓe a duk lokacin da ya so, ...