Monday, December 15
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Gwamnati ta fitar da gargadin Ambaliyar ruwan da za’a kwashe kwanaki 5 ana yi a jihohi 19, karanta jadawalin Jihohin

Da Duminsa: Gwamnati ta fitar da gargadin Ambaliyar ruwan da za’a kwashe kwanaki 5 ana yi a jihohi 19, karanta jadawalin Jihohin

Duk Labarai
Gwamnati tacw za'a kwashe kwanaki 5 ana ruwan sama a jere wanda hakan zai iya jawo ambaliyar ruwa a jihohi 19 da furare 76. Bangaren kula da ambaliyar ruwa na ma'aikatar Muhalli ne ya fitar da wannan sanarwar. Hakan na zuwane yayin da ambaliyar ruwan tuni ta shiga jihohin Gombe, Plateau, Ogun, Anambra, Delta, da Legas a ranar Talata. Wannan ambaliyar ruwa a cewar sanarwar zata fara ne daga ranar 5 zuwa 9 ga watan Augusta. Garuruwan da lamarin zai shafa sun hada da Akwa-Ibom (Edor, Eket, Ikom, Oron, Upenekang); Bauchi (Tafawa-Balewa, Azare, Jama’are, Kari, Misau, Jama’a); Ebonyi (Abakaliki, Echara, Ezilo); Cross-River (Ogoja Edor, Obubra); Nasarawa (Keana, Keffi, Wamba); Benue (Agaku, Buruku, Gboko, Igumale, Ito, Katsina-Ala, Ugba, Vande-Ikya); Kaduna (Jaji, Kafancha, Birnin-Gwa...
A wane littafin aka ce sai an sha wuya a gidan aure? Maza ku ji tsoron Allah sai ku auri mace tubarkallah amma bayan wata 7 ta rame ta lalace>> Inji Nafisa Ishak

A wane littafin aka ce sai an sha wuya a gidan aure? Maza ku ji tsoron Allah sai ku auri mace tubarkallah amma bayan wata 7 ta rame ta lalace>> Inji Nafisa Ishak

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Nafisa Ishak ta bayyana damuwa game da yanda wasu maza ke wa matan da suka aura rikon sakainar kashi. Ta bayar da misali da kanta cewa tana gidan miji duk ta lalace amma data fito sai da ta ci sama da Tiriliyan 3 kamin ta zama yanda ake kallonta. Ta yi kira ga maza da su ji tsoron Allah akan yanda suke rikon mata. Wadannan kalamai nata sun jawo cece-kuce sosai. https://www.tiktok.com/@nafisa_ishak/video/7533924472827415864?_t=ZS-8ydvIyOE6l6&_r=1
Dan majalisar tarayya daga jihar Zamfara Kabiru Mai Palace ya gyara makabartu 80 a matsayin aikin da yawa mazabarsa

Dan majalisar tarayya daga jihar Zamfara Kabiru Mai Palace ya gyara makabartu 80 a matsayin aikin da yawa mazabarsa

Duk Labarai
Dan majalisar tarayya daga Zamfara Kabiru Mai Palace ya gayara makabartu 80 a jihar. Da yake magana da manema labarai ranar Talata wajan kaddamar da aikin, yace kowane mutum idan ya rasu makabarta za'a kai a binneshi. Makabartun da aka gyara na tsakanin kananan Hukumomin Tsafe da Gusau ne Ya kuma bayyana cewa gyaran ya zama dole lura da halin lalacewa da makabartun suke. Ya sha Alwashin daukar masu gadin makabartar da kuma biyansu Haraji.
Kalli Bidiyo: Yanda aka daina sakani a Fim saboda bana bada hadin kai ayi…. dani>>Inji jarumar fina-finan Hausa, Ummi Hutu

Kalli Bidiyo: Yanda aka daina sakani a Fim saboda bana bada hadin kai ayi…. dani>>Inji jarumar fina-finan Hausa, Ummi Hutu

Duk Labarai
Tauraruwar Fina-finan Hausa dake a Kaduna, Ummi Hutu ta yi korafin cewa, an daina sakata a fim saboda bata bada hadin kai. Ta bayyana hakane a wani Bidiyon ta daya bayyana a Tiktok. Tace Amma ta samu wata harkar shine ake mata bita da kulli ana mata bakin ciki amma tace masu yi basu isa ba. https://www.tiktok.com/@iya_habu/video/7535086847328914694?_t=ZS-8ydKY609Agr&_r=1
Kalli Bidiyo: Babban Burina shine in zama Sanata, Zan Fito takara kuma babu wanda ya isa yasa in janye>>Inji Sheikh Salihu Zaria

Kalli Bidiyo: Babban Burina shine in zama Sanata, Zan Fito takara kuma babu wanda ya isa yasa in janye>>Inji Sheikh Salihu Zaria

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Salihu Zaria ya bayyana cewa yana da sha'awar zama sanata. Yace ba zasu rika bari wadanda basu cancanta ba su ci gaba da mulkar mutane ba. Yace zai fito takarar sanata kuma babu wanda ya isa yasa ya janye. https://www.tiktok.com/@yunus.abu.bakr6/video/7534836390903745848?_t=ZS-8ydK7oiav8T&_r=1
Kalli Bidiyon: Na taba aure sau daya amma yanzu bani da aure amma ina fatan in yi aure in haihu>>Inji Ladidi

Kalli Bidiyon: Na taba aure sau daya amma yanzu bani da aure amma ina fatan in yi aure in haihu>>Inji Ladidi

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Ladidi tubeless ta bayyana cewa, ta taba aure a baya amma auren ya mutu. Tace bata taba haihuwa ba amma tana fatan nan gaba ta sake yin aure ta haihu. Ladidi Tubeless ta bayyana hakane a hirar da BBCHausa suka yi da ita. https://www.tiktok.com/@ladidi_tubbles/video/7535082673556032824?_t=ZS-8ydI3fmSNjF&_r=1
Gwamnatin tarayya ta rabawa masu kananan sana’o’i tallafin Naira 250,000 dan karfafasu a Jihar Ondo

Gwamnatin tarayya ta rabawa masu kananan sana’o’i tallafin Naira 250,000 dan karfafasu a Jihar Ondo

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta rabawa masu kananan sana'o'i tallafin Naira 250,000 kyauta a jihar Ondo. Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ya jagoranci rabon inda yace wannan tsari ne da ake yinshi a kowace sashe na kasarnan dan karfafa masu kananan sana'o'i. Yace wannan daya daga cikin tsare-tsaren shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne na kokarin karfafa kananan 'yan kasuwa da suka yi zarra. Yace kudin ba bashi bane, an bayar dasu ne dan gwamnati ta karfafa 'yab kasuwar kyauta.
Manufofin Tinubu sun ƙara jefa miliyoyin ƴan Najeriya cikin talauci – Falana

Manufofin Tinubu sun ƙara jefa miliyoyin ƴan Najeriya cikin talauci – Falana

Duk Labarai
Fitaccen lauyan nan a Najeriya mai kare haƙƙin bil adama, Femi Falana ya caccaki manufofin tattalin arzikin Shugaba Bola Tinubu inda ya ce "manufofin masu tsauri" sun shafe masu matsakaicin samu tare da ƙara jefa miliyoyin mutanen ƙasar cikin talauci. Falana ya ce duk da cewa a baya-bayan nan shugaban ƙasar ya fito ya bayyana cewa ya san irin halin ƙunci da ƴan Najeriya ke ciki, manufofinsa sun ƙara talauta al'umma. Lauyan mai muƙamin SAN ya shaida hakan ne a hirar da ya yi a gidan Talabijin na Channels inda kuma ya ga baiken yadda gwamnati ke cefanar da kamfanoni ga ƴan kasuwa lamarin da a cewarsa ya ci karo da ƙoƙarin da ake na magance bambancin samu a tsakanin ƴan Najeriya. Ya ƙara da cewa ya zama dole gwamnati ta sake nazari kan manufofinta tare da samar da tallafi ga ƴan Naje...
Da kasuwancina na habaka sosai, bankuna sun rika aikomin tsala-tsalan ‘yan mata dan in mayar da kudin ajiya ta can>>Inji Attajirin Najeriya, Femi Otedola

Da kasuwancina na habaka sosai, bankuna sun rika aikomin tsala-tsalan ‘yan mata dan in mayar da kudin ajiya ta can>>Inji Attajirin Najeriya, Femi Otedola

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Femi Otedola ya bayyana cewa a lokacin kasuwancinsa na habaka sosai, bankuna suna aika mata kyawawan 'yan mata dan su ja hankalinsa ya mayar da ajiyar kudi acan. Ya bayyana hakane a wani littafin tarihin rayuwarsa da yanda ya gudanar da kasuwanci da yake shirin wallafawa wanda jaridar TheCable tace ta samu gani. Yace ya samu matsala bayan da ya saro man fetur daga kasashen wajan lokacin man yana a farashin Dala $140 amma aka samu tsaiko be karaso Najeriya ba sai da ya koma farashin dala $40. Yace hakan ya jefashi cikin matsanancin bashi. Hakanan yace karya darajar Naira ma ya kara jefashi cikin wahala sosai. Yace a lokacin da bashin bankin ya mai yawa kuma sai bankin suka koma aika masa da jigba-jibgan mazaje masu fadin kirji dan su bashi tsoro ya biya.