Thursday, February 26
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Mun Barkune kunata hauka amma babu maganar aure tsakanina da Maiwushirya, Taimakon Rayuwata yake>>Inji ‘YarGuda

Kalli Bidiyon: Mun Barkune kunata hauka amma babu maganar aure tsakanina da Maiwushirya, Taimakon Rayuwata yake>>Inji ‘YarGuda

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok Abasiya 'YarGuda itama ta fito ta tabbatar da maganar cewa babu aure tsakaninta da Maiwushirya. Ta bayyana hakane a wani Bidiyo inda take cewa Maiwushirya taimakonta yake. Tace Ko da ta amsa a Kotu cewa zata aureshi ba da gaske take ba. https://www.tiktok.com/@pharooq_/video/7565550522065767701?_t=ZS-90sPvJMyw1A&_r=1
Kalli Bidiyon Gwanin Ban Tausai: Yanda ‘Yan Uwan Habasiyya ‘YarGuda suka je Kano daga Zamfara zasu mayar da ita Gida

Kalli Bidiyon Gwanin Ban Tausai: Yanda ‘Yan Uwan Habasiyya ‘YarGuda suka je Kano daga Zamfara zasu mayar da ita Gida

Duk Labarai
Bayan hukuncin kotu da kuma tsayawar shirin da suke yi ita da Idris Maiwushirya, 'yan uwan Habasiyya 'YarGuda sun je Kano daga jihar Zamfara dan mayar da ita Gida. A Bidiyon an ga daya daga cikin 'yan uwan nata na bayyana cewa, Bakin ciki ake musu saboda Maiwushirya yana taimakon rayuwarta ne da abubuwan da ba'a rasa ba. Ta bayyana cewa matsalar 'yan Bindiga ta damesu a garinsu. Saurarin jawabinta a Bidiyon kasa: https://www.tiktok.com/@pharooq_/video/7565543245309152533?_t=ZS-90sOSmk9WC1&_r=1
Kalli Bidiyon: Asarar Naira Miliyan 3 Abba El-Mustapha yasa na yi kuma Allah ya isa, Sannan bai isa yamin Auren Dole ba>>Inji Maiwushirya

Kalli Bidiyon: Asarar Naira Miliyan 3 Abba El-Mustapha yasa na yi kuma Allah ya isa, Sannan bai isa yamin Auren Dole ba>>Inji Maiwushirya

Duk Labarai
Idris Maiwushirya ya bayyana bacin ransa kan abinda yace Abba EL-Mustapha ya masa inda yace ya shirya abinshi amma saboda bakin ciki aka sa yayi sarar Naira Miliyan 3. Maiwushirya yace Abba El-Mustapha bai isa yasa a masa auren dole be sannan kuma shi da ya kama Chairlady a ni sai ka goyani wa yace sai ya aureta? Ya kuma bayyana magungunan da ya saya saboda rashin lafiyar da ya kwanta duk saboda wannan matsalar. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya watsu sosai inda aka ganshi a kwance. Ya kara da cewa da yana so ya auri 'YarGuda ai da ba sai an tursasa shi ba. https://www.tiktok.com/@pharooq_/video/7565543951642496277?_t=ZS-90sKFJ5TOmv&_r=1
Ba zan tsaya takara a shekarar 2027 ba, na hakura haka, a samu wani matashi da bai kaini Shekaru ba shima ya zo ya gwada>>Inji Dan majalisar wakilai daga jihar Sokoto, Hon. Abdussamad Dasuki

Ba zan tsaya takara a shekarar 2027 ba, na hakura haka, a samu wani matashi da bai kaini Shekaru ba shima ya zo ya gwada>>Inji Dan majalisar wakilai daga jihar Sokoto, Hon. Abdussamad Dasuki

Duk Labarai
Dan majalisar Wakilai, Hon. Abdussamad Dasuki me wakiltar mazabar Kebbe/Tambuwal daga jihar Sokoto ya bayyana cewa ba zai tsaya takara a shekarar 2027 ba. Yace ya barwa matasa 'yan kasa da shekaru 40 su tsaya takarar dan kawo sauyi da ci gaba a mazabar tashi. Yace yayi hakanne ba dan ya gaji ko gazawa ba inda yace har yanzu shi matashi ne amma ya haura shekaru 40. Yayi godiya ga mutanen mazabatarsa da iyayen gidansa a siyasa da suka bashi dama a shekaru 14 da yayi yana siyasar.
Hukumar Hisbah ta Kano ta kama mutane 25 inda namiji ke shirin auren Namiji a Kano

Hukumar Hisbah ta Kano ta kama mutane 25 inda namiji ke shirin auren Namiji a Kano

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta kama mutane 25 dake shirin kulla auren Namiji da Namiji. An kamasu ne a Fatima Event Center dake Hotoro ranar Lahadi. Mataimakin Kwamanda na Hisbah, Mujahedeen Aminudeen ne ya bayyana hakan ga manema labarai. Yace daga cikin wadanda aka kama akwai maza 18, mata 7. Yace sun samu bayanan sirri ne kan daura auren 'yan Luwadin.
Kalli Bidiyon: Duk masu min fatan in koma me kiba kamar yanda nake a baya, Ina Rokon Allah ya dora musu kibar>>Inji Hadiza Gabon

Kalli Bidiyon: Duk masu min fatan in koma me kiba kamar yanda nake a baya, Ina Rokon Allah ya dora musu kibar>>Inji Hadiza Gabon

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta magantu kan cece-kuce da ake yawan yi kan ramar da ta yi. Ta yi wannan bayanine a shirinta na Gabon Show wanda ke gudana a shafinta na YouTube. Gabon ta bayyana rashin jin dadin cece-kucen da ake yi akan ramar tata inda tace zabinta ne ta kasance da rama. https://www.tiktok.com/@talk_showw/video/7565219801795284245?_t=ZS-90rvlB7zRg1&_r=1
Kalli Bidiyon: Wallahi ‘yan Dariqa da kuke cewa Qafurai, ko ‘Yan Bindi’a sun fi ku Ahlussunah ilimi, Mafi yawancin ‘yan Ahlussunah Jahilaine sai ‘yan kadan>>Inji Malamin Izala

Kalli Bidiyon: Wallahi ‘yan Dariqa da kuke cewa Qafurai, ko ‘Yan Bindi’a sun fi ku Ahlussunah ilimi, Mafi yawancin ‘yan Ahlussunah Jahilaine sai ‘yan kadan>>Inji Malamin Izala

Duk Labarai
Malam wanda dan Izala ne ya caccaki masu kafurta 'yan darika da masu kiransu 'yan Bindi'a. Yace mafi yawancin Ahlussunah jahilai ne inda yace 'yan Dariqa sun fisu Ilimi. Kalli Bidiyon jawabinsa a kasa: https://www.tiktok.com/@abuyesmeenherbalmedicine/video/7565232798823484680?_t=ZS-90rqW9rfm1g&_r=1
Akwai wadanda lokacin Buhari na kan Mulki sun ta yi masa dadin baki suna ce masa shi mutumin kirki ne amma yana sauka suka fara sukarsa>>Inji Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa

Akwai wadanda lokacin Buhari na kan Mulki sun ta yi masa dadin baki suna ce masa shi mutumin kirki ne amma yana sauka suka fara sukarsa>>Inji Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa

Duk Labarai
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya bayyana cewa, Akwai wadanda suka rika yabon tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari cewa shi mutumin kirki ne kuma babu shugaba Kamarsa a lokacin yana kan mulki. Yace amma yana sauka daga mulki kuma suka juya suna zaginsa. Ya bayyana hakane a wajan Taron Tunawa da marigayi Raymond Dokpesi mamallakin tashar talabijin ta AIT da gidan Radion Raypower da kamfanin Daar Communications. Ya jinjinawa marigayin da kokarin bude gidan Talabijin me zaman kansa na farko a Najeriya.