Thursday, April 10
Shadow

Duk Labarai

Ba zami iya biyan sama da Naira Dubu sittin(60,000) ba a matsayin mafi karancin Albashi>>Gwamnatin Tarayya

Ba zami iya biyan sama da Naira Dubu sittin(60,000) ba a matsayin mafi karancin Albashi>>Gwamnatin Tarayya

Siyasa
Gwamnatin tarayya ta jaddadawa Kungiyar Kwadago cewa, ba zata iya biyan Sama da Naira Dubu 60 ba a matsayin mafi karancin Albashi ba. Hakan na zuwane a Yau, Litinin da kungiyar ta kwadago ta fara yajin aikin sai baba ta gani. Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi ya bayyanawa kungiyar kwadagon da ma'aikatan gwamnatin tarayya cewa tafiya zuwa yajin aiki sabawa doka ne. Yace kuma zasu iya fuskantar daurin watanni 6 saboda tafiya yajin aikin. Ya bayyana cewa, har yanzu akwai tattaunawa tsakanin gwamnati da kungiyar kwadagon kuma ba'a kammala ba dan haka bai kamata kungiyar ta tafi yajin aiki ba. Ya roki kungiyar kwadagon data sake tunani kan wannan mataki data dauka inda yace bai kamata ba dan zai jefa da yawan 'yan Najeriya cikin halin kaka nikayi da wah...
Kalli Hoto: An dakatar da  Dan kwallo Kungiyar Monaco Mohamed Camara saboda yaki yadda yayi tallar Luwadi

Kalli Hoto: An dakatar da Dan kwallo Kungiyar Monaco Mohamed Camara saboda yaki yadda yayi tallar Luwadi

Duk Labarai
An dakatar da dan kwallon kungiyar Monaco Mohamed Camara Saboda yaki yadda yayi tallar Luwadi. An dai baiwa 'yan Kwallon kaya da tambarin Luwadi a jiki shine ya samu wani abu ya rufe nashi tambarin na luwadi dake jikin rigarsa. Dalilin hakane yasa aka dakatar dashi na tsawon wasanni 4. Camara wanda musulmi ne ya ki yadda yayi tallar luwadinne dan kare martabar addininsa.
Kwamishinan kananan hukumomi na jihar Bauchi Ahmad Jalam ya rasu sakamakon wani hatsarin mota da ya ritsa da shi a kan hanyar Misau-Darazo ranar Asabar a cewar gwamnatin jihar

Kwamishinan kananan hukumomi na jihar Bauchi Ahmad Jalam ya rasu sakamakon wani hatsarin mota da ya ritsa da shi a kan hanyar Misau-Darazo ranar Asabar a cewar gwamnatin jihar

Siyasa, Sokoto
Gwamna Bala na Jihar Bauchi Ya Halarci Jana'izar Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Allah Ya Karɓi Rayuwarsa A Daren Jiya Gwamna Bala Mohammed ya halarci Sallar Jana’izar Marigayi Alh Ahmad Aliyu Jalam Kwamishinan ƙananan Hukumomi na jihar Bauchi wanda ya Rasu a sakamakon hatsarin Mota Daga Bauchi Zuwa Jalam Gwamna Bala Mohammed ya bayyana shi a matsayin abokin aiki mai himma da kwazo da bayar da gudunmawar ci gaban Gwamnatin PDP a Jihar Bauchi. Ya ƙara da cewa Rasuwar Ahmed Aliyu Jalam ta haifar da zullumi tare da yin zaman makoki, yana mai rokon Allah ya ba shi AlJannati Firdausi, ya kuma baiwa iyalansa kwarin guiwar jure wannan babban rashi. Sai dai ya jajantawa ‘yan uwa da al’ummar Jalam a madadin Gwamnatin jihar da jam’iyyar PDP da daukacin al’ummar jihar Bauchi. Manyan ja...
Tsadar rayuwa: Tsohon Gwamnan jihar Sokoto Alhaji Aminu Waziri Tambuwal ya ce sai da suka yi wa ‘yan Nijeriya gargadi kar su sake yin kuskuren zaben jam’iyyar APC a zaben 2023

Tsadar rayuwa: Tsohon Gwamnan jihar Sokoto Alhaji Aminu Waziri Tambuwal ya ce sai da suka yi wa ‘yan Nijeriya gargadi kar su sake yin kuskuren zaben jam’iyyar APC a zaben 2023

Siyasa
Aminu Waziri Tambuwal ya ce sun gargaɗi ƴan Najeriya kan sake zaɓen APC a 2023. Tsohon gwamnan na Sokoto ya bayyana cewa halin ƙuncin da ake ciki a ƙasar nan yanzu, kin ɗaukar shawara ne ya kawo shi. Tambuwal ya bayyana hakane a wajan wani taron maau ruwa da tsaki na jam'iyyar a jihar Sokoto. Yace sun gayawa mutane, APC mulki kawai take aon samu ta ganta a ofis. Yace gashi yanzu sun samu amma sun rasa yanda zasu yi dashi.
Hoto: Hazikin Dansanda ASP Usman Lawal Tangible Ya Rasu A Katsina

Hoto: Hazikin Dansanda ASP Usman Lawal Tangible Ya Rasu A Katsina

Katsina, Tsaro
INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Hazikin Dansanda ASP Usman Lawal Tangible Ya Rasu A Katsina Allah Ya Yi Wa Hazikin Dansanda ASP Usman Lawal Tangible Rasuwa A Garin Malumfashi, Jihar Katsina Yau Lahadi. An Yi Jana'izarsa Kamar Yadda Addinin Musulunci A Gidansa Dake Bisije Babban Gida, Karamar Hukumar Malumfashi Jihar Katsina. Allah Ya Jikansa Da Rahama! Daga Jamilu Dabawa, Katsina
Yanzu-Yanzu: NLC zata ci gaba da yajin aiki gobe bayan zaman sulhu da Gwamnati ya gaza cimma matsaya

Yanzu-Yanzu: NLC zata ci gaba da yajin aiki gobe bayan zaman sulhu da Gwamnati ya gaza cimma matsaya

Siyasa
Rahoton da muke samu na cewa, Kungiyar Kwadago ta NLC zata ci gaba da yajin aikin da ta dauri aniya gobe, Litinin bayan zaman sulhu da gwamnati ya ci tura. A yau lahadi ne dai aka zauna tsakanin wakilan gwamnatin tarayya daga majalisar tarayya da kungiyoyin kwadago na NLC da TUC dan cimma matsaya kan mafi karancin Albashi, saidai an kare zaman ba tare da cimma matsaya ba. Da misalin karfe 5:50 PM ne dai aka fara zaman inda aka kareshi da misalin karfe 8:45 PM. Kakakin majalisar dattijai, Godswill Akpabio bayan taron, ya gayawa manema labarai cewa gwamnati ta roki kungiyoyin kwadagon kan su janye yajin aikin nasu amma suka kiya. Akpabio yace idan aka yi yajin aiki, abubuwa da yawa hadda asibitoci a kasarnan zasu tsaya cik. Duk da haka dai ya sake rokon kungiyoyin kwadagon da ...
‘Gwamnati za ta ci gaba da biyan ma’aikata ƙarin albashin wucin gadi’

‘Gwamnati za ta ci gaba da biyan ma’aikata ƙarin albashin wucin gadi’

Siyasa
Gwmanatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da bai wa ma'aikatan ƙasar ƙarin albashin wucin gadi - da ta fara biya wata shida ta suka gabata - har zuwa lokacin da za a kammala cimma matsaya kan mafi ƙarancin albashi a ƙasar. Cikin wani jawabi da ya yi wa manema labarai ranar Asabar a Abuja, ministan yaɗa labaran ƙasar, Mohammed Idris ya ce wa'adin mafi ƙarancin albashi da aka yi a shekarar 2019 ya ƙare ne ranar, 8 ga watan Afrilun 2024. Sai dai ministan bai bayyana adadin kuɗin da gwamnatin ke biya a matsayin albashin wucin gadin ba, to a baya gwamnatin ta ce za ta riƙa biyan ma'aikatan ƙarin naira 35,000 a kan albashinsu kowane wata har na tsawon wata shida. A ranar juma'a ne dai ƙungiyoyin ƙwadogon ƙasar suka ce za su tsunduma yajin aiki daga gobe Litinin, kasancewar wa'adin ranar 31...

NDLEA ta kama muggan ƙwayoyi na naira biliyan 2.1 a Legas da Fatakwal

Tsaro
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA ta ce jami'anta sun samu nasarar kama muggan ƙwayoyin da kuɗinsu ya kai kimanin naira biliyan 2.1 a biranen Legas da Fatakwal Cikin sanarwar nasarar mako-mako da hukumar ke fitarwa ta ce a ranar Juma'a 31 ga watan Mayu, jami'anta tare da haɗin gwiwar sauran jami'an tsaro a filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Legas suka kama wasu manyan jakankuna maƙare ƙulli 320 na tabar wiwi da nauyinta ya kai kilogiram 164.50 da aka yi safararta daga Canada. Hukumar ta ce ta kama mutumin da take zargi da safarar tabar - da aka yi ƙiyasin kuɗinta ya kai naira miliyan 960, - mai suna an kama Ughenu Nnaife Francis, wanda ya shaida wa jami'an hukumar cewa naira miliyan shida aka biya shi domin shigar da kayan Najeriya. NDLEA ta ...
NAFDAC ta yi gargaɗi kan amfani da sinadarin Sniper don taskance abinci

NAFDAC ta yi gargaɗi kan amfani da sinadarin Sniper don taskance abinci

Duk Labarai
Hukumar Kula da Inganci da Abinci ta Najeriya, NAFDAC ta gargaɗin 'yan ƙasar dangane da amfani da wani sinadarin adana abinci da ake kira Sniper. Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa shafinta na intanet ta ce tana ankarar da jama'a game da illar amfani da sinadarin wajen kare abinci daga lalacewa. Hukumar ta ce tun a shekarar 2019 aka haramta sayarwa da amfani da sinadarin da ke cikin ƙananan ƙwalabe. Yayin da aka sahalewa sayar da manyan kwabale musamman ga amintattun masu samar da magungunan ƙwari ga manoma. A baya-bayan nan ne dai wani bidiyo da ya yaɗu a shafukan sada zumunta a ƙasar ya nuna yadda wasu ke amfani da sinadarin wajen adana nau'o'in abinci, kamar kifi da wake da wasunsu. Yayin da take mayar da martani kan bidiyon shugabar hukumar Farfesa Mojisola Adeyeye...