Friday, March 20
Shadow

Duk Labarai

Sanatan Amurka ya gabatar da kudirin dokar Hukunta wasu ‘yan Najeriya da jihohin Arewa 12 dake amfani da dokar shari’ar Musulunci

Sanatan Amurka ya gabatar da kudirin dokar Hukunta wasu ‘yan Najeriya da jihohin Arewa 12 dake amfani da dokar shari’ar Musulunci

Duk Labarai
Sanatan Amurka, Ted Cruz wanda shine ya kai kudirin dokar da ta saka Najeriya cikin jerin kasashen da Amurkar ke sakawa ido bisa zargin anawa Kiristoci khisan Kyiyashi a yanzu kuma ya sake kai wani Kudirin dokar majalisar kasar. Ted Cruz ya godewa shugaban kasa, Donald Trump kan matakin da ya dauka akan Najeriya inda yace a baya lokacin mulkin Trump na farko, ya saka Najeriya cikin kasashen da Amurka zata rika sakawa ido amma tsohon shugaban kasar, Biden ya cireta. Saidai yace ya ji dadi da a yanzu Trump ya dawo da Najeriya cikin kasashen da Amurka zata rika sakawa ido. Yace a yanzu ya sake gabatar da wata sabuwar kudirin doka da zata hukunta wasu 'yan Najeriya da ake zargi da hannu wajan Muzgunawa Kiristoci sannan ya ce zakuma a dauki hukunci kan jihohi 12 na Arewa dake amfani da...
Abubuwa na ci gaba da kankama: Sojojin Amurka sun mikawa shugaba Trump kalar khare-kharen da suke son kawowa Najeriya

Abubuwa na ci gaba da kankama: Sojojin Amurka sun mikawa shugaba Trump kalar khare-kharen da suke son kawowa Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa sojojin kasar Amurka sun mikawa shugaban kasar kalar Hare-haren da suke son kawowa Naira. Sun mika masa tsare-tsaren hare-haren guda biyu, na farko yanayi ne me tsanani, sai matsaka kaici sai kuma me sauki. Yanayi me tsanani shine kawo jirgin ruwan yaki na Amurka kusa da Najeriya inda za'a rika aiko da jiragen yaki suna luguden wuta musamman a Arewacin Najeriya. Yanayi matsakaici shine Amurkar ta rika aiko da jirage marasa matuka da zasu rika kaiwa 'yan Bindiga hari. Yanayi me sauki kuma shine goyon bayan sojojin Najeriya da bayanan sirri da kuma aiki tare wajan kaiwa 'yan Bindigar hari. Zuwa yanzu dai ba'a san wanne shugaban kasar Amurkar zai dauka ba.
Trump zai zo ne ya sake Bhautar damu kawai amma babu wata maganar Mhuzghunawa Kiristoci>>Inji Fasto Elijah Ayodele

Trump zai zo ne ya sake Bhautar damu kawai amma babu wata maganar Mhuzghunawa Kiristoci>>Inji Fasto Elijah Ayodele

Duk Labarai
Shahararren Fasto Elijah Ayodele ya bayyana cewa ba maganar kisan kiyashi da aka ce anawa Kiristoci ne zai kawo Trump Najeriya ba, Satar ma'adanai ne zai kawoshi da kuma lalata kasar. Faston ya bayyana hakane a cocinsa yayin da yake wa'azi. Yace kuma ba Najeriya kadai Trump zai lalata ba idan ya kawo harin, hadda sauran kasashen Afrika za'a sake bautar damune. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1986097914918126033?t=8zpdqnO5vDOMIGJYcx1qFA&s=19
Zamu sayar da matatun man fetur na kasarnan>>Gwamnatin Tarayya

Zamu sayar da matatun man fetur na kasarnan>>Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana aniyar sayar da matatun man fetur mallakin Gwamnati, watau na Kaduna, Fatakwal, da Warri. Gwamnatin tace zata yi hakanne dan inganta aikin matatun da kuma jawo masu zuba jari Najeriya. Babban me baiwa shugaban kasar shawara akan makamashi, Olu Verheijen ce ta bayyana hakan a wajan wani taro a Kasar UAE. Matatun man fetur din na Najeriya sun lakume makudan kudade wanda aka ware dan gyarasu amma har yanzu basu aiki yanda ya kamata.
Majalisar Jihar Kano ta mayar da Yaren Hausa a matsayin wanda za’a rika amfani dashi wajan koyar da dalibai a makarantun Firamare da karamar Sakandare

Majalisar Jihar Kano ta mayar da Yaren Hausa a matsayin wanda za’a rika amfani dashi wajan koyar da dalibai a makarantun Firamare da karamar Sakandare

Duk Labarai
Majalisar Jihar Kano ta mayar da yaren Hausa a matsayin yaren da za'a rika amfani dashi wajan koyar da dalibai a makarantun Firamare da karamar Sakandare. Majalisar ta aiwatar da wannan doka ne ranar 5 ga watan Nuwamba. Hakanan Kwamitin majalisar dinkin Duniya na UNESCO ya amince da wannan mataki saboda karfafa Amani da harshen uwa.
Majalisar Tarayya zata yi dokar tilasta Amfani da motoci masu amfani da wutar Lantarki kadai

Majalisar Tarayya zata yi dokar tilasta Amfani da motoci masu amfani da wutar Lantarki kadai

Duk Labarai
Majalisar Dattawan Najeriya ta yi wa ƙudirin dokar amfani da ababen hawa masu amfani da lantarki. Ƙudirin mai taken Electric Vehicle Transition and Green Mobility Bill 2025, Sanata Orji Uzor Kalu (daga jihar Abia) ne ya gabatar da shi, wanda ke neman ɗora Najeriya kan "hanyar kyautata muhalli". Mista Kalu ya ce dokar "za ta taimaka wa ɓangaren ƙera ababen hawa, da makamashi, da ƙirƙire-ƙirƙire, da kuma samar da ayyukan yi". "Dokar ta ba da damar yafe haraji, da harajin shigo da kaya, da harajin kan hanya, da bayar da tallafi ga masu amfani da motoci masu amfani da lantarki da masu samar da su," in ji shi. Ta kuma tilasta kakkafa tashoshin caji a duka gidajen mai da ke faɗin ƙasar.
A karo na 4, Trump ya sake nanata cewa ba zai kauda ido kan Chin Khashin da akewa Kiristoci a Najeriya ba

A karo na 4, Trump ya sake nanata cewa ba zai kauda ido kan Chin Khashin da akewa Kiristoci a Najeriya ba

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump a karo na 3 ya sake maimaita cewa, ba zai zuba ido yana kallon Irin kokarin karar da kiristoci da ake yi a Najeriya ba. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da shafin Fadar White House ta wallafa. Trump yace ba lallai ne 'yan Najeriyar su ji dadin matakin da zai dauka ba amma ba zai zuba ido ba. Yace bama a Najeriya ba kadai, dama duka Duniya duk inda ake kokarin karar da Kiristoci zasu kai dauki. https://twitter.com/WhiteHouse/status/1986195249769697516?t=itL37G4-FmScFF5ayc1lfg&s=19
Muma bama son Kharin da America zata kawo, Maimakon haka ta taimaka mana a yi zaben jin ra’ayi dan a raba Najeriya a bamu kasar mu>>Inji Kungiyar Inyamurai ta Ohanaeze Indigbo

Muma bama son Kharin da America zata kawo, Maimakon haka ta taimaka mana a yi zaben jin ra’ayi dan a raba Najeriya a bamu kasar mu>>Inji Kungiyar Inyamurai ta Ohanaeze Indigbo

Duk Labarai
Itama dai Kungiyar Ohanaeze Indigbo reshen matasa,OYC ta bayyana cewa, bata son kawo harin da kasar Amurka zata yi zuwa Najeriya. Kungiyar tace maimakon haka, tana neman kasar Amurka ta taimaka musu a gudanar da zaben jin ra'ayi dan a raba Najeriya a basu kasarsu. Kungiyar ta bakin shugabanta, Comrade Igboayaka O. Igboayaka tace ba ita kadai bace hadda kungiyar Jihohin dake tsakiyar Najeriya duk suna neman a yi zaben ba raba gardama dan a raba kasarnan.
Kalli Bidiyon yanda Sabon Magajin garin New York City, na kasar Amurka, Zohran Mamdani ke karatun Qur’ani

Kalli Bidiyon yanda Sabon Magajin garin New York City, na kasar Amurka, Zohran Mamdani ke karatun Qur’ani

Duk Labarai
A wani Bidiyo dake ta yawo a kafafen sada zumunta, an ga Sabon Magajin Garin New York City, dake Kasar Amurka, Zohran Mamdani na karatun Qur'ani. Zohran Mamdani dai ya lashe zaben magajin garin New York City ne ranar Talata. Kuma hakan na zuwane duk da yake cewa shugaban kasar Amurka, Donald Trump baya sonsa. https://www.tiktok.com/@americas.muslim.network/video/7568927947562782007?_t=ZS-919PCoRieWX&_r=1