Tuesday, July 14
Shadow

Duk Labarai

Kungiyar Tuntuba ta Arewa, ACF tace a yiwa Tshàgyèràn Dhàjì irin Afuwar da akawa Tshàgyèràn Neja Delta

Kungiyar Tuntuba ta Arewa, ACF tace a yiwa Tshàgyèràn Dhàjì irin Afuwar da akawa Tshàgyèràn Neja Delta

Duk Labarai
Kungiyar Tuntuba ta Arewa, ACF ta bukaci a yiwa Tshàgyèràn Dhàjì irin afuwar da akawa tsageran Neja Delta. Shugaban kungiyar, Bashir Dalhatu ya bayyana haka a wata hira da kafar Arise TV suka yi dashi. Ya bayyana cewa, afuwar da akawa 'yan Neja Delta tasa an dauki nauyin su sun yi karatu sun zo sun zama masu amfanar da al'umma. Yace hakanan wata matsala da ake fuskanta da irin wadanan mutane itace yanda suke rayuwa babu kayan more rayuwa irin wadanda ake dasu a birane. https://twitter.com/TheYorubaTimes/status/1994415313681568091?t=f47xkBytkWl6iTcdVrhL9w&s=19
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon yanda Khàrìn da Tshàgyèràn Dhàjì suka kaiwa Shingen tsaro na jami’an Immigration a jihar Kebbi, abin ba Kyàn Gànì

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon yanda Khàrìn da Tshàgyèràn Dhàjì suka kaiwa Shingen tsaro na jami’an Immigration a jihar Kebbi, abin ba Kyàn Gànì

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kebbi sun bayyana cewa 'yan tà'àddà sun kaiwa wani shingen jami'an kula da shige da fici na Immigration hari. Sun bankawa shingen wuta, hadda masallacin dake wajan aun Qonashi. A cikin Bidiyon an ga gawar daya daga cikin mutanen dake wajan na ci da wuta. https://twitter.com/ogundamisi/status/1994455087360430193?t=VmAO9ni5WM0O-_i2fhYrrQ&s=19 Lamarin ya farune a Bakin Ruwa dake karamar hukumar Bagudu. Rahotanni sun ce mutane 3 ne suka rasu a harin.
Tsohon babban lauyan Gwamnati Abubakar Malami yace EFCC sun sakeshi bayan yi masa tambayoyi

Tsohon babban lauyan Gwamnati Abubakar Malami yace EFCC sun sakeshi bayan yi masa tambayoyi

Duk Labarai
Tsohon Babban lauyan Gwamnatin tarayya, Abubakar Malami wanda a jiya yace hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC sun gayyaceshi, yace bayan kammala masa tambayoyi, sun sakeshi. Ga sakon da ya wallafa a shafinsa: "Dangane da alkawarina na ci gaba da sanar da ’yan Najeriya game da gayyatar da EFCC ta yi mini, ina mika godiya ga Allah bisa bani ikon fitowa cikin aminci. Tattaunawar ta kasance mai kyau, kuma na samu fitowa, haka zalika an sake sanya wani sabon lokaci domin ci gaba da tattaunawa yayin da gaskiyar da ta shafi ƙagaggun zarge-zargen da aka yi a kaina ke ci gaba da bayyana. ABUBAKAR MALAMI, SAN, CON" https://twitter.com/aamalamiSAN/status/1994551164222754985?t=cD1knqyErDqSOypEY51PfQ&s=19
Jikina yana Bari, inason in Tambayi Ahmed Musa ya ban kyautar Naira Miliyan 10>>Inji Mansurah Isah

Jikina yana Bari, inason in Tambayi Ahmed Musa ya ban kyautar Naira Miliyan 10>>Inji Mansurah Isah

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa kuma Tsohuwar matar Sani Musa Danja, Mansurah Isah ta bayyana cewa tana rokon Tauraron kwallon Najeriya, Ahmed Musa ya bata kyauta Naira Miliyan 10. Ta roki masoyan ta a kafafen sada zumunta dasu tayata rokon Ahmed Musa ya bata wannan kyauta. Ta yi alkawarin cewa idan ya bata, zata baiwa mutane kyautar Naira Miliyan daya daga ciki.
Gwamnatin Kano na neman a kama Ganduje, saboda yunkurin kafa kungiyar tsaro ta sa kai

Gwamnatin Kano na neman a kama Ganduje, saboda yunkurin kafa kungiyar tsaro ta sa kai

Duk Labarai
Majalisar zartaswar jihar Kano ta yi kira da a gaggauta gudanar da bincike tare da kama tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa wasu kalamai da ta bayyana a matsayin tsokana da kuma tada zaune tsaye kan matsalar tsaro a jihar. Hakan ya biyo bayan tattaunawa ne a taron majalisar zartarwa karo na 34 da aka gudanar a ranar Alhamis a gidan gwamnatin jihar Kano, inda ƴan majalisar suka yi nazari kan kalaman Ganduje da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin na baya-bayan nan, inda suka yi zargin cewa Kano na kara fuskantar matsalar ƴan fashi da kuma bayyana shirin ɗaukar mutane 12,000 aikin ƴan sandan rundunar tsaro mai suna Khairul Nas. Da yake yiwa manema labarai ƙarin haske game da sakamakon taron a ranar Juma’a, kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim...
Kirista Grace ta ce Kalaman Baffa Hotoro akan Sheikh Dahiru Usman Bauchi basu kamata ba

Kirista Grace ta ce Kalaman Baffa Hotoro akan Sheikh Dahiru Usman Bauchi basu kamata ba

Duk Labarai
Wata Kirista Grace Charles ta bayyana rashin jin dadin kalaman da Baffa Hotoro yayi akan Marigayi, Sheikh Dahiru Usman Bauchi. Tace kalaman basu dace ba lura da cewa, Sheikh Dahiru Bauchi ya rasu. Tace duk me bin Baffa Hotoro ba zai shiga Aljannah ba https://www.tiktok.com/@gracecharles792/video/7577801632377769224?_t=ZS-91mosZIAbVB&_r=1 Baffa Hotoro na daga cikin malaman da suka soki Dahiru Usman Bauchi duk da ya rasu wanda wasu ke ganin hakan bai dace ba.
Ji ta’asar da zaratan Tshàgyèràn Dhàjì 3 sukawa wata karamar yarinya a jihar Naija

Ji ta’asar da zaratan Tshàgyèràn Dhàjì 3 sukawa wata karamar yarinya a jihar Naija

Duk Labarai
Wasu 'yan Bindiga 3 sun yiwa karamar yarinya me shekaru 13 fyàdè a kauyen Kudodo dake yankin Galko na karamar hukumar Shiroro jihat Naija. Wani dan jam'iyyar APC a jihar Naija, Babangida Wassa Kudodo ne ya bayyana hakan. Yace lamarin ya nuna irin yanda rashin tsaro ke kara munana a jihar. Tuni aka kai yarinyar Asibiti dan kula da lafiyarta. Jihar Naija na daga cikin jihohin Arewa masu fama da matsananciyar matsalar tsaro.