Friday, January 23
Shadow

Duk Labarai

Allah Sarki: Kalli Bidiyonsa inda ya fashe da kuka bayan da ya dauki kudin da ya dade yana tarawa ya buga càcà cewa Manchester City zata ci Manchester United

Allah Sarki: Kalli Bidiyonsa inda ya fashe da kuka bayan da ya dauki kudin da ya dade yana tarawa ya buga càcà cewa Manchester City zata ci Manchester United

Duk Labarai
Wannan wani dan cacar Bet Naija ne da ya buga caca cewa Manchester City zata ci Manchester United saidai kuma hakan bata faru ba ya tafka Asara. Manchester United ce ta yi nasara a wasan. An ganshi yana ta kuka bayan da aka tashi wasan. https://twitter.com/i/status/2013194442090352728
Kalli Bidiyon: Wani dan APC ya bugi kirjin cewa babu wanda zai iya kayar da Tinubu zabe a 2027

Kalli Bidiyon: Wani dan APC ya bugi kirjin cewa babu wanda zai iya kayar da Tinubu zabe a 2027

Duk Labarai
Wannan wani dan APC ne da ya dauki hankula bayan ikirarin da yayi cewa, babu wanda zai iya kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben 2027. Ya bayyana cewa an ware makudan kudade inda kowane me zabe za'a bashi Naira dubu shirin da ya zabi Tinubu. Yace Tinubu na da Gwamnoni 31 a karkashinsa dan haka a yanzu dai babu wanda zai iya kayar dashi zabe. https://twitter.com/i/status/2013287914369642732
Kalli Bidiyon: Abinda me wasan Barkwanci, Brother Shaggy yayi bayan da Senegal ta ci kofin AFCON a Morocco da ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Abinda me wasan Barkwanci, Brother Shaggy yayi bayan da Senegal ta ci kofin AFCON a Morocco da ya dauki hankula

Duk Labarai
Dan wasan Barkwanci na Najeriya, Brother Shaggy da wata abokiyarsa da suke a filin wasan kasar Morocco yayin da Senegal ta dauki kofin AFCON, sun yi wani abu da ya dauki Hankula. An gan su suna nuna bacin ransu bayan wasan alamar suna taya kasar Morocco Alhini. Saidai a zahirin gaskiya suna jin dadi ne a ransu, Dalilin da yasa suke nuna Alhini a zahiri saboda suna zagaye da magoya bayan Morocco. Lamarin ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta https://twitter.com/i/status/2013144134664548675
Kalli Bidiyon: Sojar Amurka ta bayyana Nawa ake biyansu Albashi kuma ta bayyana nawa ake biyan Danginsu idan suka rigamu gidan gaskiya a bakin aiki

Kalli Bidiyon: Sojar Amurka ta bayyana Nawa ake biyansu Albashi kuma ta bayyana nawa ake biyan Danginsu idan suka rigamu gidan gaskiya a bakin aiki

Duk Labarai
Wata sojar Amurka 'yar Asalin Najeriya ta bayyana nawa akw biyansu Albashi duk wata. Tace ana biyansu dala $4000 ne duk wata a matsayin albashi, Kwatankwacin Naira Miliyan 5,740,000. Sannan tace idan suka rasa ransu a wajan aikin, akan ba iyalansu dala $500,000, kwatankwacin Naira Miliyan 717,500,000 Ta bayyana hakane a wani Live da suka yi ita da Peller. Lamarin ya dauki hankula sosai. https://twitter.com/i/status/2013492598824939547
Kalli Bidiyon ganawar da shugaba Tinubu yayi da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

Kalli Bidiyon ganawar da shugaba Tinubu yayi da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da Gwamnan kano, Abba Kabir Yusuf a fadarsa dake Abuja a yammacin ranar Litinin. Ganawar tasu na zuwane yayin da ake ta rade-radin cewa, Gwamna Abba Kabir Yusuf zai koma jam'iyyar APC. A sanarwar da me magana da yawun gwamnan, Sunusi Dawakin Tofa ya fitar, yace gwamna Abba ya gabatarwa da shugaba Tinubu tsare-tsaren gwamnatinsa ne da suka hada da samar da Tsaro, da Ayyukan ci gaba da kuma Hada kai da Gwamnatin tarayya. A sanarwar da Shugaban jam'iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas ya fitar, yace a yau, Talata ne Gwamna Abba Kabir Yusuf zai karbi katinsa na zama dan jam'iyyar APC. https://twitter.com/i/status/2013278927289012474