Wednesday, March 11
Shadow

Duk Labarai

Babu Wani dadi da ake ji a matsayin matar Gwamna Sai Wahala>>Inji Matar Tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai

Babu Wani dadi da ake ji a matsayin matar Gwamna Sai Wahala>>Inji Matar Tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai

Duk Labarai
Matar tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai ta bayyana amincewa da kalaman gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Radda. Dikko ya bayyana cewa babu wani jin dadi a zama gwamna, mutane na ganin kamar jin dadi suke amma a zahiri wahala suke sha. Ya kara da cewa ko da kasashen waje da suke zuwa, saidai ai ta taruka ba shakatawa suke zuwa yi ba. Hajiya Hadiza da take martani akan kalaman na Gwamnan Katsina, ta bayyana cewa, shima mukamin matar Gwamna haka yake. https://twitter.com/i/status/2010824002781028737
Kusan duk manyan ma’aikatun da ake samun kudaden shiga a Najeriya Bayerabene shugabansu inji Hamma

Kusan duk manyan ma’aikatun da ake samun kudaden shiga a Najeriya Bayerabene shugabansu inji Hamma

Duk Labarai
Me sharhi akan Al'amuran yau da kullun, Hamma, ya yi zargin cewa, kusan duk manyan ma'aikatun da ake samun kudaden shiga, Bayerabene ke shugabantarsu. Ya zano ma'aikatun kamar haka, CBN, NRS, Customs, NNPC da sauransu inda yace duka Yarbawa ne shuwagabanninsu. Ya bayyana cewa, a kowace kabila a Najeriya akwai kwararru, me yasa sai Yarbawa kawai ake baiwa mukami? https://twitter.com/i/status/2010977805069107473 i
Zaben da ‘yan Najeriya ke yi bashi ke sa mutum yaci zabe ba>>Aminu Waziri Tambuwal

Zaben da ‘yan Najeriya ke yi bashi ke sa mutum yaci zabe ba>>Aminu Waziri Tambuwal

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya bayyana cewa, zaben da 'yan Najeriya ke yi bashi ke sa mutum ya ci zabe ba. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV. Ya bayyana cewa, 'Yan siyasa na yin dukkan abinda suke tunani da zai basu nasara. Hakanan suma jami'an zabe wajan tattarawa da aika sakamakon zaben akan samu wasu suna yin magudi. Tambuwal yace yana goyon bayan duk wani canji da za'a kawo a harkar zabe wanda zai inganta harkar. https://twitter.com/i/status/2010954988747702612
Kalli Bidiyon: Wani dan Najeriya da ya je kallon wasan AFCON a kasar Morocco na mamakin cewa a karin farko ya ga an dauke wutar lantarki a kasar

Kalli Bidiyon: Wani dan Najeriya da ya je kallon wasan AFCON a kasar Morocco na mamakin cewa a karin farko ya ga an dauke wutar lantarki a kasar

Duk Labarai
Wani dan Najeriya da ya je kasar Morocco kallon wasan AFCON ya bayyana mamakinsa bayan ganin a karon farko an dauke wuta a kasar. Ya rika ihun cewa a karin farko NEPA sun dauke wuta a kasar ta Morocco. Wasu dai sun rika bayyana cewa hakan alamar Nasara ce ga Super Eagles. https://twitter.com/i/status/2010823217187893698
An kama daliban jami’ar AAU dake jihar Edo su 50 saboda sun yi zàngà-zàngàr kokawa da matsalar tsaro

An kama daliban jami’ar AAU dake jihar Edo su 50 saboda sun yi zàngà-zàngàr kokawa da matsalar tsaro

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa an kama daliban jami'ar AAU kusan 50 saboda sun yi zanga-zangar neman kawo karshen matsalar tsaro. Bidiyon daliban cunkushe a cikin mota ya dauki hankula sosai inda aka gansu jami'an tsaro sun kamasu sun tafi dasu zuwa kotu. Lamarin ya dauki hankula inda akai ta muhawara akai. https://twitter.com/i/status/2010815658578047091