Saturday, December 13
Shadow

Duk Labarai

A karshe dai kasar Burkina Faso ta sako sojojin Najeriya 11 da take rike dasu bayan da jirginsu yayiwa kasar Kutse

A karshe dai kasar Burkina Faso ta sako sojojin Najeriya 11 da take rike dasu bayan da jirginsu yayiwa kasar Kutse

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Burkina Faso na cewa, kasar ta saki sojojin Najeriya 11 da take rike dasu bisa zargin jirgin saman da suke ciki ya shiga sararin samaniyar kasar ba tare da izini ba. An saki sojojin Najeriyar ne ranar Talata. A baya dai sojojin dake mulkin kasar ta Burkina Faso sun ce jirgin sojin Najeriya me lamba C-130 ya shiga sararin samaniyar kasarsu ba tare da izini ba. Saidai hukumomin sojin sama na Najeriya sun ce jirgin ya samu tangarda ne shiyasa yayi saukar gaggawa a kasar ta Burkina Faso.
Juyin Mulki ba zai taba yiyuwa ba a Najeriya inji Maj-Gen. Enenche (rtd)

Juyin Mulki ba zai taba yiyuwa ba a Najeriya inji Maj-Gen. Enenche (rtd)

Duk Labarai
Tsohon sojan Najeriya, Maj-Gen. Enenche (rtd) ya bayyana cewa, Juyin Mulki ba zai taba yiyuwa a Najeriya ba, yace dalili kuwa shine sojojin yanzu basu da zuciyaryi. Yace an rika an basu horo akan rashin yin juyin mulkin. Yace shiyasa ma shi idan yaji ana cewa wai za'a yi juyin mulki hankalinsa baya tashi dan yasan babu abinda zai faru. Ya bayyana hakane a tashar Channels TV a wata hira da aka yi dashi.
Ba gayyar sodi tasa na aika sojoji kasar Benin Republic ba, rokona suka yi>>Fadar Shugaba Tinubu

Ba gayyar sodi tasa na aika sojoji kasar Benin Republic ba, rokona suka yi>>Fadar Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Fadar Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana cewa, ba haka kawai gayyar sodi tasa shugaban kasar ya aika da sojoji kasar Benin Republic ba. Yace kasar ta Benin Republic ce ta bukaci hakan. Ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Bayo Onanuga. Hakan na zuwane jim kadan bayan da shugaban ya aikawa majalisar Dattijai bukatar aikawa da sojoji kasar Benin Republic inda kuma suka amince.
Da Duminsa: ECOWAS ta saka dokar ta baci a Afrika ta yamma saboda yawaitar Jhuyin mulki

Da Duminsa: ECOWAS ta saka dokar ta baci a Afrika ta yamma saboda yawaitar Jhuyin mulki

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar Hadin kan kasashen Afrika ta yamma, ECOWAS ta saka dokar ta baci saboda yawaitar juyin mulki a kasashen Yankin Shugaban kungiyar, Omar Touray ne ya bayyana hakan a taron kungiyar da aka yi a babban birnin tarayya Abuja. A kwanakin bayane sojojin kasar Guinea Bissau suka yi juyin mulki hakanan sojojin kasar Benin Republic suma sun yi yunkurin Jhuyin mulkin duk da bai sau nasara ba
Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikewa majalisa Bukatar su amince masa ya aika da Sojoji kasar Benin Republic

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikewa majalisa Bukatar su amince masa ya aika da Sojoji kasar Benin Republic

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aikewa da majalisar Dattijai da bukatar su amince masa ya aika da sojoji kasar Benin Republic. Kakakin Majalisar Dattijai Godswill Akpabio ya karanta wasikar da shugaba Tinubun ya aikawa majalisar. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da shugaba Tinubu ya aike da sojoji kasar ta Benin Republic suka hana juyin Mulki da sojojin kasar suka so yi.
Bidiyo: Wannan Mutumin yace wai an masa Wahayin ya kera jirgin ruwa saboda ranar Kirsimeti Duniya zata tashi

Bidiyo: Wannan Mutumin yace wai an masa Wahayin ya kera jirgin ruwa saboda ranar Kirsimeti Duniya zata tashi

Duk Labarai
Wani mutum dan kasar Ghana yace wai an masa wahayi cewa nan da ranar Kirsimeti, 25 ga watan Disamba, Duniya zata tashi. Yace wai an Umarceshi da ya kera jirgin ruwa irin na Annabi Nuhu(AS). Yace yan kan kera Jiragen guda 8 manyamanya wadanda kowanensu zasu dauki mutane akalla Miliyan 600. Ya nemi duk wanda suka yadda dashi su zo su tayashi aiki. A cewarsa wai za'a yi ruwa irin na Dufana. https://www.tiktok.com/@ebonoah/video/7554531904482069771?_t=ZS-924jLzUhgZt&_r=1