Saturday, February 14
Shadow
Kalli Bidiyon: Abinda dan Atiku, Abba Atiku da ya koma APC yace akan mahaifinsa ya baiwa mutane mamaki

Kalli Bidiyon: Abinda dan Atiku, Abba Atiku da ya koma APC yace akan mahaifinsa ya baiwa mutane mamaki

Duk Labarai
Dan Atiku Abubakar, Abba Atiku da ya koma jam'iyyar APC ya dauki hankula bayan jawabin daya gabatar na farko bayan komawarsa APC. An ga Bidiyon sa yana cewa, duk wani me goyon bayansa ko wanda suke karkashinsa su daina goyon mahaifinsa, Atiku Abubakar su koma goyon bayan shugaba Tinubu. https://twitter.com/i/status/2013136856678879496 Saidai wani abu na daban da ya kara daukar Hankula akan Abba Atiku shine yanda aka ga yana magana, baya iya tsayawa da kyau. Da yawa sun yi zargin cewa yana shaye-shaye.
Ji dalilin da ya hana Abba Kabir Yusuf komawa jam’iyyar APC

Ji dalilin da ya hana Abba Kabir Yusuf komawa jam’iyyar APC

Duk Labarai
A yayin sa labarai suka bayyana cewa, gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf zai koma jam'iyyar APC daga NNPP, har yanzu komawar tasa bata tabbata ba. Sau biyu kenan ana daga shirin komawar Abba APC saboda wata matsala. Rahoton yace, Dalilin da ya hana abba komawa jam'iyyar APC shine bukatun da ya gabatarwa da jam'iyyar ta APC wanda ita uma har yanzu bata amince dasu ba. Jaridar Thisday tace Gwamna Abba ya bukaci APC ta bashi tabbacin samun tikitin takara a 2027 ba tare da hamayya ba, hakanan ya bukaci a bashi damar aika sunayen wadanda za'a baiwa Ministoci zuwa Gwamnatin tarayya. Saidai wani dake kusa da Tsohon gwamnan jihar kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa akwai gwamnoni da yawa da suka koma APC wadanda basu nemi wadannan bukatu ba. ...
Kungiyar Goyon bayan Atiku sun kori dan Atikun, watau Abba Atiku da ya koma jam’iyyar APC

Kungiyar Goyon bayan Atiku sun kori dan Atikun, watau Abba Atiku da ya koma jam’iyyar APC

Duk Labarai
Kungiyar goyon bayan Atiku Abubakar, me suna Atiku Haske Organization ta kori dan Atikun me suna Abba Atiku bayan da ya koma jam'iyyar APC. Abba ya canjawa kungiyar suna zuwa ta goyon bayan Tinubu saidai shugaban kungiyar, Musa Bakari ya ce dan Atiku bai da hurumin canjawa kungiyar suna ko ya bayar da umarni ga mabiya kungiyar. Yace sune suka kafa wannan kungiyar kuma shahadar yi mata rijista na hannunsu. Yace dan haka sune masu gudanarwar kungiyar ba dan Atikun ba. Dan haka yace sun koreshi daga kungiyar.
A shekarar 2020, ya sayi kayan abinci na Naira dubu ashirin da biyar, a shekarar 2026 ya koma ya sake sayen irin wadannan kayan abincin komai da komai saidai farashinsu ya koma Naira dubu dari da arba’in da bakwai

A shekarar 2020, ya sayi kayan abinci na Naira dubu ashirin da biyar, a shekarar 2026 ya koma ya sake sayen irin wadannan kayan abincin komai da komai saidai farashinsu ya koma Naira dubu dari da arba’in da bakwai

Duk Labarai
Wannan wani dan Najeriya ne da a shekarar 2020 ya sayi kayan abinci akan Naira 25,000. Saidai a shekarar 2026 da muke ciki ya koma ya sake sayan kalar wadannan kayan abincin komai da komai saidai farashinsu ya karu zuwa Naira 147,000. Hakan na nufin farashin kayan ya karu da kusan kaso 6 kenan. Ya kuma wallafa rasit din abin a shafinsa na X. Lamarin dai ya dauki hankula sosai inda akai ta tattauna yanda farashin kayan masarufi ke kara tashi. https://twitter.com/i/status/2013142426169561153
Kalli Bidiyon abinda Sadio Mane yayi wanda ya taimakawa Senegal yin nasara da ake ta yaba masa

Kalli Bidiyon abinda Sadio Mane yayi wanda ya taimakawa Senegal yin nasara da ake ta yaba masa

Duk Labarai
A yayin da wasan Senegal da Morocco na jiya ya kusa zuwa karshe, An baiwa Morocco bugun daga kai sai me tsaron gida wanda baiwa 'yan wasan Senegal dadi ba. Hakan yasa 'yan wasan Senegal suka fita daga filin a matsayin wata hanya ta nuna fushinsu. Saidai Kyaftin dinsu, Sadio Mane ya tsaya inda ya rika kiransu su dawo cikin fili a ci gaba da wasa, hakan ya jawo masa yabo sosai. Kuma bayan dawowarsu sai suka sakawa Morocco kwallo 1 wadda hakan ya basu nasarar daukar kofin. https://twitter.com/i/status/2013024634082337009
Kalli Bidiyon: Dambarwar data faru tsakanin jami’an tsaron kasar Morocco da magoya bayan kasar Senegal da ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Dambarwar data faru tsakanin jami’an tsaron kasar Morocco da magoya bayan kasar Senegal da ya dauki hankula

Duk Labarai
An ga wata Dambarwa data faru tsakanin magoya bayan kasar Senegal da jami'an tsaron kasar Morocco. Bidiyon da ya watsu a kafafen sada zumunta ya nuna yanda dambarwar ta kasance inda akai ta dauki ba dadi, da yawa dai sun jinjinawa magoya bayan kasar ta Senegal. https://twitter.com/i/status/2013009957570949487
Kalli Bidiyon kokarin da golan Senegal yayi da ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon kokarin da golan Senegal yayi da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Golan Senegal Yehvan Diouf wanda ke wajan fili yayin da ake wasa, ya rikewa bokin aikinsa tsumman goge zufa ya hana ma'aikatan Filin wasan daukarsa. A wani Bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, an ga golan yana kokawa da ma'aikatan filin yayin da suke ta kokarin kwace tsumman daga hannunsa. https://twitter.com/i/status/2013065997125566495 A baya dai, An ga yanda ma'aikatan filin suka dauke tsumman na goge zufar golan Najeriya, Nwabali wanda hakan ya jawo cece-kuce sosai.