Wednesday, April 29
Shadow
Kalli Bidiyo: Yanda Shugaban Izala Sheikh Bala Lau ya janye Lasifika daga bakin Alaramma Ahmad Sulaiman yana tsaka da karanta Qur’ani ya tafi gaisawa da shugaba Tinubu ya jawo cece-kuce

Kalli Bidiyo: Yanda Shugaban Izala Sheikh Bala Lau ya janye Lasifika daga bakin Alaramma Ahmad Sulaiman yana tsaka da karanta Qur’ani ya tafi gaisawa da shugaba Tinubu ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
A ranar Juma'ar data gabata ne aka daura auren dan Sanata Abdulaziz Yari a Masallacin Sultan Bello Kaduna. Shugaban Izala,Sheikh Bala Lau ne ya ya gabatar da huduba kamin zuwan liman. Saidai a yayin da yake wa'azi, Alaramma Ahmad Sulaiman na ja masa baki, sai ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya shiga masallacin. Ai kuwa nan da nan Sheikh Bala lau ya janye lasifika daga bakin alaramma Ahmad Sulaiman yana tsaka da karatun Qur'anin ya tafi gaisawa da shugaba Tinubu. Hakan ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke ganin bai kamata ba. https://www.tiktok.com/@muhammadsunnahaljosawy/video/7552481590450900231?_t=ZS-8zvFbjBS0LA&_r=1
Kalli Bidiyo: Fasto da ya lura mata na zuwa cocinsa sanye da riga kawai babu rogar Mama a ciki ya raba musu rigar maman saidai yace ba zasu tafi da ita gida ba, da an gama zaman cocin su cire su aje mai kayansa

Kalli Bidiyo: Fasto da ya lura mata na zuwa cocinsa sanye da riga kawai babu rogar Mama a ciki ya raba musu rigar maman saidai yace ba zasu tafi da ita gida ba, da an gama zaman cocin su cire su aje mai kayansa

Duk Labarai
Wani fasto ya dauki hankula bayan da aka ga yana rabawa mata rigar mama. Faston ya bayyana rashin jin dadinsa ne da ganin yanda mata ke zuwa cocin nasa babu rigar mama. Dan hakane ya raba musu rigar maman amma yace ba zasu tafi da ita gida ba. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1969467628222661084?t=feabGIpcSzv_4kTqje1imw&s=19
Akwai yiyuwar Tinubu ba zai so sauka daga Mulki ba, zai so ci gaba da zama shugaban Najeriya har karshen rayuwarsa>>Inji El-Rufai

Akwai yiyuwar Tinubu ba zai so sauka daga Mulki ba, zai so ci gaba da zama shugaban Najeriya har karshen rayuwarsa>>Inji El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi gargadi cewa muddin 'yan Najeriya basu tashi tsaye ba suka yi abinda ya kamata a 2027 ba, to lallai Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai so ya zarce ya mulki Najeriya har iya tsawon rayuwarsa. El-Rufai ya kwatanta Abinda Tinubu ke son yi da irin mulkin shugaban kasar Kamaru, Paul Biya. El-Rufai yayi wannan maganane a yayin da Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya kai masa ziyarar jaje bayan tarwatsa taron ADC da aka yi a Kaduna. El-Rufai yace ko mulkin Soja bai ga ana yin irin kamar karyar da Gwamnatin Tinubu ke yi ba Dan haka yace dolene a hada kai.
Kalli Bidiyo: Iya Karshen Rashin Kunyane mutum yace baya neman komai wajan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)>>Inji Digital Imam

Kalli Bidiyo: Iya Karshen Rashin Kunyane mutum yace baya neman komai wajan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)>>Inji Digital Imam

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Digital Imam ya bayyana cewa, iya karshen rashin kunyane mutum yace baya neman komai wajan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Malam Yace ba da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Musuluncìn mutum baya cika. Yace kuma idan mutum ya isa yace Ashhadu An la'ilaha Ilallah ba tare da cewa, Ashhadu anna Muhammadu Rasulullah ba, yace musuluncinsa bai cika ba. https://www.tiktok.com/@digital_imaam/video/7551551643100138759?_t=ZS-8zuZYoENj1s&_r=1
Da na so zama shugaban kasa a karo na 3, nasan yanda zan yi in samu, babu wanda ya isa ya hanani>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Da na so zama shugaban kasa a karo na 3, nasan yanda zan yi in samu, babu wanda ya isa ya hanani>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Duk Labarai
Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya karyata rade-radin dake yawo cewa ya so ya sake zama shugaban Najeriya a karo na 3. Obasanjo ya bayyana hakane a wajan wani taro kan Dimokradiyya da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya shirya. Yace babu wanda zai iya cewa ya kirashi ya gaya mai cewa yana son zarcewa a karo na 3 akan mulki. Yace neman a yafewa Najeriya bashin da ake binta da yayi a zamanin mulkinsa, yafi neman zama shugaban kasa a karo na 3 wahala.