Saturday, December 6
Shadow
Hukumar Hisbah ta Kano ta kama mutane 25 inda namiji ke shirin auren Namiji a Kano

Hukumar Hisbah ta Kano ta kama mutane 25 inda namiji ke shirin auren Namiji a Kano

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta kama mutane 25 dake shirin kulla auren Namiji da Namiji. An kamasu ne a Fatima Event Center dake Hotoro ranar Lahadi. Mataimakin Kwamanda na Hisbah, Mujahedeen Aminudeen ne ya bayyana hakan ga manema labarai. Yace daga cikin wadanda aka kama akwai maza 18, mata 7. Yace sun samu bayanan sirri ne kan daura auren 'yan Luwadin.
Kalli Bidiyon: Duk masu min fatan in koma me kiba kamar yanda nake a baya, Ina Rokon Allah ya dora musu kibar>>Inji Hadiza Gabon

Kalli Bidiyon: Duk masu min fatan in koma me kiba kamar yanda nake a baya, Ina Rokon Allah ya dora musu kibar>>Inji Hadiza Gabon

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta magantu kan cece-kuce da ake yawan yi kan ramar da ta yi. Ta yi wannan bayanine a shirinta na Gabon Show wanda ke gudana a shafinta na YouTube. Gabon ta bayyana rashin jin dadin cece-kucen da ake yi akan ramar tata inda tace zabinta ne ta kasance da rama. https://www.tiktok.com/@talk_showw/video/7565219801795284245?_t=ZS-90rvlB7zRg1&_r=1
Kalli Bidiyon: Wallahi ‘yan Dariqa da kuke cewa Qafurai, ko ‘Yan Bindi’a sun fi ku Ahlussunah ilimi, Mafi yawancin ‘yan Ahlussunah Jahilaine sai ‘yan kadan>>Inji Malamin Izala

Kalli Bidiyon: Wallahi ‘yan Dariqa da kuke cewa Qafurai, ko ‘Yan Bindi’a sun fi ku Ahlussunah ilimi, Mafi yawancin ‘yan Ahlussunah Jahilaine sai ‘yan kadan>>Inji Malamin Izala

Duk Labarai
Malam wanda dan Izala ne ya caccaki masu kafurta 'yan darika da masu kiransu 'yan Bindi'a. Yace mafi yawancin Ahlussunah jahilai ne inda yace 'yan Dariqa sun fisu Ilimi. Kalli Bidiyon jawabinsa a kasa: https://www.tiktok.com/@abuyesmeenherbalmedicine/video/7565232798823484680?_t=ZS-90rqW9rfm1g&_r=1
Akwai wadanda lokacin Buhari na kan Mulki sun ta yi masa dadin baki suna ce masa shi mutumin kirki ne amma yana sauka suka fara sukarsa>>Inji Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa

Akwai wadanda lokacin Buhari na kan Mulki sun ta yi masa dadin baki suna ce masa shi mutumin kirki ne amma yana sauka suka fara sukarsa>>Inji Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa

Duk Labarai
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya bayyana cewa, Akwai wadanda suka rika yabon tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari cewa shi mutumin kirki ne kuma babu shugaba Kamarsa a lokacin yana kan mulki. Yace amma yana sauka daga mulki kuma suka juya suna zaginsa. Ya bayyana hakane a wajan Taron Tunawa da marigayi Raymond Dokpesi mamallakin tashar talabijin ta AIT da gidan Radion Raypower da kamfanin Daar Communications. Ya jinjinawa marigayin da kokarin bude gidan Talabijin me zaman kansa na farko a Najeriya.
Ji Kabakin Alherin da za’a baiwa manyan sojojin da shugaba Tinubu yawa ritayar dole, Dala $60,000, da Motar da Harsashi baya ratsata da Kuma Mota Prado Jeep

Ji Kabakin Alherin da za’a baiwa manyan sojojin da shugaba Tinubu yawa ritayar dole, Dala $60,000, da Motar da Harsashi baya ratsata da Kuma Mota Prado Jeep

Duk Labarai
Rahotanni sun ce Manyan sojojin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yawa ritaya zasu samu kudin sallama da motocin Alfarma. Daga cikin abubuwan da za'a basu kawai mota kirar SUV wadda harsashi baya hudata sai kuma wata Jeep kirar Prado Hakanan za'a rika musu gyaran wadannan motoci lokaci zuwa lokaci sannan za'a sai musu sabbi bayan shekaru 4. Hakanan duk shekara za'a rika basu Dala $20,000 na neman lafiya.
‘Yan Damfarar Yanar Gizo(Yahoo Boys) mutanene masu Bhasiyra bai kamata ana Zhaginsu ba, kamata yayi a jawo su jiki>>Inji Peter Obi

‘Yan Damfarar Yanar Gizo(Yahoo Boys) mutanene masu Bhasiyra bai kamata ana Zhaginsu ba, kamata yayi a jawo su jiki>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2023 a Labour Party Peter Obi ya bayyana cewa, masu damfarar yanar gizo, Wanda aka fi sani da Yahoo Boys mutanene masu basira. Yace ida aka kula dasu aka canja musu tunani zasu amfani ci gaban kasa. Ya bayyana hakane a Onitsha Jihar Anambra ranar Asabar. Ya yi kiran da a daina karfafa cin hanci da Rashawa a Najeriya.
Subhanallahi: Kalli Bidiyon inda wani Dan Dariqa ya jawo cece-kuce sosai bayan da yayi Ikirari Sheikh Tijjani yafi Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)

Subhanallahi: Kalli Bidiyon inda wani Dan Dariqa ya jawo cece-kuce sosai bayan da yayi Ikirari Sheikh Tijjani yafi Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)

Duk Labarai
Wani dan Darika ya jawo Muhawara me zafi sosai bayan da yayi ikirarin cewa Sheikh Tijjani Yafi Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya bayyana cewa, su akan karantarwar da aka dorasu kenan amma idan ya gane gaskiya zai canja https://www.tiktok.com/@buharimandemgy/video/7565017487750876423?_t=ZS-90r74ueAimG&_r=1