Saturday, April 25
Shadow

Amfanin tazargade

Magunguna
Amfanin Tazargade ( Artemisia) Ga Lafiyar Jikin Dan Adam TAZARGADE?? Tana daya daga cikin dadaddun ciyawoyin da ake amfani da su a bangarori mabambanta na kiwon lafiya, kuma ana sanyata a ruwan wanki domin fitar da karni ko wari da dai sauran su. Yanzu insha ALLAH za mu kawo muku wasu daga cikin amfanin da takeyi ga lafiyar mu, daga cikin abubuwan da take magancewa da yardar Allah su ne kamar haka: 1- Zazzabin cizon sauro, ko duk wani zazzabi na (Maleria). 2- yin Amai3- matsalar ciwon ciki.4- matsalar ciwon shanyewar barin jiki.5- matsalar ciwon Qoda6- Tana daidata jinin al’ada.7- Gubar Ciki8- Hawan Jini9- ciwon kai YADDA AKE AMFANI DA ITA:Asamo ganyen a nikeshi yazam gari karamin cokali safe rana dare so uku a ranaA kunu Ko Koko Ko Yaughourt 2- Mai shayarwa3- Mai ciwo...
Gwamnatin Jihar Kano ta saka dokar hana zirga-zirga na tsawon awanni 24

Gwamnatin Jihar Kano ta saka dokar hana zirga-zirga na tsawon awanni 24

Duk Labarai
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ne ya ayyana dokar a taron manema labarai da ke gudana a gidan gwamnati a halin yanzu. Ya ce an saka dokar ne domin a dakile sace-sace da fashe-fashen kayan gwamnati da na al'umma da wasu ɓatagari ke yi a ƙarƙashin zanga-zanga. Ya ce wasu ƴan siyasa ne da ba sa don ci gaban Kano ke daukar nauyin yan daba wadanda su ka dake da zanga-zanga su ka fara kai hare-hare. Ya kuma umarci jami'an tsaro da su gaggauta fara aiwatar da dokar nan take.

Babu ranar daina Zàngà-zàngà sai Tinubu ya biya mana bukatunmu>>Inji Wanda suka shirya zanga-zangar tsadar rayuwa

Duk Labarai
A yayin da kamin fara zàngà-zàngà wanda suka shiryata suka ce an shiryata ne na tsawon kwanaki 10. A yau bayan da aka fara zàngà-zàngàr sun ce ba zasu daina ba har sai shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ya biya musu bukatunsu. Hakan na zuwane yayin da kusan kowane sako da lungu na Najeriya ya dauki harama akan yin zanga-zangar.

Da Duminsa: ‘Yansanda a jihar Naija sun yi harbi dan hana masu zàngà-zàngà tare babbar hanya

Duk Labarai
Rahotanni sun ce 'yansanda sun yi harbi a iska a Tunga dake babbar birnin Jihar Naija watau Minna dan hana masu zanga-zanga tare babbar hanya. Da farko dai 'yansandan sun fara watsawa masu zanga-zangar barkonon tsohuwa ne saidai daga baya masu zanga-zangar sun sake taruwa a waje daya. Rahoton yace jami'an tsaro da suka hada da sojoji, 'yansanda da sauransu sun cire duwatsu akan titi da matsa suka sa.

Yayin da aka fara zàngà-zàngà, farashin kayan abinci ya sake tashi

Duk Labarai
A yayin da aka fara zàngà-zàngà akan yunwa a yau, farashin kayan abinci ya sake tashi a kasuwannin Najeriya. Hakan ya farune yayin da mutane ke ta rububin ahuga kasuwa dan sayen kayan abinci saboda rashin sanin me zai je ya dawo game da maganar zanga-zangar. Gwamnatin tarayya dai ta yi iya bakin kokarinta dan ganin ba'a yi zanga-zangar ba amma abun ya ci tura inda tuni an fara zanga-zangar a jihohi da yawa na kasar nan.