Friday, May 23
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Rarara yasa an saki Hassan Make-Up bayan ya kwana a ofishin ‘yansanda

Rarara yasa an saki Hassan Make-Up bayan ya kwana a ofishin ‘yansanda

Duk Labarai
Rahotannin da Hutudole ke samu na cewa, Rarara da Rashida Mai Sa'a sun sa an saki hassan Make-Up daga ofishin 'yansanda bayan kamun da aka masa. Hutudole ya fahimci cewa da misalin karfe 10 na dare ne aka kama Hassan Make-Up inda ya kwana a ofishin 'yansandan. Sannan da Misalin karfe 10 na safe aka sakeshi. Rahotanni sun ce Hassan Make-Up ya zo Najeriya ne halartar bikin Rarara da kuma yiwa Mai Wushirya gaisuwar rasuwar mahaifiyarsa. A wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sadarwa, An ga yanda wani dansanda ya mari hassa Make-Up tare da zaginsa wana haka ya sabawa aikin dansanda.
Kasar Ingila na fama da rashin aikin yi da rabon da a ga irinsa tun shekaru 4 da suka gabata

Kasar Ingila na fama da rashin aikin yi da rabon da a ga irinsa tun shekaru 4 da suka gabata

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Ingila na cewa, kasar na fama da karancin aikin yi wanda rabon da aga irin sa shekaru 4 kenan da suka gabata. Hakanan rahoton yace ma'aikata basa samun karin Albashi yanda ya kamata. Alkaluma daga hukumar kididdigar kasar, (ONS) sun bayyana cewa rashin aikin yin ya karu da kaso 4.5 cikin 100 wanda rabon da aga hakan tun shekarar 2021.
Obasanjo da Atiku da Obi sun halarci kaddamar da littafin Sule Lamido a Abuja

Obasanjo da Atiku da Obi sun halarci kaddamar da littafin Sule Lamido a Abuja

Duk Labarai
Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo, tsofaffin Mataimakan Shugaban Kasa, Atiku Abubakar da Namadi Sambo, da tsofaffin Shugabannin Majalisar Dattawa, Ken Nnamani da Pius Ayim, sun isa wurin kaddamar da littafin tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido. Tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, shi ne zai yi nazari kan tarihin rayuwar Lamido da ke dauke da take “Being True to Myself”. Daga cikin manyan baki da suka halarci kaddamar da littafin a cibiyar taro ta NAF da ke Abuja har da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a zaben 2023, Peter Obi, sai gwamnonin Gombe, Muhammadu Yahaya; Jigawa, Umar Namadi; da na Filato, Caleb Mutfwang. Haka zalika, wasu daga cikin fitattun mutane da suka halarta sun hada da tsofaffin gwamnonin Benue, Gabriel Suswam; Kaduna, Ahme...
Sanatocin Jihar Kebbi 3 Sun Sauya Sheka Zuwa APC a Hukumance a zaman majalisa na yau

Sanatocin Jihar Kebbi 3 Sun Sauya Sheka Zuwa APC a Hukumance a zaman majalisa na yau

Duk Labarai
Mai girma Sanata Dakta Muhammad Adamu Aliero, CON, mai wakiltar Kebbi ta Tsakiya, tare da Sanata Dakta Yahaya Abubakar Abdullahi Mallamawan Kabi na Kebbi ta Arewa da Sanata Musa Garba Maidoki na Kebbi ta Kudu, sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP) zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC). Sanatocin sun bayyana wasu dalilai da suka sa suka bar PDP kamar haka: Rashin Jagoranci: Sun nuna damuwa game da rashin ingantaccen jagoranci a cikin jam’iyyar PDP. Rigimar Cikin Gida: Sun ce rikice-rikicen cikin gida da ke ci gaba da faruwa a jam’iyyar ya taka rawa matuka a yanke shawarar da suka dauka. Goyon Bayan Jagorancin APC: Sanatocin sun bayyana goyon bayansu ga jagorancin Mai girma Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Dakta ...
Sanata Natasha ta bayyana gaban Kotu a wajan shari’ar kalubalantar dakatar da ita daga majalisa

Sanata Natasha ta bayyana gaban Kotu a wajan shari’ar kalubalantar dakatar da ita daga majalisa

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wadda ke wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya ta isa Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a yau Talata don sauraron karar da aka shigar a kanta. Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Mai Shari’a Binta Nyako ta sanya ranar yau talata domin sauraron karar raina kotu da shugaban majalisar dattawa ya shigar kan Akpoti-Uduaghan. Mai Shari’a Nyako ta dage sauraron shari’ar zuwa ranar Litinin mai zuwa domin ci gaba da sauraron karar gaba ɗaya. Jaridar Arewa
Kalli Bidiyo: ‘Yansanda sun kama Jarumin Tiktok, Hassan Make-Up, Sannan an ci zarafinsa ta hanyar zagi da mari, duk da dokar ‘yansanda ta hana hakan

Kalli Bidiyo: ‘Yansanda sun kama Jarumin Tiktok, Hassan Make-Up, Sannan an ci zarafinsa ta hanyar zagi da mari, duk da dokar ‘yansanda ta hana hakan

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, 'yansanda sun kama Jarumin Tiktok, Hassan Make-Up. A wani Bidiyo da aka ganshi a ofishin 'yansanda, An ga Dansandan dake masa tambayoyi ya mareshi tare da zagi wanda hakan ya sabawa dokar aikin dansanda. Ko da a jiya, saida Kwamishinan 'yansanda na birnin tarayya, Abuja ya ja kunnen jami'ansa cewa, zagi da marin wanda ake zargi ko me laifi baya cikin aikin dansanda. https://twitter.com/Sadeeq_Malo/status/1922182213228978353?t=IuFMmAMvMSZV4WyxBsU_2g&s=19 Rahoton da muke samu shine Hassan Make-Up ya zo bikin Rarara ne aka kamashi.
ABIN ALFAHARI: Matasa Uku Daga Jihar Gombe Sun Kammala Karatun Jami’a A Garin Madina Dake Kasar Saudiyya

ABIN ALFAHARI: Matasa Uku Daga Jihar Gombe Sun Kammala Karatun Jami’a A Garin Madina Dake Kasar Saudiyya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Matasa Uku Daga Jihar Gombe Sun Kammala Karatun Jami'a A Garin Madina Dake Kasar Saudiyya Daliban sune; Khuzaifa Usman Muhammad daga Pantami Abubakar Waziri Daga Kumo Yahaya Ibrahim Daga Kasuwar Mata Allah Ya sanyawa karatunsu albarka.
Matashiya ta Kàshè kanta saboda bata ci maki me yawa a jarabawar JAMB ba

Matashiya ta Kàshè kanta saboda bata ci maki me yawa a jarabawar JAMB ba

Duk Labarai
Matashiya me suna Opesusi Faith Timilehin 'yar Kimanin shekaru 19 ta sha guba ta kashe kanta ranar Litinin saboda ta ci maki 190 a jarabawar JAMB. Faith na zaunene da yayarta a Legas amma 'yar asalin Abeokuta ce, makwabtansu sun bayyana ta a matsayin mutuniyar kirki wadda bata son hayaniya. Danginta sun ce ko a shekarar data gabata ta rubuta jarabawar JAMB amma makinta na shekarar data gabata ya fi na yanzu. Saidai wani abin tashin hankali shine an bata Admission bayan mutuwarta.
‘Yar Shekaru 16 ta yi Gàrkùwà da kanta inda ta nemi iyayenta su biya kudin fansa Naira Miliyan 2

‘Yar Shekaru 16 ta yi Gàrkùwà da kanta inda ta nemi iyayenta su biya kudin fansa Naira Miliyan 2

Duk Labarai
Matashiya 'yar kimanin shekaru 16 wadda ke ajin SS2 a makarantar Sakandare ta yi garkuwa da kanta inda ta nemi a biya kudin fansa Naira Miliyan 2. Lamarin ya faru ne a Abakaliki, Jihar Ebonyi. Matashiyar ta kira dan uwanta inda ta sanar dashi cewa an yi garkuwa da ita. Wani dake da alaka da iyayenta ne ya taimaka mata wajan shirya wannan lamarin. Kakakin 'Yansandan jihar, Joshua Ukandu ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace an kama wadanda ake zargi kuma sa'a tabbatar an hukuntasu.
An kama mahaifi da zargin yiwa ‘ya’yansa mata Fyàde

An kama mahaifi da zargin yiwa ‘ya’yansa mata Fyàde

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Legas na cewa, 'yansanda a jihar sun kama wani uba me suna Best Orji dan kimanin shekaru 39 da zargin yiwa 'ya'yansa fyade. Mahaifiyar yaran ce ta kai korafi wajan 'yansandan inda tace ya aikata lamarin a yayin da yaran ke da shekaru 12 da 14. Kakakin 'yansandan jihar, (PPRO),CSP Benjamin Hundeyin ne ya tabbatar da hakan a sanarwar da ya bayar ga manema labarai. Yace sun kama Best Orji zasu gurfanar dashi a gaban kuliya.