Saturday, April 25
Shadow

Author: Bashir Ahmed

EFCC sun kulle gidaje da kasuwancin Tsohon Ministan shari’a Abubakar Malami

EFCC sun kulle gidaje da kasuwancin Tsohon Ministan shari’a Abubakar Malami

Duk Labarai
A ranar Litinin, EFCC sun kulle gidaje da kasuwancin tsohon Ministan shari'a Abubakar Malami. Rahotanni sun bayyana cewa EFCC sun rubuta da jan fenti cewa an kulle gidajen kada wanda ya shiga. A wani Bidiyo da ya watsu a kafafen sada zumunta, An ga Malami yana tambayar EFCC din ina umarnin kotu da yace a kulle masa gida? Malami dai yace umarnin farko da kotu ta bayar ya dina aiki. Saidai jami'an EFCC din sun bashi amsar cewa zasu iya kulle gidajen nasa tunda har yanzu ana kan binciken su. https://twitter.com/i/status/2036138556024906020
Bani bace, Ni Bazan Mvtv ba, inji matar tsohon Gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai bayan da wani rahoto yace ta rigamu gidan gaskiya

Bani bace, Ni Bazan Mvtv ba, inji matar tsohon Gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai bayan da wani rahoto yace ta rigamu gidan gaskiya

Duk Labarai
Matar tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai ta musanta wani rahoto dake cewa ta rigamu gidan gaskiya. Tace ba ita bace, ita ba zata mvtv ba inda tace ita Allah zai barta. Ta rubuta hakane a shafinta na X. https://twitter.com/i/status/2036050333705588786 Hon. Bello El-Rufai dai ya wallafa cewa matar dan uwan mahaifinsu ta rasu. Inda daga nan ne masu rahoton suka samu matashiyar labarin suka wallafa ba tare da bincike ba.
Rahotanni sun ce Dangote na shirin daina sayar da mansa a Najeriya ya rika sayar dashi duka zuwa kasashen waje

Rahotanni sun ce Dangote na shirin daina sayar da mansa a Najeriya ya rika sayar dashi duka zuwa kasashen waje

Duk Labarai
Wasu Rahotanni sun bayyana cewa, Aliko Dangote na shirin fara sayar da duka man da ya tace a matatarsa zuwa kasashen waje. Rahoton yace Dangote na fushi ne da Gwamnatin Najeriya saboda har yanzu tana baiwa 'yan kasuwa lasisin shigowa da man fetur duk da yake cewa ga matatar mansa tana samar da man. Kasashen Afrika irin su Afrika ta Kudu da sauransu na yiwa Dangote matsin lamba kan ya kara yawan man fetur din da yake sayar musu.
Karya ake min ban taba yin sana’ar Sayar da katin waya ba>>Inji Tsohon Hadimin Buhari, Malam Bashir Ahmad

Karya ake min ban taba yin sana’ar Sayar da katin waya ba>>Inji Tsohon Hadimin Buhari, Malam Bashir Ahmad

Duk Labarai
Tsohon hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya mayar da raddi bayan da wani yace a da kamin ya shiga harkar siyasa yna sana'ar sayar da katin waya ne. Malam Bashir Ahmad ya bayar da tallafin Naira Miliyan 5 ne a wani shiri da ake yi na tara kudaden da za'a tallafawa matasa da sana'o'i a Arewa. Sai wani yace a da fa sana'ar sayar da katin waya yake. Saida malam Bashir Ahmad ya karyata wannan ikirari. Yace idan da yayi sana'ar sayar da katin waya ba zai ji kunyar fadar hakan ba da itama sana'a ce kuma wasu sun yi sun samu nasara a rayuwa. https://twitter.com/i/status/2036159753030701268