Wannan matashiyar ta bayyana cewa, zuwa Lahira da Bidi'a kamar zuwa bankine da jabun kudi.
Ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta.
https://www.tiktok.com/@salzee23/video/7578532472703552788?_t=ZS-91r0utW1SpV&_r=1
Daliban jami'o'in Federal University Kashere, Gombe dana jami'ar BUK, Kano Kiristoci sun koka da cewa, akwai masallatai da yawa a wadannan jami'o'in amma an hanasu gina coci ko guda daya.
Daya daga cikin daliban na Kashere ne ya fito yake zanga-zanga shi kadai inda yace suna bukatar Coci a jami'ar.
https://twitter.com/Zeru010/status/1995207329504235744?t=PK6iWd492V___RWeKguilw&s=19
Wani kirista ta bayyana cewa abin haushin shine jihar Gombe da yawan musulmai da kirista daidai suke watau 50/50 amma irin wannan abin na faruwa.
https://twitter.com/Zeru010/status/1995375684320207249?t=b2LtmuYCGtr1EUeOSloutg&s=19
Wannan zanga-zanga da dalibin yayi tasa shima wani dalibin jami'ar BUK Kano ya bayyana cewa suna hakan take, akwai masallatai a BUK amma su ba'a basu damar...
Shafukan sada zumunta na Facebook da Instagram sun kulle shafin mawakin Najeriya, Edris Abdulkarim saboda wakar da yawa shugaban kasar Amurka, Donald Trump.
Idris yayi wakar ne akan harin da aka ce Trump din zai kawo Najeriya.
Sannan ya bayyana irin matsalolin tsaron da Najeriya ke fama dasu.
Ya kuma bayyana irin satar kudin da 'yan siyasa ke yi da rashawa da cin hanci yayin da Talakawa ke fama da matsalar tsaro da Talauci.
Saidai bincike ya nuna cewa tuni an kulle shafinsa saboda wannan wakar.
Bidiyon Tauraron matashin mawakin Arewa, Bilal Villa a daji sanye da kayan sojoji ya bayyana a kafafen sada zumunta inda kuma aka ganshi dauke da Bindiga.
Lamarin ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke cewa ko da barkwanci ne hakan bai kamata ba musamman yanda ake cikin halin matsalar tsaro.
https://twitter.com/iam_muazzam1/status/1995226619695469001?t=AU2y5OgiB5JSw2RIUr92zQ&s=19
Babu dai tabbacin ingancin Bidiyon ko na gaske ne ko kuwa AI ne.
Saida a wani lamarin me kama da wannan, An kuma ga Bilal Villa a wani Bidiyo a daji sanye da kayan sojoji shima yana cewa suna daukar waka ne.
A karshen Bidiyon yace shi ba da Bindiga bane.
https://www.tiktok.com/@bilalvillah675/video/7578480300410342677?_t=ZS-91qvLVI9Sam&_r=1
https://www.tiktok.com/@daddy_collection/...
Dan fafutuka kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore ya kaiwa malamin Darika da aka kulle, Sheikh Abduljabbar ziyara a gidan yari.
Ya bayyana hukuncin da akawa Abduljabbar da cewa na siyasa ne inda yace suna neman a sakeshi da gaggawa.
https://twitter.com/sowore/status/1995207003224916376?t=OTsHwaONPUnNogBggvxQBQ&s=19
Rahotanni sun bayyana cewa, Kasar Amurka ta aiko da jirgin saman Lekan Asiri zuwa Najeriya.
Jirgin kamar yanda me saka ido akan ayyukan masu ikirarin Jìhàdì a yankunan Sahel, Brant Philip ya bayyana, yace ya yi leken Asirin ne a Jihar Borno, Akan Kungiyar ÌSWÀP.
Jirgin ya taso ne daga matsugunin kasar Amurkar dake kasar Ghana.
Sahara Reporters ta ruwaito Brant Philip yana cewa Gwamnatin Najeriya ta amincewa kasar Amurkar ta kai hari kan 'yan kungiyar.
Sannan yace Amurkar zata yi amfani da jihar Naija a matsayin matsuguninta yayin wannan aiki.
Saidai hadimin tsohon shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya soki Brant Philip inda yace bai kamata ya fitar da wannan bayani ba dan bayanine na sirri kuma kamar yana ankarar da 'yan Kungiyar ÌŚWÀP dinne su shiryawa harin.
Matashi Umar Khalid da ya fito ya bayyana soyayyarsa ga matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari ya jaddada soyayyar tasa.
Yace yana son ya auri A'isha Buhari da gaske kuma in Allah ya yadda zata amince inda yace sai ya ga yanda 'yan Bakin ciki zasu yi.
https://www.tiktok.com/@umarpitykhalid0/video/7578512484462644498?_t=ZS-91prORQwqob&_r=1
Matashiya me suna Naomi Capacity ta bayyana cewa, Bidiyon tsiraici da aka gani tabbas na Amanine.
Tace amma bata sani aka dauke ta ba saboda sai da aka bata kwaya tasha sannan.
Ta kuma bayyana sunan Saurayin Amanin da ya ci amanarta.
https://www.tiktok.com/@naomikfr0j3/video/7577735172527885589?_t=ZS-91ppH55r6sT&_r=1
Matashin Tauraron mawakin Arewa, Bilal Villa ya bayyana cewa, Bidiyon tsiraici da ya nuna a live dinsa bana Amani bane.
Yace kuma ba wai ya nunashi ne dan aci zarafin ta ba.
Yace ba zai so ya tozarta ko da wanda bai sani ba ballantana ita Amanin.
Hakan na zuwane bayan da aka yi ta masa ruwan Allah wadai saboda nuna Bidiyon tsiraicin inda da yawa ke cewa ko da kowa zai yace mata baya, bai kamata ace yana ciki ba.
https://www.tiktok.com/@bilalvillah/video/7578482628253240594?_t=ZS-91poIh4zXGq&_r=1