Wednesday, January 14
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Hukumar jirgin kasa ta Najeriya ta sanar da rage kudin tikitin jirgin da kaso 50 saboda bukukuwan karshen shekara

Hukumar jirgin kasa ta Najeriya ta sanar da rage kudin tikitin jirgin da kaso 50 saboda bukukuwan karshen shekara

Duk Labarai
Hukumar jirgin kasa ta Najeriya, The Nigerian Railway Corporation ta sanar da rage farashin Tikitin jirgin da kaso 50 saboda bukukuwan karshen shekara. Hukumar tace ragin zai fara aiki ne a yau, Talata. A ranar 25 ga watan Disamba ne za'a yi bikin Kirsimeti sannan akwai bikin karshen shekara na 1 ga watan Janairu wanda duka Gwamnati ta bayar da hutu.
Gwanin Burgewa, Kalli Bidiyon yanda ‘yan kwallon kasar Egypt suka karanta Fatiha da Suratul Ikhlas sau 3 dan neman nasara kamin wasansu da Zimbabwe

Gwanin Burgewa, Kalli Bidiyon yanda ‘yan kwallon kasar Egypt suka karanta Fatiha da Suratul Ikhlas sau 3 dan neman nasara kamin wasansu da Zimbabwe

Duk Labarai
'Yan Kwallon kasar Misra/Egypt sun karanta Fatiha da suratul Ikhlas sau 3 a dakin canja kaya kamin wasansu da kasar Zimbabwe a ci gaba da gasar AFCON. Bidiyon nasu ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda musamman musulmai suka rika musu fatan Nasara. https://twitter.com/SalahUpdates/status/2003266206233755890?t=sRHJ59Q3V0Hiw2pwduOocA&s=19 Kuma sun yi nasara a wasan inda Egypt taci 2 Zimbabwe taci 1
Kalli Bidiyon: A yayin da ya rage saura kwanaki 2 a tashi Duniya kamar yanda faston kasar Ghana yace, Mabiyansa da suka yadda dashi sun sayar da kadarorinsu sun koma wajansa da zama

Kalli Bidiyon: A yayin da ya rage saura kwanaki 2 a tashi Duniya kamar yanda faston kasar Ghana yace, Mabiyansa da suka yadda dashi sun sayar da kadarorinsu sun koma wajansa da zama

Duk Labarai
Faston nan na kasar Ghana da ya ce wai an masa Wahayi Duniya zata tashi ranar Kirsimeti watau 25 ga watan Disamba kuma wai an ce masa ya kera jiragen ruwa 8 dan ya kwashi mutane a ciki saboda za'a yi ruwa irin na Dufana a yanzu ya fito yanawa mabiyansa bankwana. Rahotanni sun ce wadanda suka yadda dashi tuni suka sayar da kadarorinsu suka koma wajansa da zama inda suke jiran ranar 25 ga wata tazo. An ganshi ya fito yanawa mabiyan nasa bankwana. https://twitter.com/OzorNdiOzor/status/2003172382266290185?t=OmsYRbBH1RqQiyr_YeBMRQ&s=19
Kasar Amurka ta ce duk dan Chiranin dake kasar zata bashi dala $3000(Watau sama da Naira Miliyan 4 kenan) idan ya yadda ya koma kasarsa

Kasar Amurka ta ce duk dan Chiranin dake kasar zata bashi dala $3000(Watau sama da Naira Miliyan 4 kenan) idan ya yadda ya koma kasarsa

Duk Labarai
Kasar Amurka ta sanar da cewa, duk dan Chiranin dake kasar ta amince zata bashi dala $3000 kwatankwacin sama da Naira Miliyan 4.3 kenan idan ya yadda ya koma kasarsa. Kasar ta bayyana hakane daga Ma'ikatar DHC inda a baya dala $1000 ce kawai ake baiwa 'yan Chiranin idan sun amince zasu koma kasashen nasu. Hukumar tace daga watan Janairu na shekarar 2025 zuwa yanzu 'yan Chirani akalla Miliyan 1.9 suka amince su koma kasashen su daga kasar Amirkar ba tare da an kamasu ba.
Da Duminsa: Kasar Amurka tace ta fas kawo Khàrì Najeriya inda tace ta fahimci abinda ke faruwa a Najeriya kuma bai fi karfin jami’an tsaron kasar ba

Da Duminsa: Kasar Amurka tace ta fas kawo Khàrì Najeriya inda tace ta fahimci abinda ke faruwa a Najeriya kuma bai fi karfin jami’an tsaron kasar ba

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka tace ta janye matakin soji da take son dauka akan Najeriya bisa zargin Kisan Kiristoci. Tace a yanzu bayan ta fahimci yanda abin yake ta gane abune da za'a iya warwareshi ta hanyar diplomasiyya. Amurkar ta canja matsayine bayan ganawar 'yan majalisar kasar, Bill Huizenga da Reps. Michael Baumgartner, Keith Self, da Jefferson Shreve, babban me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro Malam Nuhu Ribadu. Tace ta fahimci akwai banbancin rikicin dake faruwa a Arewa maso gabas da Arewa maso tsakiya. Tace amma zata ci gaba da aiki da Najeriya wajan ganin lamuran tsaro sun inganta.
Kalli Bidiyo da Duminsa: Bayan Daurin aure, Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Kinal da Angonta sun saki zazzafan Bidiyo suna Rùngùmar juna

Kalli Bidiyo da Duminsa: Bayan Daurin aure, Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Kinal da Angonta sun saki zazzafan Bidiyo suna Rùngùmar juna

Duk Labarai
An ga wani sabon Bidiyon Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Kinal da Angonta suna rungumar juna wanda matar Rarara, Aishatulhumaira ta wallafa da yammacin yau. Hakan na zuwane bayan da aka daura aurensu. Da yawa sun yi ta sam barka kan lamarin. https://www.tiktok.com/@aishatulhumairah/video/7586772365858573579?_t=ZS-92RZuiHFtyL&_r=1
Babbar Matsalar Buhari itace yasan da baragirbin Gwamnatinsa amma ya kasa ciresu, ni kaina sai da aka so fitar dani daga Villa amma ba kiya>>A’isha Buhari

Babbar Matsalar Buhari itace yasan da baragirbin Gwamnatinsa amma ya kasa ciresu, ni kaina sai da aka so fitar dani daga Villa amma ba kiya>>A’isha Buhari

Duk Labarai
Matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari ta bayyana cewa, an so a fitar da ita daga fadar shugaban kasa lokacin mijinta na mulki amma taki yadda. Tace wani jami'in tsaro ya ce mata ya kamata ta koma Daura da zama saboda suna son yin wani bincike idan an kammala sai ta dawo. Saidai tace amma taki amincewa da hakan. A'isha Kuma a cikin Littafin tarihin Rayuwar Buhari da aka rubuta tace babbar matsalar mijin nata yasan bara gurbi a gwamnatinsa amma yaki ciresu daga mukaminsu. Tace tana fatan Shugaba Tinubu ba zai tafka irin kuskuren da mijin nata a tafka ba.
Amurka ta baiwa Najeriya tallafin Dala Biliyan 2 a inganta kiwon Lafiya, amma tace afi baiwa Kiristoci muhimmanci

Amurka ta baiwa Najeriya tallafin Dala Biliyan 2 a inganta kiwon Lafiya, amma tace afi baiwa Kiristoci muhimmanci

Duk Labarai
Amurka ta rattaɓa hannu kan wata yarjejeniya ta haɗin gwiwa a fannin inganta kiwon lafiya lafiya mai ɗorewa na tsawon shekaru biyar da Najeriya, wadda ta kai kimanin dala biliyan 5.1, don inganta tsarin lafiyar ƙasa karkashin tsarin Amurka na samar da lafiya ga al'ummar duniya ta America First Global Health Strategy. A karkashin wannan yarjejeniyar, Amurka za ta bayar da tallafi na dala biliyan 2.1, yayin da Najeriya za ta zuba dala biliyan 3.0 a kiwon lafiya a cikin shekaru biyar. Saidai kasar Amurka tace a fi baiwa Kiristoci muhimmanci wajan bayar da kiwon lafiyar. Wannan shi ne mafi girman haɗin gwiwa da kowace ƙasa ta yi tun lokacin da aka kaddamar da tsarin. Yarjejeniyar za ta ƙarfafa tsarin kiwon lafiya na Najeriya, ta ceci rayuka, kuma ta ƙara ƙarfafa haɗin kai tsakanin ...
Kalli Bidiyon: Haba A’isha Buhari to ai ke da irin wannan halin naki, ko me aka cewa Buhari zaki mai ai dole ya yadda>>Inji Malam

Kalli Bidiyon: Haba A’isha Buhari to ai ke da irin wannan halin naki, ko me aka cewa Buhari zaki mai ai dole ya yadda>>Inji Malam

Duk Labarai
Malam ya bayyanawa Hajiya A'isha Buhari, matar Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari cewa, da irin wannan halin nata, dole ko me aka cewa Buhari zata mai ya yadda. Yace An yi shuwagabannin kasashe da yawa a baya amma babu wanda iyalansa suka fito suka masa irin wannan tonin Asirin sai su. Yace kuma har Musulunci ma ta ciwa mutumci wadannan kalaman da ta yi. Malam yace gaskiya hakan sam bai dace ba. Kalli Bidiyon malam anan https://www.tiktok.com/@abdulnassergarba/video/7586606310364417336?_t=ZS-92R3b6LgZA9&_r=1
Wallahi na dauka matar tsohon shugaban kasa, Mace ta gari ce, Ashe ‘yar Tàshà ce irin su Murja Kunya? Inji Maryam Gombe

Wallahi na dauka matar tsohon shugaban kasa, Mace ta gari ce, Ashe ‘yar Tàshà ce irin su Murja Kunya? Inji Maryam Gombe

Duk Labarai
Me amfani da shafin Tiktok, Maryam Gombe ta bayyana cewa tasha matar tsohon shugaban kasa Mara'atussaliha ce, ace 'yar tasha ce irin su Murja Kunya da Me Bakin Kiss. Tace to ai gara ma Murja Kunya da me bakin Kiss su basuwa iyayensu tonon silili ba. Tace sai da suka gama amfana da Gwamnatinsa suka yi amfani da sunansa suka tara kudi shine yanzu zasu fito bayan bashi da rai suna masa tonon silili? Kalli Bidiyon anan https://www.tiktok.com/@mgombe55/video/7586645397578304788?_t=ZS-92R28vzb0td&_r=1