Friday, February 20
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Maganin ulcer sadidan

Magunguna
A wannan rubutu, zamu yi bayanin ciwon gyambon ciki watau Ulcer, saidai kamin mu fara bayani, muna da maganin ulcer sadidan wanda da yardar Allah ana warkewa, ga wanda yake da bukata yana iya yi mana magana a wannan lambar ta WhatsApp ko a kira, 09070701569 muna turawa duka jihohin Najeriya. Da farko Menene Ulcer? Ulcer ko Gyambon Ciki, wani ciwo ne ko kumburi dake faruwa a cikin hanjin mutum. Yawanci yana taba abinda ke da alaka da hanjin cikin mutum ne. Alamomin ulcer Alamomin ulcer sun hada da, jin zafi a cikin ciki dake dadewa zuwa wasu awanni ko a ji shi na dan lokaci kadan. Wasu kan daina jin zafin a yayin da suka daina cin abinci ko suka sha magani. Wata ulcer din sai tsakar dare tako tasowa mutum ko yayin da yake cikin cin abinci. Ana iya samun sauki ta hanyar ...
Kalli Bidiyon cikakkiyar hirar da aka yi da matar marigayi Albani Zaria

Kalli Bidiyon cikakkiyar hirar da aka yi da matar marigayi Albani Zaria

Duk Labarai
Matar marigayi Sheikh Albani Zaria ta fito ta yi cikakken bayani kan matsalar da suke ciki game da 'yan damfara da kuma daliban malamin. A wani Bidiyo da ya yadu sosai a kafafen sada sumunta, an ga me dakin Albani tana zubar da hawaye saboda bakin cikin da ta samu kanta a ciki. https://youtu.be/3U7poakQT3k?si=uqg92n2W86Sf8Kn8 Da yawan mutane sun tausayawa iyalan malam inda aka rika tambayar ina dalibansa da sauran malamai 'yan uwansa? Kalli Bidiyon anan
Tonon Silili: An kama basarake da karbar Naira Miliyan 1.5 ya baiwa ‘yan Bìndìgà masauki a masarautarsa

Tonon Silili: An kama basarake da karbar Naira Miliyan 1.5 ya baiwa ‘yan Bìndìgà masauki a masarautarsa

Duk Labarai
Mahukunta a jihar Taraba sun kama wani basaraken jihar da karbar Naira Miliyan 1.5 ya baiwa 'yan Bindiga mafaka a masarautarsa. Mutane 23 ne aka kama ciki hadda wasu mata 4 wanda ake zargin basarakenne ke basu mafaka. Basaraken ya karbi kudinne dan baiwa 'yan Bindigar mafaka, kamar yanda sanarwar ta tabbatar. Sojoji sun kashe daya daga cikin 'yan Bindigan da kuma kwati makamai ciki hadda Bindigar AK47. Lamarin ya farune ranar Lahadi, 2 ga watan Janairu a kauyen Angwan-Bala dake kamar Hukumar Karim Lamido ta jihar. Kakakin rundunar sojin dake jihar ta taraba, Captain Oni Olubodunde ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace 'yan Bindigar sun tserone daga jihar Filato inda suka nemi mafaka a wajan basaraken.
Kalli Bidiyon mawakiyar Najeriya me shigar banza, Tiwa Savage tana waka a Kasar Saudi Arabia

Kalli Bidiyon mawakiyar Najeriya me shigar banza, Tiwa Savage tana waka a Kasar Saudi Arabia

Duk Labarai
Mawakiyar Najeriya wadda ta shahara wajan nuna tsiraici, Tiwa Savage ta je Jedda kasar Saudiyya inda ta yi waka. A baya dai 'yar shekaru 44 din har sai da bidiyonta ya bayyana inda aka ganta wani yana lalata da ita. Saidai a ziyarar data kai jedda, wadi abinda ya dauki hankula shine yanda aka ga tayi shiga data rufe mafi yawan jikinta, ba kamar yanda ta saba a baya ba. An ga larabawa da iyalansu suna daukar hotuna da ita bayan wasan. kalli Bidiyon anan Kallo karin bidiyon anan Ga wani Kuma:
Kalli Hotuna:Yanda aka ceto wata Budurwa da saurayi ta ya mata tsìràrà ya daureta dan yin tsafi a dakin Otal

Kalli Hotuna:Yanda aka ceto wata Budurwa da saurayi ta ya mata tsìràrà ya daureta dan yin tsafi a dakin Otal

Duk Labarai
Wata budurwa ta tsallake rijiya da baya biyo bayan bin saurayinta da ta yi zuwa Otal. Budurwa ta hadu da saurayinne a kafar sada zumunta inda ya bayyana mata cewa shi ma'aikacin kamfanin man fetur ne inda suka yi mahada a wani Otal dake Abuja. Masu otal din sun bayyana cewa, mutumin ya bayyana sunansa da cewa, shi Emmanuel Okoro ne kuma daga jihar legas yake. Ita kuma budurwar sunanta Promise Eze daga jihar Ebonyi. An isketa a dakin Otal daure a jikin kujera bayan da ma'aikatan Otal din suka kira 'yansanda. Bayan da aka kwaceta aka kaita Asibiti ta dawo hayyacinta, ta bayyana cewa mutumin ya ce mata sunansa, Michael Prince. Kakakin 'yansandan babban birnin tarayya, Abuja, SP Josephine Adeh ta tabbatar da faruwar lamarin inda tace suna kan neman wanda ake zargi...
‘Yar Haya ta fasawa me gida kai bayan da ya bata notice na tashi

‘Yar Haya ta fasawa me gida kai bayan da ya bata notice na tashi

Duk Labarai
Wata mata dake zaune a gidan haya ta fasawa me gida kai bayan da ya bata notice ta tashi daga gidansa. Me gidan wanda matashine kuma marayane ya bukaci matar ta tashi. Lamarin ya farune a garin Umugbabe Ovoko dake karamar hukumar Igbo-Eze ta jihar Enugu. Wani dan jarida daga jihar ne me suna, Chijinkem Ugwuanyi ya bayyana hakan inda yace tuni jami'an 'yansansa sun kama matar da 'ya'yanta 2.
Gwamnatin Tarayya ta fitar da gargadi ga ‘yan Najeriya bayan da aka samu bullar cutar Ebola A kasar Uganda

Gwamnatin Tarayya ta fitar da gargadi ga ‘yan Najeriya bayan da aka samu bullar cutar Ebola A kasar Uganda

Duk Labarai
Hukumar kula da cutuka ta kasa, NSCDC ta bayyana gargadi ga 'yan kasa bayan da cutar zubar da jini, Ebola ta sake bayyana a kasar uganda. Shugaban hukumar ta NCDC, Jide Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwa daya fitar. Cutar Ebola dai tana yaduwa ne a tsakanin Al'umma ta hanyar taba jikin me ita ko jininsa ya taba naka ko sauran ruwan dake fita daga jikin dan Adam. Jide Idris yace duk da yake cutar bata kai ga zuwa Najeriya ba amma suna kokarin ganin bata shigo kasar ba inda suka hada hannu da hukumomin da abin ya shafa.
Dan Allah kada ku sake zaben jam’iyyar PDP ta shugabanci Najeriya>>Jam’iyyar APC ta roki ‘yan Najeriya

Dan Allah kada ku sake zaben jam’iyyar PDP ta shugabanci Najeriya>>Jam’iyyar APC ta roki ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Jam'iyyar APC ta bayyana Jam'iyyar hamayya ta PDP da cewa Jam'iyya ce wadda aka kusa mantawa da ita saboda irin rikice-rikicen da Jamhuriyar ke fama dasu na cikin gida. APC ta yi roko ga 'yan Najeriya da cewa, kada su bari PDP ta dawo kan mulki musamman saboda la'akari da irin lalata kasarnan da suka yi a shekaru 16 da suka yi suna mulki. Me magana da yawun Jam'iyyar ta APC, Bala Ibrahim ne ya bayyana haka a ganawar da yayi da jaridar Punchng inda yace har yanzu barnar da PDP tawa Najeriya bata kare ba. Jam'iyyar bata iya gudanar da komai ba hadda ma gudanar da kanta kamar yanda Bala Ibrahim ya fada inda yace abin dariya yake basu a APC.
An yiwa dan shekaru 60 tiyata dan ciro hodar IIbliss da ya hadiya dan kaiwa kasar waje a biyashi

An yiwa dan shekaru 60 tiyata dan ciro hodar IIbliss da ya hadiya dan kaiwa kasar waje a biyashi

Duk Labarai
Dan Najeriya, Chijioke Igbokwe me shekaru 59 da yayi ikirarin yin kasuwancin Sayar da kaya an kamashi da hadiyar daurin hodar Iblis har guda 81. Ya hadiyi wannan kwayane da niyyar kaita kasar Lebanon inda aka masa alkawarin idan ya kai za'a bashi dala $3000. Saidai an yi sa'a hukumar NDLEA ta kamashi inda kuma ya kasa yin kashin daurin da ya hadiya kamar yanda aka saba. Sai da ta kai ga an yi masa tiyata aka samu ciro guda 57 daga cikin 81 daya hadiya. Kakakin hukumar, Femi Babafemi ne ya bayyana haka inda yace sun ajiye mutumin tsawon kwanaki 5 amma dauri 24 kadai ya iya yin kashinsu daga cikin 81 da ya hadiya wanda hakanne yasa dole aka yi masa tiyata.