Saturday, April 18
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa:Ji Hukuncin da kotu ta yanke kan bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai da ya baiwa mutane mamaki

Da Duminsa:Ji Hukuncin da kotu ta yanke kan bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai da ya baiwa mutane mamaki

Duk Labarai
kotu ta ɗage buƙatar bayar da belin tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai Zuwa Ranar 21 Ga Wannan Watan. Alƙalin da ke jagorantar shari’ar a Babbar Kotun Jiha a ƙarar ICPC da El-Rufa’i ya nemi afuwa bisa gazawar gabatar da hukunci kamar yadda aka tsara, yana mai danganta hakan da ƙarancin lokaci. Saboda haka, an ɗage sauraron buƙatar beli zuwa ranar Talata, 21 ga Afrilu, 2026.
Kalli Bidiyon: Duk da wajan Taron Rainbow yacewa jam’iyyar ADC ya fasa basu dakin taron da zasu yi babban taronsu saboda Wike ya hanasu, Jam’iyyar ta ADC tace babu gudu ba ja da baya sai sun yi taronsu a wajan saidai duk abinda zai faru ya faru

Kalli Bidiyon: Duk da wajan Taron Rainbow yacewa jam’iyyar ADC ya fasa basu dakin taron da zasu yi babban taronsu saboda Wike ya hanasu, Jam’iyyar ta ADC tace babu gudu ba ja da baya sai sun yi taronsu a wajan saidai duk abinda zai faru ya faru

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC tace zata gudanar da babban taronta a dakin taro na Rainbow dake Abuja duk da cewa dakin taron yace ya fasa basu wajan saboda an masa barazanar kwace masa lasisinsa. Saidai me magana da yawun jam'iyyar ta ADC, Bolaji Abdullahi yace ba gudu ba ja da baya sai sun gudanar da taronsu a wajan dan sun sakawa takardar yarjejeniya hannu. Tuni aka ga Bidiyon wajan taron sun fara bayyana a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2043944090287411706
Kalli Bidiyon abin Kunya: Kakakin majalisar jihar Adamawa wanda dan APC ne ya je kauyensu wajan taron siyasa yace Najeriya, yana tsammanin za’a ce sai Tinubu, sai jama’a suka ce sai Atiku

Kalli Bidiyon abin Kunya: Kakakin majalisar jihar Adamawa wanda dan APC ne ya je kauyensu wajan taron siyasa yace Najeriya, yana tsammanin za’a ce sai Tinubu, sai jama’a suka ce sai Atiku

Duk Labarai
Kakakin majalisar jihar Adamawa ya je garinsu inda ya tara taron siyasa dan yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yakin neman zabe. Saidai a yayin da ya tashi zai yi bayani yace, Najeriya, sai aka ce masa sai Atiku a yayin da yake tsammanin ace masa sai Tinubu. https://twitter.com/i/status/2043965596111434080
Da Duminsa: Wajan taron Rainbow da muka shirya yin babban taron mu na kasa a yau, yace ya fasa bamu wajan saboda Gwamnati ta masa barazanar kwace lasisinsa idan ya bamu>>Inji Jam’iyyar ADC

Da Duminsa: Wajan taron Rainbow da muka shirya yin babban taron mu na kasa a yau, yace ya fasa bamu wajan saboda Gwamnati ta masa barazanar kwace lasisinsa idan ya bamu>>Inji Jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC ta bayyana cewa wajan taro na Rainbow data shirya yin taronta na kasa a yau, Talata ya sanar da ita cewa ya fasa bata wajan. Me magana da yawun ADC, Bolaji Abdullahi ne ya bayyana haka a wata sanarwa inda yace, Rainbow ya basu dalilin cewa, Hukumar kula da babban birnin tarayya, Abuja, FCTA ce ta musu barazanar cewa idan suka bayar da wajan za'a kwace lasisinsu. Saidai Bolaji Abdullahi yace sun riga sun sakawa takardar yarjejeniya da raibow hannu dan haka ba zasu fasa ba a wajan zasu yi taronsu.
Da Duminsa: Ji matakin da Wike ya dauka dan hana ADC gudanar da babban taronta na yau

Da Duminsa: Ji matakin da Wike ya dauka dan hana ADC gudanar da babban taronta na yau

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC ta sanar da samun wajen taro me zaman kansa na Rainbow a Abuja inda tace a canne zata gudanar da taron nata. Hakan na zuwane bayan da jam'iyyar tace ta yi iya bakin kokarinta wajan karbar Eagles Square da Filin wasa na Moshood Abiola amma aka hanata. Saidai wasu rahotanni dake fitowa sun ce Ministan Abuja, Nyesom Wike ya yi shirin aika jami'an tsaro dan hana taron na ADC a wajan taron na Rainbow. Saidai jami'an tsaron sun gayawa Wike cewa, hakan ba zata yiyu ba saboda 'yan Adawar na da yawa sosai kuma sun hada kawunansu da kyau. Wike dai yace ADC karya take bata nemi wajan taron ba a hukumance yayin da ADC din kuma tace ta nema amma hanata aka yi. https://twitter.com/i/status/2043878928226329015
Kalli Bidiyon: Yanda Tauraruwar fina-finan Hausa, Momi Gombe ta nuna kirjinta ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon: Yanda Tauraruwar fina-finan Hausa, Momi Gombe ta nuna kirjinta ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Momi Gombe ta dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta bayan da aka ga wani Bidiyon ta inda ya nuna kirjinta a waje. Da yawa sun ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi akai inda wasu ke nuna bai dace ba, wasu kuwa cewa suke ta burgesu. https://www.tiktok.com/@hausa.comedy.nishadi/video/7628158113757089032?_r=1&_t=ZS-95Vs9pE3tR2