Wednesday, March 11
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Wata ‘yar Najeriya dake zaune a kasar Amurka ta nuna wani bangare na kasar Amurkar da ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon: Wata ‘yar Najeriya dake zaune a kasar Amurka ta nuna wani bangare na kasar Amurkar da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Wata 'yar Najeriya dake zaune a kasar Amurka, ta nuna wani sashe na kasar Amurka da tace mutane basu yi tsammanin gani ba. A yayin da a fina-finan kasar Amurka ake nuna ginegine masu tsawo da kuma gidaje masu kyau. A Bidiyon nata an ga wata unguwar Talakawa data nuna. https://www.youtube.com/watch?v=WMaLJdebWsw?si=NX0q98YYH6zOhtcp
Kalli Bidiyon: Wike yayi martani kan kiran da ake cewa, shugaba Tinubu ya saukeshi daga Ministan Abuja

Kalli Bidiyon: Wike yayi martani kan kiran da ake cewa, shugaba Tinubu ya saukeshi daga Ministan Abuja

Duk Labarai
Ministan babban Birnin Tarayya, Abuja, Nyesom Wike yayi martani game da neman a saukeshi daga mukaminsa. Yace masu kiraye-kirayen su kwantar da hankalinsu wanda ya nasashi ne ke da wannan ikon, idan yaga cewa baya aikata abinda ya dace, to shine zai saukeshi. Ya kara da cewa amma shi yasan yana yin abinda ya kamata a matsayin Ministan Abuja. https://twitter.com/i/status/2010368170335305951
Wata Sabuwa: An baiwa Shugaba Tinubu shawarar yayi kokari tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya koma APC in ba haka ba zai kawo mai tangarda a zaben 2027

Wata Sabuwa: An baiwa Shugaba Tinubu shawarar yayi kokari tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya koma APC in ba haka ba zai kawo mai tangarda a zaben 2027

Duk Labarai
Dan takarar Gwamnan jihar Kebbi a jam'iyyar APC, Mallam Salihu Isa Nataro ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar ya yi kokarin mayar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai jam'iyyar APC. Yace masa, El-Rufai na da karfin fada aji sosai musamman a siyasar Arewa maso yamma. Yace kuma komawarsa jam'iyyar APC zata sa talakawa da yawa su dawo suna son Tinubu din. Yace kada a bari rashin jituwa tsakanin shuwagabannin jam'iyya da El-Rufai yasa a kyaleshi. Ya bayyana cewa ya kamata a yi kokari El-Rufai ya koma APC kamin zaben 2027.
Watan mu 6 bamu da wutar Lantarki>>Inji Wannan matar dake zaune a birnin New York City na kasar Amirka

Watan mu 6 bamu da wutar Lantarki>>Inji Wannan matar dake zaune a birnin New York City na kasar Amirka

Duk Labarai
Kristy Hallowell 'yar shekaru 44 dake zaune a Greenwood Lake, New York City na kasar Amurka tace watansu 6 kenan basu da wutar Lantarki. Ta bayyana cewa a watanni 6 na karshe na shekarar 2025 basu da wuta. Tace ta rasa aikinta kuma an kara kudin wuta, dan haka ta kasa biya, tace gas ma basu dashi. Tana zaunene ita da 'ya'yanta da mahaifiyarta. Inda tace dole saidai janareta suka rika amfani dashi. Saidai an samu irin kungiyoyin masu taimakawa mutane sun biya mata rabin kudin kuma an sakw hada musu wutar amma har yanzu basu da gas. Saidai tace har yanzu akwai yiyuwar a sake yanke mata wutar dan bashin da ake binta ya kai na sala $3000.
Kalli Bidiyon: Amsar da Riyad Mahrez ya bayar da aka tambayeshi ko yana ganin Rafali ne ya cinsu?

Kalli Bidiyon: Amsar da Riyad Mahrez ya bayar da aka tambayeshi ko yana ganin Rafali ne ya cinsu?

Duk Labarai
Bayan wasan da Algeria ta buga da Najeriya jiya wanda Najeriya ta ci Algeria 2-0, An tambayi Tauraron dan kwallon Algeria, Riyad Mahrez ko me zai ce kan Rafali. Yace tabbas Rafali ba dari bisa dari yake ba amma kuma baya zarginsa, yace Najeriya sun fisu kokari ne kawai Game da ritaya, Mahrez yace wannan shine wasan karshe da zai buga na kasar AFCON. https://twitter.com/i/status/2010273589153661373